yanzu idan nadawo sallah zamu fita da Rufaidah se mutafi dukan mu harda Auta ma kishirya ta " ba tare da dukan su sun san me yake nufi da hakan ba ,suka amsa da to " duk da kasan zuciyar Rufee ba haka taso ba ,taso ne Sufita su kaɗai saboda su fara samun kusanci da juna ,akwai kuma maganar da take so suyi ,wanda tasan matuƙar suka fita waƴan nan jarababbun to ba sake wa zasuyi ba ,bata so ta koma sashen su dan kar Mama ta gane cewar zasu fita da Mu'aisam dan haka tayi zaman ta anan , toilet din da kecikin falon Rumaisa ta shiga ta ɗauro alwala ,da tafito ta kalli Rufee da take canja channel tace " sis Rufee ko zakiyi alwala ne akwai ruwa a cikin toilet "batare da ta kalli Rumaisa dake maganar ba tace " am off salat" taɓe baki Rumaisa tayi tana shigewa bedroom.
cikin doguwar Riga ta shirya tayi kyau sosai fitowar ta yasaka Rufee kallon ta batadai ce komai ba itama Rumaisa batayi mata magana ba ,ta shiga ɗakin Ammi lokacin ta sameta tana sallah saboda haka direct kan gado ta nufa dan tashin Nawwara dake bacci ,bubbuga bayan ta tafara, kasancewar batada nauyin bacci se gashi ta budé ido ,tana ganin Rumaisa tafara narke fuska kamar zatayi kuka tace " Yaya baccin be isheni ba " ok bara mutafi mu barki to dama Yaya yace natashe ki zamu fita shopping" ai tana jin zancen yawo se ta tashi da sauri ,tana faɗin " to mutafi" hararan ta Rumaisa tayi tace " kinyi sallah ne da zaki ce mutafi kuma kinsan baxaki bimu a haka ba ko? Nawwara batayi magana ba ta shiga toilet da sauri alwala tayo ta fito fici-fici tayi sallar saboda batason su tafi su barta ,koda ta gama Rumaisa ta fito mata da kayan da zata saka dan haka ta sanya mata ,suka tsaya jiran Ammi tagama addu'a suyi mata sallama ,bayan ta idar Rumaisa tafaɗa mata zasu fita ,adawo lafiya tayi musu ,cikin wasa tace " wato kun faki idon Mimi da Nurain shine zaku fita ko aiko idan yadawo gidan nan ya samu kun fita da Auta kunsan za'ayi darga da shi " Ammi karki damu xan siyo masa Icecreem ,ko Yaya? ta kalli Rumaisa ,dariya tayi mata a haka suka fita
Fitowar su yayi daidai da fitowar Mu'aisam daga cikin ɗaki da alama ya daɗe da dawo daga masallaci dan kuwa har ya sauya kayan jikinsa yayi kyau sosai wanda har Rufee ta kasa ɓoyewa seda ta maganta " gaskiya Yaya kayi kyau ko har ka fara hasken amarci ne? Haɗe fuska yayi bece komai ba ,ita kuma Rumaisa se tace" yaya smile mana ,Allah baka ganka ba kamar zakaje wurin babyn ka anya kodai ,zance zamu raka ka? murmushin gefen baki ya sakar mata tare da faɗin " wlh za'a fasa fitar nan ,naga kuna neman maidani wani abokin wasan ku"
Rufaida da takaicin maganar Rumaisa ya cikata se taja tsaki tace " wahalar tambaya name kikeyi bayan kinsan tare dani ze fita wannan duk wani yayiwa" fahimtar inda zancen ta ya dosa se Rumaisa tace " haba ke kam ai uwar gida ce sis Rufee ,kika sani ko har ya fara kyarkyarar amarya waƙil ma ku biyu za'a kai masa kinsan masu iya magana sun ce me mata ɗaya abokin gauro ,so yayana ze fita daga cikin su "cikin tsawa Rufee tace " aniyar ki tabiki Rumaisa sedai idan kece kike son sa wannan zamu iya zaman kishi dake amma babu wata mace da ta iso ya so ta ni nasan wanann ,hassada ne da baƙin ciki koda yake na daɗe da gane cewar kema kina son sa " riƙe baki Rumaisa tayi tace" ikon Allah kin taɓa ganin yaya ya auri ƙanwarsa ko kin manta alaƙana dashi ne ni matsayin ɗan uwan da aure ya haramta a tsananin mu nake masa ,da ace ina son sa kamar yadda kika faɗa kema kinsan da baxaki sameshi ba"Rufee xatayi magana ta tare nunfashin ta da faɗin " ki ajiye kalamanki zuwa gaba wata ƙil zeyi miki amfani a lokacin da kika gane cewar akwai wacce yakeso ba keba "da sauri ta wuce ta bar Rufee na sababi ,koda suka iso motar har ya gyara parking Rufee har ta buɗe gaban mota zata shiga se ta ga Nawwara zaune ,cikin haɗe fuska tace " ke fito ki koma baya " ɗago kai Mu'aisam yayi ya kalleta sedai bece komai ba ,har ta fita ta shiga baya ita kuma ta zauna gaban.
