soma yi na canza kaya sannan na fito falo.
Zungum na tarar da su kamar ba su cikin walwala,Maryam ta taso da sauri za ta soma yi mini tambayoyi amma Mama ta dakatar da ita sai ma abinci da aka ce ta ɗebo mini.Bayan na ci na ƙoshi sai na je na kwanta kan kujerar da Mama ke zaune,kaina na ɗora kan cinyarta sai da ta ɗan buɗe rigata ta taɓa ƙatuwar layar da ke wuyana sannan ta ce “Fatee ya aikin fatan komai ya tafi daidai?”
Na yi murmushi mai sauti na ce “eh alhamdullah,sai gobe kuma zan koma da safe” sai na ga ta kalli Maryam tare da sakin ajiyar zuciya.
Wunin ranar dukkan motsina akan idon Mama yake da muka zo kwanciya sai da ta shafa mini wani mai marar daɗi.
Washegari haka na shirya na tafi asibiti,sai dai tun daga bakin ƙofa na ga canji saboda yadda kowa ya sha jinin jikinsa.Ina isa na samu abokiyar aikina Farida,cikin sakin fuska na soma yi mata magana amma sai na ga tana haɗe rai ina shirin tambayarta lafiya ai kuwa sai ga wanda ya ɗauke ni aikin ya shigo tare da miƙo mini takarda.
Da na duba sai na ga ta sallama ce,na ɗaga kai ina shirin yi masa magana ya nuna mini ƙofar fita cikin tsawa yake cewa “ki fita” babu yadda na iya na fice ɗin.
Idona tab ƙwalla haka na soma tafiyar ƙasa ina tunanin me zan cewa su Mama,kawai sai ji na yi na faɗi ƙasa.Na maido hankalina jikina,wani mai mota ne ya kaɗe ni,idona kansa har ya fito ya miƙar da ni tsaye.
Cikin sanyin murya yake cewa “fatan kyakkyawa ba ta ji ciwo ba? ”
Kai na girgiza masa,murfin motarsa ya buɗe mini tare da cewa “da dukkan alamu akwai abin da yake damunki mu je na rage miki hanya” kamar wacce ya yi wa asiri haka na shiga kuwa.Ya zagayo ya zauna,ya soma driving yana mai cewa “sunana Dr Bilal”
Da sauri na dube shi sai na ji tamkar na san sunan da kuma fuskar,sai dai ban iya tunawa ba sai murmushin yaƙe da na yi.
Takardar hannuna ya karɓe ya karanta bai ce komai ba haka ya ajiye ta yana ɗan haɗe rai,ni ma sai na sunne kaina.Ban ɗago ba sai da na ji yayi parking,ido na shiga ƙyaftawa ina kallon wata haɗaɗiyar asibiti wacce ta fi waccan girma da kuma kyawu.
Fita ya yi,ya buɗe mini ƙofa haka ni ma na fito kamar wata doluwa na take masa baya har muka shiga ciki.Likitoci na tarar birjit,duk suka miƙe tsaye tamkar masu zaman jiranmu.Cike da girmamawa suka gaishe shi kafin shi kuma ya ce “ina mai gabatar muku da nurse Fateema,daga yau za ta fara aiki da mu a wannan asibitin ” duk sai suka shiga taɓa mini suna murmushi,a dole ni ma na murmusa ɗin ina kallon Dr Bilal ina mamakin ta ya aka yi ya san sunana .Nan ya bar ni tare da su,suka soma gabatar mini da junansu a nan ne na haɗu da ƙawata Rahinatu mace mai sauƙin kai da tausayi.Ita ce ta nuna mini ko ina na asibitin,a cikin zagawar da take yi da ni ne take ce mini “kina da matuƙar sa'a tun da har ki ka samu Dr Bilal shi ne da kansa ya kawo ki asibitin nan,a kaf manyan likitocin asibitin nan masu faɗa a ji duk ya fi su tsatsauran ra'ayi kusan saboda kafiyarsa ne akan ra'ayinsa yasa ya shiga komar maƙiya.Tsawon lokaci yana hannunsu sai jiya ne ya dawo”
Na ce “ni kuwa ban ga wani zafin kai a tattare da shi ba” . Tana shirin yin magana wata nurse ta zo da sauri tana mai cewa “ Dr Bilal na neman nurse Fateema a ofis ɗinsa” wata irin faɗuwar gaba ce na ji wacce ban san dalili ba,nurse Rahinatu ce ta yi mini rakiya har zuwa bakin ƙofa.Bayan ya bada izinin shigowa sai na tura ƙofar tare da yin sallama,bai amsa ba ya dai zuba mini idonsa masu kashe ruhi da mugun sauri na sunne kai tare da ja na tsaya.Ya taso ya yi tsaye a gabana yana mai kamo dukkan hannuwana,murya kamar mai yin raɗa yake furta mini “ina sonki ƴar cikin Fateema ”yana gama furta haka babu zato babu tsammani na ji bakinsa kan laɓana yana mai tura harshensa....” yadda na ji an fizge gilashin da ke manne a idona haɗi da hullar kaina su suka tsayar da labarin rayuwata da nake gani ana hasko mini.
Cikin zafin rai na ga Mu'azzam ya finciko ni da mugun ƙarfi daga kan kujerar,ƙirjina ya bugu da nasa na yi baya kamar zan faɗi amma yadda ya riƙe hannuna gam ya hana faruwar haka.
Tsabar yadda yake wani tamke fuska dukkan illahirin jijiyon kansa suka fito,cikin masifarsa da nake mugun tsoro ya soma yi mini ihu.
“Wato da yake ke ballagaza ce shi ne daga baki aiki har da yi masa sumbata,ke jarababiya ƙanwar ayyu”
Idona suka fara zubar da hawayen azaba,cikin rawar murya na ce “sumbata kuma? Ni ban sumbaci kowa ba”
Tamkar wanda ya fita hankalinsa haka ya wani tura ji jikin bango tare da kama wuyana ya ce “in ina magana kina ƙaryatawa sai na shaƙe miki wuya ki mutu kowa ya hutu da fitinarki,ke yanzu ko kunya ba ki ji ni kike faɗa wa Dr Bilal ya sumbace ki? ” muƙut ! Na haɗiye yawun tsoro ina son ƙaryatawar amma ina jin tsoronsa,ni ban ma san taƙaimamai abin da yake magana a kai ba.
Hawaye ne suka soma yi mini zarya ina mai kallon tsakiyar idonsa waɗanda masifa ta saka su yin ja sosai.Tsawon lokaci muna kallon juna kafin ya janye daga kusa da ni ya juya mini baya,can kuma ya ce “fita” furucinsa ya tuna mini dagar da na sha da mahaukacin ai kuwa da mugun sauri na koma gabansa ina mai girgiza masa kai.Tsakiyar idona ya duba,kafin ya kawar da kai ya je ya buɗe wata ƙofa ya shiga.Kamar jira take ya gusa haka ta bayyana gare ni tana mai kallona da idonta masu matuƙar firgitarwa.Da wani irin bala'in gudu na bi bayansa,sam ban yi tunanin toilet ce ya shiga ba.Jikina na mugun kyarma na juya masa baya,tsorona na daɗa ƙaruwa ido kawai na rumtse ina jin yadda zazzaɓi ya soma kawo mini farmaki.
Ƙiiii haka ya jawo ni waje ,a dole na buɗe idona nan na yi arba da ita fatalwar ya buɗe baki zai yi masifar na ƙanƙame shi tare da yi masa magana cikin fitar hayyaci “fa..tal...ta..talwa ” yadda numfashina ke ta ƙoƙarin tsinkewa yasa a dole na yi shiru.
Ina jin lokacin da ya saɓe ni ya fito da ni,wani ɗaki ya kai ni ya kwantar kan gado yana son ɓanɓare ni amma na ƙi sakinsa don har ga Allah tsoron budurwar nake yi wacce ban san wace ce ba.
“Ki nutsu ta tafi” ya faɗa cikin taushin murya,jin yanayin da ya yi maganar yasa na sake shi tare da buɗe ido a hankali.Cikin nasa idon na sauke nawa,babu laifi ya saki fuskarsa duk da babu wani annuri.Hannuna na duba sai na ga ashe bottle ɗin rigarsa ne na tsinke,ya juya mini baya kafin ya fiddo waya a aljihu ya yi kiran Jabeer .Babu jimawa ya shigo riƙe da akwatin likitoci.
“Ka duba ta sai ka yi mata allura ” Mu'azzam ya faɗa yana mai waigowa ya dube ni,shi kuwa Jabeer ya matso kusa da gadon da nake kwance.Da sauri na tashi zaune ina mai cewa “wallahi lafiyata lau ban so” Jabeer ɗin bai saurare ni ba ya soma ƙoƙarin yi mini allurar,ban kuwa yi wani tunani ba na gantsara masa cizo a dole ya yi baya yana kallona yayin da shi kuma Mu'azzam yake wani murmushi mai fitar da tsantsan kyawunsa.
Kamar wata yarinya na dire daga kan gado na je bakin ƙofa ina rarrabar ido, Mu'azzam ya kalli Jabeer ya tuntsire da dariya kafin ya ce “zan wuce gida sai mun yi waya” sai ya zo gabana ya buɗe ƙofar,na take masa baya har mota.Wannan karon ni na buɗewa kaina can gidan baya,na takure wuri guda.Shi ma a slow ya soma tuƙin har muka iso gida yana satar kallona ta cikin madubi.Kusan a tare muka shiga falon sai kawai duk muka yi tsaye saboda yadda aka ƙawata shi ,goggonsa Kabira ta zo da sauri ta kamo hannunsa tana cewa “Zeezi ki sauko ga angonki ya ƙaraso” Daddynsa ne ya soma yin taɓi shi da sauran dangin da aka tara a wurin amma banda Ammy wacce ke kallon fuskar ɗanta.
Ƙarar saukowarta yasa na ɗaga kaina sama,budurwar da muka fara cin karo ce a can Duwala gidan Ammy.Ta sha kyawu har ta gaji,kuma babu ƙarya ta haɗu sosai don sai da ta burge ni.Tana isowa falon jikin Mu'azzam ta je ta faɗa ,da dukkan alamu kuma ba wannan ne farkon yin hakan ba duba da ko kaɗan bai yi ƙoƙarin ture ta ba.
Taɓi aka shiga yi a karo na biyu,ni ma haka na samu kaina da taɓawar sai dai fa a can ƙasan zuciyata haka nake jin wani abu kamar ban murna da hakan.
Goggo Kabira ce har yanzu ta ƙara yin magana “kamar yadda kuka sani an daɗe da ɗaura auren Mu'azzam da Azeeza a yau kuma mun shirya ɗan ƙaramin shagali domin tarewarsu” wata irin langwaɓewa ita Azeezar ke sake yi a jikin Mu'azzam wanda har zuwa yanzu bai nuna farin cikinsa ba,muna haɗa ido da shi sai na ga yana aiko mini wani kallo ya tsayar da dubansa kuma a kaina.Na shagala sosai cikin kallonsa na ji muryarta kusa da ni,“ungo wannan furannin je ki ƙawata ɗakin da za a tarbi amarya”goggo Kabira ta faɗa tana mai miƙo mini wani basket mai furanni sai wani gangame fuska take.Na karɓa tare da juyawa na haura can sama,tsaye na yi ina tunanin to wanne ne daga ciki ɗakin amaryar? Daga bayana na ji motsi ko da na waiga sai na ga ita ce ƴar masifar ta biyo ni.
“Zo na nuna miki yadda komai zai tafi” ta faɗa tare da shiga ɗaya daga cikin ɗakunan,tun daga falon wani sihirtacen ƙamshi ne ke tashi ko ina an gyara shi tsaf,ina biye da ita har muka shiga can bedroom nan ne ƙamshin Mu'azzam ya farmaki hancina ban san lokacin da na lumshe ido ba saboda a ɗan zaman da muka yi da shi na fahimci na fara son ƙamshinsa.
“Ki canza wannan zanen gadon ki shimfiɗa ɗaya daga cikin waɗannan ” furucinta yasa na buɗe ido na ga zannuwan gadon da pink da kuma fara.Da ɗan murmushina a fuska na ce “ina ga a shimfiɗa pink ɗin za ta fi kyau”
“A'a farar za ki shimfiɗa ita wannan gobe sai a shimfiɗata in an cire wannan ” ta miƙo mini farar.Ni kuwa da yake sokuwa ce sai cewa na yi “kamar farar za ta yi saurin ɗaukar dauɗa”
Ta langwaɓar da kai ta ce “dama iya daren farko kawai ake buƙatarta” da sauri na sunne kai don zuwa yanzu na fahimta,ina jin lokacin da ta yi murmushi mai sauti kafin ta ce “kin san daren nan ya fi komai muhimmanci a rayuwar ma'aurata,za su san junansu kuma duniya za ta shaida sun zama ɗaya” tana gama faɗa ta fice.
Wani irin zafi ne na soma jin yana taso mini daga ƙasan zuciya,ban san na mine ne ba haka na soma gyaran kamar yadda ta buƙata .Bayan na gama sai na koma gefe ina kallon yadda gadon yayi tsaf,wata guntuwar ƙwalla ta zubo mini na yi saurin goge ta kafin na fito.
Daga nan saman bene nake kallon yadda dangi ke ta yin hidima,shi kuwa gogan sai faman danna waya yake yi amarya kuwa tana can tsakiyar danginta.A gaban idona Jabeer ya shigo,sai kuma a wannan lokacin ne Mu'azzam ya miƙe ya tarbe shi ina ganin sun tunkaro bene na yi saurin rugawa a guje na shige ɗaya daga cikin ɗakunan .
Wani irin duhu ne ke da ɗakin, amma kamar daga sama na soma hango wani haske wanda ya ja ragamar ruhina izuwa gare shi.Ina isa na zube gwiwaina ƙasa tare da kai hannu na buɗe wani ɗan ƙaramin akwati na ƙarfe,da sauri na rumtse ido saboda yadda hasken ya dalle mini ido.Duk da idona a rufe suke hakan bai hana ruhina gane mini wani ɗan mitsitsin littafi ba wanda duk yayi ƙura,page ɗin farko ce ta buɗe kanta harufan da ke rubuce a ciki suka soma karanta mini kansu ba tare da ni na karanta ba,duk wani sirri kuma da ya ambaci kansa haka zuwa cikin kwanyata ya zauna a daidai lokacin da na buɗe idona kuwa wani irin yanayi ne ya riske ni na ƙarfin power......
[18/08 15:13] MRS SADAUKI: *TUKUNYAR MAYU*🏴☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Fateema Abdou dite Mrs Ƙarshen Ƙauna🇳🇪
*FCWA*☀️
________________________
10
Cikin riga na ɓoye littafin kafin na miƙe na je bakin ƙofa,ganin babu kowa yasa na fice da sauri .Kai tsaye ɗakinmu na wuce ban bi ta wani shagalin biki ba,gudun kar Maryam ta zo ta tarar da ni ina karatun littafin yasa na shige toilet tare da buɗe page ta biyu sai dai tamkar an kunna fanka haka dukkan pages ɗin suka dinga buɗe kansu harufan ciki na tashi sama kamar wasu ledodi.Banda idanu babu abin da na zuba musu ina kallo,pages ɗin na gama idawa littafin ya ɓatan dabo daga cikin hannuna.
Wani irin nauyi na ji kaina ya yi mini,kamar makauniya haka idona duk suka disashe.Da lalube haka na samu na fito na kwanta kan bed,gurnani haɗi da nishi nake ji a cikin kwanyata yayin da kuma matattun idona ke nuno mini wani ƙasurgumin daji mai albarkar ruwa masu gudana.A cikin yanayin da ya riske ni sam na kasa sanin taƙamaimai halin da nake ciki.
★MU'AZZAM
Tun da suka shigo gidan aka tarbe shi da zancen tarewarsa da Azeeza ya ji zuciyarsa na tafasa.Ji yake kamar ya yi ihu amma ya daure ya ɓoye damuwarsa har abokinsa Jabeer ya ƙaraso.
Ƙofar ɗakin ya rufe ko kafin ya ce wani abu Jabeer ya furta “ ya kamata ka nutsu domin kar ciwonka na zuciya ya tashi ”
A hasale ya ce “na nawa kuma? Ka duba fa ka gani babu shawara ba komai ake yin walimar nan,Ammy kuma na tsaye ba ta ce komai ba ita kuma mahaukaciyar yarinyar nan har da wani taɓa hannuwa take yi tana murna da kuma zuwa ta gyara gado hum! Ji nake kamar na kama da wuta” Mu'azzam ya ƙarashe faɗa yana mai kawai bango naushi.
Jabeer ya ce “kar fa ka manta kai ne da kanka ka ce kana son Zeezi ba haɗa ku aka yi ba”
“Amma ai soyayyar ƙurciya ce,ni yanzu ban sonta ” cewar Mu'azzam.
“In ba ka sonta wa kake so kenan? Don dole akwai wacce ta canza maka ra'ayi” Jabeer ya faɗa yana mai dafa kafaɗarsa.
Shiru ya ɗan yi kafin ya ja tsuki ya ce “ni babu wacce nake so,kawai dai yanzu Zeezi ba ta gabana ” Jabeer ya ɗan yi murmushi mai sauti ya ce “to kawai ka yi haƙuri ƙila ta sake dawowa gaban naka in wacce ta tare mata ƙofa ta gusa”
Da wani mugun kallo ya kalli Jabeer kafin ya ce “kar ma banzan tunaninka ya baka wai ni Mu'azzam zan iya son wannan mahaukaciyar ”
Yayi ƴar dariya ya ce “ni ai dama ban ce ba kai ne ka furta da kanka hakan na nufin dama tana cikin ranka”
Mu'azzam ya haɗe rai ya ce “na kira ka don ka yi mini maganin damuwata amma kana daɗa mini wata”
“Abokina kai ne ba ka son gaskiya in kana cikin wata matsala maimakon ka duba gaskiyar lamarin amma sai ka bari ego ɗinka ya rinjaye ka.Da ka ƙi da kaso kana son Fateemah,tun ranar da ka ganta ka kamu da sonta a kallon farko amma saboda girman kai gani kake ka fi ƙarfin ka so mace kamar ta.Ka sani yanzu duniya ta ci gaba ba wani abu ba ne don ka so macen da ba ta waye ba,kai ne za ka wayar da ita ta zama classic.In ka ɗauki Azeeza da Fateema banbancinsu ƙalilan ne,ka ga....” cikin tafasar zuciya Mu'azzam ya dakatar da shi yana mai cewa “kai ka ga ban kira ka nan don ka zo ka yi mini surutu ba,in ba za ka bani shawara ka tafi kawai”
Jabeer ya dube shi da kyau kafin ya ce “yanzu ya kake so a yi?”
“Inda na san yadda za a yi zan kira ka ne?”
“Kana ganin fatalwar Nadiya ba za ta iya kai wa Azeeza farmaki ba?”
“Inda za ta yi da tun tuni ta yi,amma ko sau ɗaya ba ta taɓa yi ba.Kaf cikin waɗanda take fito ma irin patient ɗina ne da aka kawo masu jinya”
Jabeer ya ce “ka yi wa kanka tambaya don me sai waɗanda kawai suka zo neman magani wurinka?”
“Ban san dalili ba Jabeer amma tabbas da akwai shi,amma mene ne?”
“Ya kamata mu je wurin teacher shi kawai zai bamu amsa ”
“Mu je” ya furta tare da buɗe ƙofar suka fito,har za su sauka idonsa ya kai ga ƙofar rufaffen ɗaki wanda tsawon shekaru ba a taɓa buɗe shi ba.
“Mu tafi ba mu da sauran lokaci ” Jabeer ya faɗa .Haka Mu'azzam ya bi bayansa,da suka sauko sosai Goggo Kabira ta so tsayar da su amma ya ƙi saurarenta.A motar Jabeer suka tafi gidan teacher,wani tsohon mutum ne mai farin gashi ya tsufa sosai sannan makaho ne.
Amma duk makantarsa ya san ƙamshi dukkan ɗalibansa, wannan yasa su Jabeer na isa ya ambaci sunansu.Gaishe shi suka yi a mutumce kafin su faɗi abin da ya kawo su,teacher ya yi murmushi yana mai cewa “maɗaukakiyar littafin tsira tuni ta bayyana a gidanku,tana ɗaya daga cikin baƙinku.Haƙiƙa mawallafin littafin taswira ya yi gaskiya,kamar yadda ya ce ba za a iya ɗaukar littafin sirri ba sai a ranar da ake gudanar da wani taro a cikin wannan filin gidan.Mu'azzam matarka ta gaskiya ta bayyana,matar da a kullum fatalwar Nadiya ke shakkar zuwanta wannan dalili ne yasa take farmakar patient ɗinka don ta san cewa a cikinsu ne za a samu wannan Goddess ”
Kallon juna suka yi kafin Mu'azzam ya ce “kenan tuni an ɗauki littafin sirrin? To amma ta ya za a yi na gane ita wannan Goddess ɗin?”
“Ita ɗin ta fita daban da saura! Kammaninta sun banbanta da na mutane,in tana tafiya iska ne abokin tafiyarta zai dinga kaɗa gashin kanta yana haskaka idanunta.Saura ƙiris ta mallaki dukkan wasu sirrika na tafiyar da aikin prophecy,muddin ta mallake su a yau to akwai yi yiwuwar gidan gawa ya ɗauki fasanja ”
Ran Mu'azzam ne ya sake ɓaci,da wani irin sauri ya miƙe tsaye yana mai cewa “muddin ina numfashi ba zan taɓa barin hakan ta faru ba.Mu je Jabeer,teacher mun gode sai mun sake dawowa”
Teacher ya ce “ Mu'azzam ka kula da kyau,sannan ina so ka sake yin bitar darussan da muka yi a baya sannan ina so ka sani fansar Aljani ba ɗaya take da ta ɗan Adam ba”
Ba tare da ya ce komai ba suka fito shi da Jabeer,tsabar yadda yake jin zuciyarsa na tafasa shi ne ma yayi tuƙin ya dinga gudu kamar zai tashi sama.Shi kuwa Jabeer sai ƙoƙarin dannar ƙirjinsa yake a haka har suka isa gida, lokacin tuni an shiga sallar asar dakyar ya yin alwala suka shiga masjid.Bayan sun fito suka wuce can cikin gida,kamar wani zararre haka yake kallon duk baƙin da suka zo amma bai ga alamomin nan ba da teacher ya shaida masa.
Ammy ta zo ta ja hannunsa ta soma nuna masa wasu dangin da suka zo bayan fitarsa,sama-sama suke gaisawa sai faman baza ido yake kuwa.Lura da hakan yasa Ammy ta ce “lafiyarka kuwa Mu'azzam? Ko dai patient ɗin da aka kawo ɗin ce aikin ya fi ƙarfinka?”
“An kawo wata patient ne?” ya tambaya da sauri.
Da mamaki Ammy ta ce “au dama ba a sanar da kai ba? Oh! Ƙila aiki ne yasa na sha'afa suna can ɗakin waje” yana gama ji ya bar Ammy ya nufi ƙofa,Jabeer ya take masa baya.
Tun da suka doshi ƙofar suke jin wani irin ɗohi,amma a haka suka shiga.Turus suka yi suna kallon wata matashiyar budurwa wacce jikinta yake da shegen datti ,idonta jawur suke kamar barkono kammaninta kuwa kamar wata halitta daga wata duniya .Sun ƙure ƙarshen fanka sai gudu take wannan ya saka figagen gashin kanta damar kaɗawa.
Mahaifiyarta na ganin Mu'azzam ta taso ta gaishe su,ya ce “tun yaushe ku ke nan? ”
“Jiya cikin dare”
Mu'azzam ya kalli Jabeer kafin ya ce “amma ya aka yi ba ku neme ni ba?”
“Wata mata ce ta ce mana mu zauna a nan” ta basa amsa tare da zayyano masa siffar Goggo Kabira.
“Tun da kuka zo kenan a nan kuke?”
“A'a ɗazu Kando ta fita har zuwa can cikin gidan shi ne na je na nemo ta har muka haɗuwa da wata mata mai kirki ta zubo mana abinci” tana faɗar haka ya gane Ammy ce.
Hannun Jabeer ya ja suka ƙara komawa can ciki,sai dai wannan karon can saman bene ne suka haura.Sawun taku ya gani masu cike da dauɗa ,zuciyar Mu'azzam ce ta soma tsinkewa yana addu'ar kar dai abin da zuciyarsa ke raya masa ya zamana gaskiya.
Idonsa ne suka kaɗa suka yi ja lokacin da ya shiga rufaffen ɗaki ya tarar da babu wannan littafi na sirri wanda aƙalla ya gwada ɗaukarsa ya fi cikon casbi amma ya kasa.
Jabeer kamar ya shiga zuciyar Mu'azzam ya ce “tana iya yi wa kuma ba Kando ba ce ta ɗauki littafin wata ce daban”
Jin abin da Jabeer ɗin ya ce sai ya tuna da Mama wacce ya rufe a wani ɗakin kuma.Da sauri ya tafi can sai dai kuma ita kanta ta yi ƙasa ko sama da dukkan alamu ma ba ta cikin gidan,kai ya dafe ya rasa abin da ke yi masa daɗi.
Haka suka zauna shi da Jabeer suna ta saƙa da warwara yayin da kuma gefe guda ake ta tsara yadda diner ɗin da za a yi a yau za ta tafi.
★FATEEMA
Ban san tsawon lokacin da na ɗauka ba cikin wannan yanayin kafin na samu kaina.Toilet na shiga na tsarkake jikina na zo na yi sallolin azahar da asar kafin na gabatar da magarib.Ina nan zaune kan sallaya aka kira isha'i na miƙe na mayar kafin kuma na yi zaune ina lazumi,a haka Maryam wacce yanzu ta zama ƴar gida ta same ni.
“Ga kayanmu waɗanda za mu saka Ammy ta bamu,ki gwada ki gani ko za su yi miki ” shi ne abin da ta faɗa tana mai cillo mini wata doguwar riga pink an yi mata ratsin fari haka kuma an zuba mata duwatsu masu shegen kyawu.
“Ina za mu je?” ita ce tambayar da na yi mata.Sake da baki take kallona kafin ta ce “wajen diner na Mu'azzam ko?”
Na ɗan taɓe baki don har ga Allah duk na manta abin da ya faru,tashi na yi tsaye na gwada rigar ta kuwa yi mini daidai sai dai ta wurin tsawo ta yi mini tsayi.Sai da Maryam ta gama yaba kyawun da na yi kafin ta shiga toilet ta yo wanka,ni ma sai da na sake yin wani kafin na zo na shafa mai da kwalli sai man leɓe.
Da na saka rigar sai na soma dubarar yadda za a yi ta bar jan ƙasa,Maryam da ta lura da haka sai ta ce “ko na karɓo miki takalmi masu ɗan tudu wurin Goggo Kabira?”
Kamar na shaƙe mata wuya haka na ji,na ce “matar da ta nuna tsantsar tsanarmu ita ce za ki je ki nemi alfarma ai gwara na fasa tafiya”
Ammy ta shigo tana cewa “ya aka yi har yanzu ba ku fito ba?” gaishe ta na yi yayin da Maryam ke shaida mata matsalar da aka samu,“ok ina zuwa.Maryam yi mata kwalliya kafin na dawo” Ammy ta faɗa tare da ficewa.
Maryam ta yi ɗan murmushi kafin ta ce “don Allah anty ki bari na yi miki kwalliyar nan kar Ammy ta ga kamar ba mu yaba da auren ɗanta ba” na buɗa baki zan yi magana kenan sai Maryam ta kamo hannuna,haka na yi shiru kamar kullum na yi zaune ta soma tsantsara mini kwalliya.Tana cikin yi ne wayarta ta yi ringing wacce ban san yaushe ta same ta ba,lambar ƙafata ce Ammy ta tambaya.Har sai da aka kawo mini takalmin Maryam ba ta gama mini kwalliya ba, lokacin da muka