Share this page
8 / 8
rikici a tsakanin mu ba ita kanta wadda muke so hakan ze taɓa zuciyarta sosai muyi maslaha a ganina shine mafi sauƙi tin kafin abun yayi tsauri" Khaalif yayi saurin tarar sa da cewa, "indai da haske ne maslahar kake so to abu ɗaya ne ze kawo maslaha" ABU ya ɗan murmusa kafin yace, "menene Junior ????" Kai tsaye yace, "kabarmin Ayeeshah ta" Lumsassun idanunsa yaƙara lumshewa ya buɗe sannan yace, "ba lallai ka fahimci irin yadda nakeji ba ƙanina, ta yuwu soyayyar tsakanin ku ƙarfinta shaƙuwa ce kawai saboda kun taso tare, amma ni nayi DAKON SO na ɗauki nauyin sonta tin bansan kaina ba, ina tsaka da azabtuwa a gurin matar baba na amma hakan be sa na manta da ita ba, uhm.. kasan ma abunda nake tunawa ya sani farin ciki a lokacin?? idan na tuna wata rana Eeeshu xata girma, zuciya tana gaya min itace farin cikina sai naji na ƙagara lokacin yayi wanda zan kasance tareda ita, ASALIN SO nakewa Eeeshu Junior kai kaɗai ne gareni ciki da waje kaine dole na kai zan nuna nace kaine ƙani na ka tausayawa ɗan uwanka mana dan Allah ka barmin Eeeshu" Girgiza kai Khaalif yayi yace, "wannan labarin naka yayi fa Bro, sai dai be hau kan layi ba, bazan iya janyewa ba bana so ma naƙara ji ka kira soyayyar da nake mata da sunan shaƙuwa ko menene ma ina so kabarni da ita kamar yadda ka ganni tare da ita" ABU yace, "bazan iya ba, duk da in na faɗa ma ba yarda zakayi ba amma bazan iya barinta ba idan nayi haka naci AMANAR SO ka ɗangale min mana ɗan uwana, shi so ba'a yimasa shamaki, a lokacin da nafara sonta ban taɓa zaton ma wani namijin ze sota ba bayan ni bare nayi tunanin Ƙanina ze so ta, sai dai so makaho ne kuma kurma ne baya gani kuma bayajin kira haka baya ɗaukar shawara amma da yaso yimana adalci da be kaini kanta ba" Sosai ran Khaalif yaƙara ɓaci dan haka ya miƙe tareda cewa, "ni yanzu tafiya zanyi banida lokacin tsayawa naji wannan kalaman naka masu kama da wasan kwaikwayo, kamar yadda kace bazaka iya ba haka nima bazan iya ba, Ayeesha tawa ce adalcin da zakaiwa kanka nima kaimin kawai ka barni da ita dani tafi dacewa, idan ba haka ba kuma mu zuba ɗan halak ka fasa, dani da kai zan ga ɗan halak a cikin mu" ƙasa ABU yayi da kai ya Share ƙwallar da ta zubo kan kumatunsa cikin takaici yace, "Junior uwa ɗaya ce ta haife mu kuma a ƙasa ɗaya a iya sani na Mahaifiyar mu bata haifi ɗan da ba na halak ba, dani da kai duk ƴaƴan halak ne, kana da uba ina da uba banbancin kawai kai mahaifinka mutuwa yayi ni kuma rabuwa sukayi dan ƙaddara badan mugun halinta ba, Mahaifiyar mu Uwa ce tagari me son ganin dariyar ƴaƴanta idan kai baka santa ba to ni da hankali na ta mutu" takaici ya hana Khaalif magana ya fice fuuuuu yayi gaba kamar me shirin tashi sama. Zazzafar iska ABU ya furzar tareda zabga tagumi yana roƙon mafita a gurin Allah. Khaalif yana dawowa gida yayi sa'a Mama bata nan sai Aisha ita kaɗai tana kicin tana girki ya shigo, kai tsaye can ya nufa dan yasan a can ne ze same ta. Tana aikin tana ƴan waƙe waƙe tana juyowa babu zato tayi tozali dashi haka kawai taji gabanta ya faɗi, ta zaro ido tana kallonsa ganin yadda fuskar sa take ba annuri tsoro ne yafara kafa sansani gareta, da kyar ta haɗiyi yawu tana son tayi magana amma takasa sai ido. Takawa yayi har zuwa gabanta yana fuskantar ta cikin tsananin ɓacin rai yace, "rayuwar da kika zaɓa mana kenan??? bakya tunanin faruwar wani mummunan abu akan mu?? kuskure ne haɗa hamayya tsakani na da ɗan uwa na dan bazan iya janye masa ba kuma bazan saurarawa kowa ba, shin da gaske ne kina son sa ko kuma shima yaudarar sa kike kamar yadda kike yaudarata???" Kauda kai tayi daga kallonsa cikin ƙarfin hali tace, "eh ina son sa kamar yadda kakejin kana sona haka nakejin ina sonsa, abu wanda ba na zahiri ba shine wanda akeyin tambaya amma ai yanzu a zahiri ka gani ko?" a hasale yace, "haka ma kike gaya min, ya kike so nayi ne wai?? kinsan bazan iya jurar rashin ki ba bakya tsoron nayi abunda ze sa kowa ya rasa ko kuma nayi abunda dole sai na mallake ki???" Kai tsaye tace, "bana tsoron ko ɗaya idan kayi abunda ka mallake ni hakan zeyi min daɗi dan na samu wanda nake so idan kayi abunda kowa ze rasa shima zanji daɗin kasancewar ban auri ɗayan ku ba hakan ze fi wa kowa kwanciyar hankali, halama Khaalif ba kai bane na asalin Khaalif ɗina ka zama wani daban ba wanda na sani ba, kai me haƙura ne da komai ka barwa yayanka ko da ba ni ba amma kake irin haka" Hannun ta ya finciko har sai da tafaɗa jikinsa ya haɗe duka hannayen nata ya riƙe gamm cikin zafin rai yace, "bazanji komai ba ko me kika gaya min amma abunda nake so ki barwa kanki sani babu wani ɗan da aka haifa kuma zaki aure shi ki kasance cikin kwanciyar hankali bayan ni, daa nake me haƙuri da juriya amma yanzu ta ƙarfi kin canja ni ko me na koma kece sila kinsa na haukace, tabbas yanzu ba Khaalif ɗin daa bane na yanzu ba ya yafiya kuma baya ragawa duk wanda ya hau hanyarsa ko me na aikata kisa a ranki kece sila haka ko me na zama kece kika maidani hakan, ba ina faɗan komai bane da sunan wasa da gaske nake kuma zan aikata" kuka me ƙarfi ne ya ƙwace mata ta shiga rusa shi kamar tashin hankali, ta rasa wace irin masifa ce take damunta a rayuwa shin meye maganin matsalarta??? waye wanda ze kawo mata ɗauki a rayuwarta?? a cikin su waye ze zama katangar ƙarfe tsakanin ta da damuwar da ta taso da ita???, girgiza masa kai ta shigayi alamar "aa" tana son cewa wani abu amma ta gaza magana dole ta cigaba da kukan gami da kwantar da kanta akan ƙirjinsa saboda mugun riƙon da yayi mata. Ido ya zuba mata kamar wanda yake wani dogon nazari, sai a lokacin kukan nata yafara ratsa zuciyarsa tareda jefashi cikin wani yanayi, cikin sanyi yace, "Ayeeesha kiyi haƙuri ba laifi na bane sonki ne ya zautar dani na rasa makama abun sunyi min yawa har yasa nafara wasu banzayen tunani bana son rasa ki shiyasa nake tunanin yin komai domin na sameki, ki dena kukan nan bana so" Ɗagowa tayi da kyar ta kalleshi sannan taƙara maida kai ta kwantar, cikin ƙunar zuci tace, "ka rage son zuciya Khaalif, Allah ya jarrabe ni da son mutum uku kai kuma ni kaɗai kake so bana son ɓacin ran ku ku duka ina son saku farin ciki na taƙaitaccen lokacin da ya rage min kun sani zan auri Saif amma kai baka ta kowa son zuciyarka shine kan gaba komai sai dai ya kasance kaine, Khaalif ina son Yusuf Ina Son ABU kuma ina Sonka kuma zan auri Saif bazance komai ba dan ba ni nayiwa kaina wannan zaɓin ba Allah ne ya tsara haka a jikin Allon rubuta abu me afkuwa a rayuwata har ma da wanda be faru ba da wanda yafaru a baya duk daga Allah ne kuma gareshi nake roƙon sassauci kuma inaji a jikina a kwana a tashi dole wannan damuwar zata gushe nima zan zama mutum kamar kowa, zuciyata tana gaya min a cikin ku ɗaya ze zamo silar zamana mutum, amma bansan kowaye ba kayi min uzuri karka illata min rayuwa Khaalif" Taƙarasa maganar tana ƙara fashewa da wani sabon kukan. Dumm.. dummm. zuciyarsa ta shiga bugawa ɗaya bayan ɗaya, girgiza kai yayi gami da lumshe idanunsa har cikin ransa yakejin kukan nata kamar ya tarwatsa masa zuciya , jimmm yayi kafin ya buɗe idanun nasa da yanzu sun gama canja kamanni ya ɗora akanta, hannunsa yasa ya shiga share mata hawayen wasu suna ƙara zubowa, cikin wata rikitacciyar murya yace, "Ayeesha kukan ki barazana yake ga rayuwata, ki saurari bugun zuciyata shirin tarwatsewa take saboda kukan ki ki tausayawa Khaalif ɗinki ki dena kuka Ayeeshahh.." a hankali tafara sassauta kukan har tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya sai da tafara nutsuwa sannan tafara jin yadda zuciyarsa take tsalle fakare tayi tana saurara kafin ta ɗago idanunta ta jefa cikin nasa, a hankali ta zame daga jikinsa ta nufi ɗaki ta nemi guri ta zauna. da ido ya rakata har ta ɓacewa ganinsa sannan ya wuce yabar gidan. Tin tana sa ran jin wata magana ko wani alamu daga Saifu har ta dena sai dai tasa a ranta kawai yayi shiru ne badan ya tsorata ba sai dan yaƙara ɓullowa ta wani gurin da ze mata illa. Saif yaga canji da canje canje sosai a gurin Khaalif har ta kai ga ko maganar arziƙi baya yi masa kuma tin daga ranar da ya gaya masa maganar ABU dan haka ya yanke hukuncin tambayar sa dalili. Suna zaune Khaalif yana danne danne shi kuma yana cin abinci, kallonsa yayi ya kauda kai sannan yace, "Khaalif in ɗan tambaye ka mana" Yace, "inaji" Saif yace, "meke faruwa tsakanin mu ko kuma nace tsakaninka da Aisha tabbas akwai abunda ban sani ba ko kuma nace nagagara ganewa, na shiga ruɗani sosai" Murmushi Khaalif yayi kafin yace, "hmmm hakane kam abun kaico ne wannan wai yaya na ne wanda yake son Ayeeshah, inajin zafin abun sosai yanai min ƙuna " Da mamaki yace, "kana nufin wannan yayanka ne?" Yace, " na jini ma kuwa be min adalci ba ko kaɗan ina shi ina Ayeeesha banda sharrin zuci??" Jinjina kai Saifu yayi tareda cewa, "yayan ka ne????" Khaalif Mohammad ya gyaɗa masa kai. Murmushi me tarin manufofi ya saki kafin yace, "ka ja masa kunne akanta dan babu abunda bazan aikata ba, tsira da mutuncinsa shine fita harkar Aisha abarta da mijinta" Shima Khaalif murmushin yayi wanda babu wanda yasan asalin sa sai Allah, yace, "ko baka faɗa ba dama ni meyin ruwa da tsaki ne akan hakan don nima ta shafeni" maganar tayi masa bau shiyasa ya tambaye shi akan yayi masa fashin baƙi akan manufarta amma sai ya share zancen hakan yasa Saifu ya ƙudurewa kansa shiga da fita domin ja musu layi gaba ɗaya dan ya lura akwai wani abu a tattare da Khaalif. *INDO CE..* An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 8 of 8