tana shiga ya tada motar suka fita
Babban shopping mall ya kaisu yace kowa ya zaɓi abinda yake so ,sosai suka zaɓi manyan tarare irin desingners dinnann masu matuƙar tsada ,daganan suka tagi gefen kayan yara teddies masu kyau Auta ta zaɓa ,daganan ne suka tafi gefen su chocolate,wannan kam Rufee da Nawwara ne kawai su diba dan ita Rumaisa bata shan kayan zaƙi ,Atm yabada a cire kuɗi ,har anyi debited se Nawwa ta hango wani babban boll cikin net ɗinsa irin elastic dinnann da ake hurawa da sauri ta je ta ɗauko tace " yaya musiyawa Nurain wannan " kai kawai ya ɗaga mata yasake bada Atm ɗin suka cire kudin suka tafi ,har zasu fita daga wurin idon sa ya hango mishi bangaren da ake seda irin jalabiyoyin nan ,dan haka kawai yabasu key yace su jirashi a mota yana zuwa , haka ya tafi ya zaɓo jalabiya har kala 3 masu shegen kyau da tsada , sannan ya dawo suka bar wurin.
ganin kamar ba hanyar gida ya ɗauka ba yasaka Rufee kallon sa " Yaya ina kuma zamuje nifa nagaji gida nikeso na koma "to ko mu ajiyeki se ki shiga Napep dan zankai su wani wurin ne " haba yaya yanzu saboda Allah kamar ni dinnann se na tsaya a titi neman Napep? " ke ba mutum bace ko kinfi sauran muta ne ne " to Yaya abun ai a bayyane ne kaiman kasan ta zara me yawa da Allah yayi tsakanin talaka da me kuɗi ,saboda haka ni gaskiya bazan shiga Napep ba " to ko se kijira har mugama abinda mukeyi se ki koma a mota ,daidai lungun su Meerah ya shiga da motar sa , parking yayi daga nesa kaɗan da gidan dan ganin wata motar da ke a jiye kusa da gidan ,wannan karon kam hatta Rumaisa se da tayi magana dan mamakin inda ya kawo su tace " Yaya ina ne nan ɗin ? wlh kamar ba'a kd ba " hararan ta yayi ta madubin motar yace " idan kin fita kya tantance ,fitowa yayi ya ce dukan su su fito ,babu musu suka fito ,kiran Auta yayi yaimata raɗa a kunne ,a mamakin su se sukaga ta daga tsalle tana faɗin " da gaske yaya ? Kai ya ɗaga mata alamar tabbatar wa tare da mata nuni da ƙofar gidan su Meerah.
kallon su Rumaisa tayi tace" yaya yace nan ne gidan Aunty Ameerah mushiga mugani ,kallon mamaki sukayi masa sedai be basu damar magana ba ,sema cewa da yayi "Rumaisa kishiga kudubata sauri nakeyi " bin banyan Meerah tayi ,ita dai Rufee kamar wacce aka kafe a wurin tama kas motsi ,lokacin da suka kai kofar gidan yayi dai² da fitowar Meerah tare da Muhsin ,alamar rakiya tayo masa ,sam bata kula dasu ba se da Nawwara ta rungume ta tana murnar ganin ,da mamaki ta cire hannayen ta da ta zagaye cikin ta dasu itama cikin jin daɗin ganin su tace " Auta waya nuna muku gidan mu? munxo ne muduba ki kwana biyu shiru ko bakida lafiya ne ,ashe ke kina nan soyayya ta ɓoyeki "ta faɗa cikin sigar zolaya "rufe ido Meerah tayi tana daria tace " Aunty ai wannan yaya ne ko? Tayi maganar tana kallon Muhsin ,se a lokacin Rumaisa ta gaidashi ,amsawa yayi yana shiga Mota tare da faɗin " bara na wuce tunda kinyi baƙi xamuyi waya dai Allah yaƙara lafiya"bata amsa shiba sedai ta ɗaga masa kai kawai tare dayimasa waving ,seda ya tada motar tukuna ta ja hannun Rumaisa tace" mushiga ciki Aunty " bin bayanta Rumaisa tayi.......
Comments and share pls
Real Bazamfaria ce ❤️
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels