An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
🌳AUREN KADDARA🌳
🌷 Ko BIYAYYA🌷
💃🏼Na bilkisa ibrahim📝📝
1«****» "Kyawawan" dattijaine guda biyu a kayataccen, falonsu dayaji kayan more rayuwa kallo daya zakai musu kagane dattijan ma'auratan suna matukar "so" da kaunar junan su.
Aka kwankwasa kofa tare da sallama suka bada izinin shigowa. Wani kyakykyawan saurayine mai lafiya da kuzari kallo daya zaka masa kagano tsananin kamarsa da dattijan dake zaune afalon dan harya so yafisu kyawu, saboda duk ya hada kyawun dattawan guda biyu,
Yazo ya tsugunnah agaban iyayennasa,barka da yamma dad & mom.
Cikin fara'a suka amsa dad yace babana ya gida ya iyalin ?? Yadan rage fara'a sannan yaca kalau dad. Mom takallesa babanmu yadai naga karage fara'a dan antan bayeka iyalinka, yace bako mai mom.
Dad yace ban yardaba dady akwai matsala, dady bazan juri ganinkaba acikin rashin walwala tabbas nayimasu yaya biyayya kuma kaima kayi mini, dan haka na yanke shawarar kaima yanzu kanemo zabinka ka kara AURE. Da sauri ya dago kai yan kallon dad dinnasa, dad yadaga masa kai alamar hakane
Shima cikin rauni ya girgiza kai tare da fadin dad AURE kuma?? Inji da wadannan ma dad.
Dad kaima dakake da shekaru dayawa aduniya kana mata daya ka hakura saini da ban wuce 30 ba ace inada mata biyu har ana neman nakara ta uku, haba dad dan "ALLAH" KAyi hakuri wallahi bala'in mata biyun nanma neman zautani yakeyi bare uku iba so kuke kurasaniba dad
Bazamu rasakaba dady insha "ALLAHU" sai munga 'ya 'yanka. Hasalima wannan kara auren shine zai samamaka zaman lafiya agidanka damu kanmu, yakama ta kasamu mai kwantar maka da hankali babana. Jibi yanda ka rame ka lalace sai dogon hanci👃da tsayi duk ka fita hayya cinka acikin shekara daya
Tunda aka fara maganar auren ka da yarannan bamu sake ganin dariyar kaba dan haka kaje kayi nazari akan maganar nan kaji. Kayi hakuri konace ka kara dan "ALLAH" yana tare damasu hakuri ya fada tare da shafa kansa.
Dady yasaki ajiyar zuciya yace to dad na gode in sha allahu zanyi kokari bari nawuce gida , mom sai anjima. Tace to dady kagaida gida tafada cikin raunin murya,ya mike ya fice........
🌺billy🌺
{Abdus'salam}💘
[1/14, 4:09 PM] mrs bilkisu: 🌳AUREN KADDARA🌳
🌷 Ko BIYAYYA🌷
💃🏼na bilkisa ibrahim📝📝
2 «*****» suka bishi da kallo hawayen da mom ke makalewa suka zubo, dad ya kalleta haba bilkisu ai dama tunda naga kinyi shuru nasan kuka kikeyi, adda'a yaronnan yake bukata agaremu ba kukaba yasa hannu yana share mata hawayen fuskarta.
Tace hakane alhaji, amma al'amarin yaronnan yana damuna matuka.
Hakane amma muci gaba da yimasa addu'a "ALLAH"ya kawo masa mafita.
To amin alhaji.
Shikuwa abdul'aziz wato dady bayan fitarsa daga gidan iyayensa mota yashiga ya nufi gidansa zuciyarsa ba dadi jiyake tamkar kar yakoma gidan yana isa kofar gidan yay hon mai gadi ya bude masa get yaturo hancin motarsa🚗 zuwa ciki ko gaisuwar mai gadin bai amsaba, bayan yayi parking a ma'ajiyar motocin🚘🚖🚗 yanufi cikin gidan wanda yake da tazara da harabar ajiye motocin
Tunda ya gabato gidan yake jin hayaniya yay tsaki tare da fadin karnukan 🐕🐕 banza, yaturo kofar falon yashigo, ilai kuwa matan nasane sukecin uban danbe da zagin fallasa tamkar ba 'yan uwan junaba
Kallo daya yay musu ya dauke kansa, dakinsa yanufa da sauri ikileema ta sha gabansa tana fadin malam jimana.. yabita da kallon mamaki, tare dafadi bani hanya nawuce. Tarike kugu da hannu daya tace ba inda zakaje saika gayama waccan jakar cewa ita ba komai bace agurinka tafada tana nuna husna da dayan hannunta, husna tazo ta damki wuyan rigar ikileema tace kece jaka banza karamar 'yar iska aike yakamata ya fadama wannan kalmar baniba shashasha kawai, aifa kan kace me danbe yasake har kumewa har suna kokarin fada masa
tsawa yadaka musu waiku wadanne irin shaidanu ne ko so kuke ku maida mini gida gidan gala ne , dan danan suka nutsu ya watsa musu harara wallahi kunji na rantse duk wadda na sake jin muryar ta acikin ku kunsan "ALLAH" saita kama hanyar gidansu da saka mako mai kyau dan nagaji da iskan cinku, inkuma kun cika cikakkun 'yan club ku cigaba. Ni nan dakuke gani nafiku iya iskanci. Yashige dakinsa tare da banko kofa da karfin gaske, sukansu sun razana
Kowa tai tsaki tanufi dakinta, dan suna masifar son dady da tsoronsa.
"Shikuwa gadonsa yafada yana fadin na shiga uku ni abdul'aziz wannan wace irin rayuwace ta dabbobi ya "ALLAH" kakawo mini dauki a lamurana....
🌺billy🌺
{Abdus'salam}
[1/14, 4:09 PM] mrs bilkisu: 🌳AUREN KADDARA🌳
🌷 Ko BIYAYYA 🌷
09093044460
Na bilkisa ibrahim
3 «*****» TUSHEN LABARI alhaji el~mansur adam sa'id sunan mahaifin abdul'aziz (dady) su uku mahaifinsu ya haifa alhaji adam sa'id yola, matan alhaji adam biyu halima wadda suke kira umma itace uwar gida tana da yara biyu ashiru, da salisu,
Sai amarya maryam dasuke kira gwaggo tanada da guda daya mansur, alh adam dan kasuwa ne babba a yola domin in har za a lissafa manyan 'yan kasuwa na yola zai iya zuwa na goma. Gidan alh. adam anayin zama bana jin dadiba domin uwargidansa haj.halima macace mafada ciya sosai, amaryarsa kam tada matukar hakuri haj.maryam,dan haka yaronta mansur yakasance mai hakuri gashi kuma karami acikinsu
Yaran haj.halima sun gado halinta kaf suna bin hudubar ta daki~daki sun raina gwaggo danma suna tsoron babnsu
Amma gwaggo da danta suna shan wahalarsu agidan, har amakaranta kullum wahalar da mansur sukeyi bashida ikon shiga cikinsu yayi wasa saisun dokesa koda gwaggo tagani bata magana saidai taja shi daki ta rarrashesa
Wannan yasa yatashi atsan gwame acikinsu ahaka akaita tafiya harsuka girma su la kammala karatunsu ashiru, da salisu, suka aure bayan kamar shekara uku shima mansur yay aure ya auri diyar kanwar gwaggo sunanta bilkisu, salisu, da ashiru, suka sami aiki dan sunce basa son kasuwa.
Mansur kam yana kasuwa wajan babansu, ana haka ciwon ajali yakama alh.adamu allah ya dauke abinsa ba a rufa shekara ba gwaggoma ta rasu,bayan rasuwar gwaggo mansur da matarsa suka kara shiga halin takura awajen 'yan uwansa da mahaifiyar su sun kwace gadonsa da sunan za a hada ajuya.
Ana haka billkisu tasami ciki mai wahalar wa ko dayau she tana cikin jinya idan mansur yatan bayesu kudin dazai kaita asibiti saisuce basudashi, wannan halin yasashi fara neman aiki amma aikin yaki samuwa
Ga bilkisu da ciki ga mansur ba aikiyi, ga matansu salisu sun takurama ta da aiki duk da wahalar
[1/14, 4:09 PM] mrs bilkisu: Kuyi hakuri ga karshen fage 3
Da takesha ta laulayin ciki dayake ita aarkin hakurice sai tayi
Wannan abubuwan ne suka taru aukai ma mansur yawa, yaje yasanar da dangin gwaggo wani kaninta dayake kano yace yadowo wajansa da zama.....
🌺billy🌺
🌳AUREN KADDARA🌳
🌷ko BIYAYYA🌷
09093044460
Na bilkisa ibrahim
4«******» da yagaya su alhaji salisu sai sukace basu yardaba anaso ne kawai araba musu zuminci
Wannan yasa ya kyalesu bayan kamar sati dayavyashiya kayansu ya aika kano tatashar mota batare da kowa yasaniba,bayan kwana uku suka shirya kamar masu zuwa anguwa sai kano ta , sun isa gidan kawunaa dan madai daici daki hudune agidan sai bayi da kichin irindai ginin kano, anbasu daki biyu suzauna
Ayola kam bayan sun gane su mansur sungudu sai suka kwashe kayan dakinsu
""Tunda mansur yadawo kano sai ya ajiye magar nean aiki gefe yashiga gwagwar mayar kasuwanci, badadewa bilkisu da haihu tanta namiji akasa masa sunan baban ta ABDUL'AZIZ wanda tunda cikin yaimata alkawari sa sunan mahaifinta indai ta hafi namiji,suna kiran yaro da dady.
Tun daga nan kofofin arziki auka kara budema mansu yasai gida mai kyau yasaya ma kawunsa, ya biya musu aikin hajji harda yayyansa🕋🕋,
Tundaga abdul'aziz hai huwa shiru amma wannan baisa ya kara aure ba, bayan shekara sha biyu tasamu ciki tahaifi yan biyu duk mata aka saka sunan gwaggo da mahai fiyarta maryam da fateema anace musu kausar da kairat, sannan dady yana primary 6
Mansur daya zama alhaji el~mansur adam sa'id yola yazama attajiri wanda sunansa baya boyuwa agarin kano yakanje yola yagaida dangin mahaifiyar sa da 'yan uwansa, wadanda haryanzun basa kaunarsa burunsu ma yanzu taya zasu salwantar da rayuwarsa su mallaki dukiyarsa sukeyi, to allah ya shirya su.
{*******« »*******}
Ana haka aiki yadawo da alhaji salisu kano suka dawo tare da iyalisa da umma dan tace bazata zauna ayola ba duk da matarsa bataso hakaba amma bayanda zatayi, sannan yaransu shida badiyya, nuwaira,ikileema,auwal,zainab,ma'aruf.
Bayan sun dawo alhaji sashiru ma yadawo kano yace bazai iya zama akano shi kadaiva shima matarsa daya da tara hudu jabir,nafisa,husna,nabil, gaba dayansu alh el~mansur yabasu gidaje yasaka yaransu a school mai tsada wannan yasa suka boye kiyayyar su garesa sai abayan idonsa, koda yaushe yaransu suna gidan alh. El~mansur suna saka idanu kamar yanda iyayendu suka sakasu, amma dady da'yan biyu basu isa suje gidajensu su sakeba dan hakama dady baya son zuwa saboda shi miskiline bana wasaba agidan summa saiya gadama yake kulasu....
🌺billy🌺
[1/14, 4:09 PM] mrs bilkisu: 🌳AUREN KADDARA🌳
🌷ko BIYAYYA🌷
09093044460
Na bilkisa ibrahim
5 «******» ranar akawayi gari kawun alhaji el~mansur yarasu, mutuwar ta girgiza shi sosai dan kallon mahaifi yake masa, ga shi bai taba haihuwa ba, inna matarsa kuma tace zata koma yola, ba lallashin da baimataba taki, tace bazata iya zamaba inhar ba malam, suyi hakuri zata rinka zuwa akai akai, dubasu haka ya hakura ta tafi tabarsu da kewarta
******* rayuwa taci gaba da gudu tamkar yanda ruwa ke gudana ahanyarsa, dady ya kammala karatusa a kasar amuruka {American} yazama cikakken likeetan mata, tare da jabir aka kaisu amma shiyya ki maida hankali akan karatun sai neman mata kamar bunsuru, ga shaye shaye, acan dady yabarosa shi sainan da wata uku zai dawo,
Badiyya, da nuwaira, da nafisa duk sunyi aure, harma da yara,
Ikileema da husna sune 'yan mata yanzun suna karatu a kunbotso [SA'ADATU RIMI COLLEGE] bama wani kokarine da suba sai girman kan tsiya da iyayi su adole 'ya 'yan masu kudi, yanzuma shawarar da iyayen sukeyi wai zasu kaisu gana suci gaba da karatu.
ABDUL'AZIZ EL~MANSUR ADAM ya zama cikakken namiji kyakkawa ajin farko, dole duk mace mai lafiya ta gansa ta kyasa, sai dai miskiline, amma yanada saukin kai da son mutane, sai dai baya kula mata,dan basa cikin 'yan kayansa, hasalima baya dariya agaban mace,yace yawan yima mace dariya yana kawo su rainaka, shikuma baya son raini.
'Yan biyu ma anzama 'yan mata suna (ss 3 )a school sune ke kokarin zana (s,s,c,e)awannan shekaran
Ayau dady ya sauka kasarsa ta haihuwa kowa yayi murna da dawowarsa, barema kannansa
Bayan yahuta suna zaune a palo shida iyayensa da kannansa suna hira
Dady ya kalli dad, yace dad 'yanmatan kafa sunyi girma mikake basu kaida mom haka??
Dad yay murmushi yace babana kaima baga yanda ka komaba, kazama handsome,komai naka ya canja. Gaba daya suka saka dariya, kairat tace wallahi kuwa yaya ka kara kyau sosai, turai ta karbeka, dama muma mom tayarda dad ya kaimu muyi karatunmu acan wallahi, yaya dan allah kasa baki.
Dady yace a'a wlh koni ban yarda, akaikuba yanda ake lalata yaran mutane, ana koya musu rashin tarbiyya, ai bazan yarda akaimini kanne canba.
Kausar tace yaya baka yarda damuba ne,yace nayarda daku, saidai kinga ku matane kunada rauni, yaci gaba ku gane abinda nake nufi, kuyi hakuri kuyi karatunku anan gida najeria kunji.
{An expert drier can also last long my dear sister's}
Sukace hakane yaya dama danmuga su husna zasune shiyyasa,yace to ina ruwan ku dasu,kuyi harkar gabanku kudai mana,to ko sudin ma wazai kaisu??
Kausar tace abban gidan su husna mana.yace to allah ya kiyaye hanya,ku dai kuyi zamanku akasarku kuyi karatunku,duk inda mutum yake indai yasa kansa karatu to zaiyishi kunji.
Mom tace ato gaya musu dai, kila kai suji maganarka, danmu gani sukeyi bamuyi dai daiba.
Dady yace wlh kunyi dai dai mom, su wadannan mi suka sanine, game da duniya da yanda take tafiya. Haka suka cigaba da hirarsu cikin fahimtar juna.......
🌺billy🌺
[1/14, 4:09 PM] mrs bilkisu: 🌳AUREN KADDARA🌳
🌷ko BIYAYYA🌷
09093044460
Na bilkisa ibrahim 📝📝
6«***** » bayan wata uku da dawo war dady su ikileem suka rikice waishi sukeso itada husna, sunsan halinsa baya son wargi dan haka suka sanar da iyayensu amma ba wadda tasan kudirin 'yar uwarta,
Alhaji ashiru yasami alhaji salisu dazancan yanason hada auren husna da abdul~aziz, alhaji salisu yace aishima burinsa kenan akan ikileema, alhaji ashiru yace to saidai kayi hakuri ita ikileemar ta auri wani tabarma husna tunda nina fara magana, gaskiya yaya bazai yuwuba saidai ahada masa su suduka, rigima dai hartakai kunnan umma mahaifiyarsu, itama tace sai dai ahada masa su suduka, washe gari suka kira alhaji el~mansur gidan umma,sukai masa bayani kudirinsu, yace to shiba zai hanaba amma anemi dady suji tabakinsa,duk abinda yace shikenan,aiko suka hayayyako masa da bala'i wai dan yaga yana dakudi shiyasa yake neman jawo musu raini wajan yaro,to bawani gaya masan da za ayi, yaje ya shirya sati mai zuwa daurin aure.
Haka dad yatafi gida cikin bacin rai dan yasan wannan auren ba don allah aka kulla shiba akwai wani abu aransu, yasamu mom da maganar dayake macece mai matukar hakuri sai tace bakomai allah yasa alkairi,sai ma tarinka kwantar ma dad hankali, suka kira dady sukai masa nasiha sannan suka sanar dashi abinda ake ciki, shima dayake mai biyayyane saiyace ba komai indai su sun yarda to shi bashi daja,dad yace allah yayima ka albarka babana, amin dad nagode.
Haka aka daura aure rankowa agida su dady bayaso an fara daura na ikileema, sai husna da daddare aka kai amare bikin bawani armshi dan dady ma ko gurin daurin auren bai jeba bai kuma gayyaci kowaba,saisu safwan dasukazo daga yola, tare sukai karatu a amerika, safwan,sadiq,jafar,suna kaunar junansu.
Shi angon ma ranar a asibiti ya kwana abinsa,
Wasa wasa dady yaki yarda su hadu da amaren nasa har tsawon sati biyu, wannan yasa suka wanke kafa fuwa sukakai kararsa wajan dad,
Dad yabasu hakuri yace suje gida zai masa magana,sukace to......
Bayan tafiyar su dad yakira dady yace inya taso aiki yazo gida yana nemasa,
Yace to,bayan yataso daga aiki kai tsaye gidansu yataho,yarussuna ya kwashi gaisuwa wajan tsaffinsa,cikin gimamawa, yace mom ina 'yan biyu?? Mom tace suna makaranta, to allah yadawo fasu lafiya.
Dad yace ina ganinka mai han kali babana ashe ba haka bane??dady yace dad minayi?? Dad ya gyara zamansa dazu matanka sunzo nan gidan sunce tunda aka aura maka su baka taba shiga dakinsu ba bama su gankaba.
Dady nasan baka son aurennan kayimi biyayya ne kawai,to dan allah ina rokonka kaji tsoron allah ka bi dokar ubangijinka,domin aure bautar allah ne,kaga yanzun hakkinsu akanka yake,dolene kasauke, kadaure ma zuciyarka karinka kamanta adalci agaresu, ka ajiye maganar raashin sonsu gefe, kaima allah biyayya saiyaji tausayinka ya hadaka da wadda kake so nan gaba ko allah ya canja maka halayensu na banza zuwa na kwarai danka amfana.
To shike nan dad nagode zanyi kokari kayi hakuri,sun tattauna sosai sannan yay musu sallama yatafi gida.....
🌺billy🌺
{💝Mrs abdus'salam}
[1/14, 4:09 PM] mrs bilkisu: 🌳AUREN KADDARA🌳
🌷ko BIYAYYA🌷
09093044460
Na bilkisa ibrahim 📝📝
7«*****» sanda ya isa gidan matan nasa na falo zaune,yaturo kofa da sallama yashigo,suduka suka mike suna masa sannu, ya amsa ciki ciki dan haushin su yakeji ,duka suka rakashi dakinsa,suka zauna bakin gado, shikuma ya shiga bayi danyin wanka,dakin ya burge su sosai ba wani tar kace aciki,daga wardrobe sai gado sai madubi, sai katon hotonsa shi kadai saikuma wani shida 'yan biyu da iyayensa sunyi kyau,sunan suna kalle kalle, ya fito wanka daure da tawul ya ratayo karami a wuyansa yana goge sumar kansa, su duka suka tsura masa idanuwa👀, yadanja karamin tsaki amma basu jiba, gaban madubi yanufa yashafa mai, sannan ya canja kaya zuwa kanana,yada wo yazauna kan kujerar madubi ,ya kallesu fuskarsa ba walwala dazu waya baku izinin fita da har kuka kai karata, wajan dad dina.
Ikileema tace kayi hakuri bazamu sakeba husna ma ta baahi hakuri, ya dan tabe baki to naji daga yau duk wadda tasake fita bada izeninaba inhar ba school zataba to zata hadubda fishina,ya mike yana duban agogosa ni nawuce masallaci.
Sukace to adawo lafiya, bawadda ya tanka ma wa ya fice abinsa,suka hada baki wajan kiran jara babbe dole dai azauna damu, suka tun tsure da dariya harda tafawa
************
Bai dawoba saida akayi sallar ishsha'i,kai tsaye dakinsa ya nufa yay kwanciyarsa wajan karfe 9:pm saiga husna tazo cikin kayan barci anata wani karye karyen jiki waisu mata ko kallo bata isheshiba, sai kuma ga ikileema itama cikin kayan barci, cikin mamaki suka kalli juna, ikileema tace husna miya kawo ki dakin mijina, husna ta kalleta kallon raini mijinki kuma canza dai maganarki yarinya
Ikileema tace husna kinsanni niba kanwar lasarki bace, aikin sanni sarai,dady yadaka musu tsawa kunga dallah malamai kumin shiru kudaina yimin hayaniya aka,su duka suka tabe baki sannan kowa ta zagayo gefensa ta kwanta suka sakashi tsakkiya lokaci daya suka kai hannu zasu tabashi, dasauru ya mike zaune suma suka tashi, kallon banza yay musu to dakuka sakani tsakiya mi kuke nufi da ku biyun zan kwana tamkar akasar arna, yavmike kunga ku sasata kanku tukafin guri ya kure muku inba hakaba zakuyi biyu babu wallahi ya shige bayi abinsa....
🌺billy🌺
{💝Mrs abdus'salam}
[1/14, 4:09 PM] mrs bilkisu: 🌳AUREN KADDARA🌳
🌷ko BIYAYYA🌷
09093044460
Na bilkisa ibrahim📝📝
8 «*****» husna ta watsama ikileema harara, banza mayyar maza saiki kwana, ta tashi tafice dan dama husna akwai zuciya.
Alwala yayo ya fito,ya kalli ikileema data cika tai fam saboda maganar da husna ta fadama ta tayi mata zafi, yace ke tashi kiyo alwala, yanda taga ya hade rai saita mike tayo alwalar ta fito, taje dakinta ta dakko zani da hijjabi,
Sunyi nafila raka'a biyu yay musu addu'oi, sannan ya hau yimata tanba yoyi akan addini?? amma ba wadda ta amsa, tundasu ba islamiyya suke zuwaba,ransa yay zafi yaja tsaki kaini dai wallahi ban moreba, to tayaya za'ayi wannan tabama yaranka tarbiyya?? Azuciyarsa yake wannan maganar,ya tashi ya canja kayansa zuwa na barci yasaka turaren barci, gado ya haye abinsa,itama tamatso kusa da shi dan ganin yanda yakoma karshen gado, amamakinsa saiyaji tana shafashi, ransa ya kara baci, akasar hausa ansan mace da kunya musaman adarenta na farko,amma yazaiyi tunda matarsace, yakuma tuna nasihar iyayensa ta dazu da rana.dole ya daure ya karbi tayinta yabata hakkinta, bayan nutsuwa tazo musu,sai wani farin ciki ya lullube ikileema tuda take hudda da maza bata taba samun gwarzon namiji wanda ya iya soyayya irin dady ba,gaskiya yau tasami natauwa sosai,dukda ta lura dady farin shigane, tana ganin ma yaune rana ta farko da fara sanin mace arayuwarsa, dan ta kula bama wani iya harkar yayiba sosai,amma dai yayi kokari.
Shikam wani irin bakinciki ne yacika zuciyarsa,dukda bai taba kusantar maceba,shi likitane na mata kuma yanada ilimin addini musamman na "fikihu", yayi karatu mai zurfi akansu,yasan dukkanin suffofin mace budurwa,yasan na wadda tasan namiji,ya fitar da huci mai zafi,"ALLAH"kai shaidane ban taba zinaba,amma ka jarabceni da auren mazinaciya,YA " ALLAH" ina neman afuwarka da gafararka tasanadin hakurin zaman dazanyi da ita,"ALLAH" kafini sanin dalilin yin hakan.ya mike yashiga bayi yay wanka,sanda ya fito har tayi barci, wata muguwar harara ya zabga mata, yaja guntu tsaki, ya dauki filo ya dawo kan kujerar dake dakin ya kwanta,zuciyarsa cike da tsanarta......
🌺billy🌺
{💝Mrs abdus'salam}
[1/14, 4:09 PM] mrs bilkisu: 🌳AUREN K'ADDARA🌳
🌷Ko BIYAYYA🌷
09093044460
Na billkisa ibrahim 📝📝
9 «*****»da safe haka ya tashi duk ransa ab'ace wata k'arin tsanarsu yakeji aransa,dan yasan itama husnar duk tafiyar d'ayace,tunda bata da k'awar data wuce ikileema,bayan yayi wanka ya shirya cikin k'ananun kaya yayi kyau, ya tara matan nasa yagaya musu doko kinsa,cikin isa yay musu sallama"
" suka amsa "
"Yay musu kallon second biyar, yak'ara tsare gida ina san sanar daku hanyar dazamu iya zama lafiya daku in kunso,
Na farko bana son k'azanta,
Na biyu bana son yawo,
Na uku bana son hayaniya,
Na hud'u bana son taron k'awaye acikin gidana, bana cin abincin 'yan aiki, ban yarda 'yan aiki sushigar mini d'akiba da nufin gyara, wannan kad'an daga cikin doko kina ida kun kiyaye kun tsira in kuma kun k'iji ba kwak'i ganiba, ya mik'e ya kwashi wayoyin sa da makullin