ni ta yi yana niyyar fita daga hall d'in ba ki
d'aya. Da sauri ita ma ta bi bayansa,bayan ya
isa in da ya ajiye motarsa yana k'ok'arin shiga,
ta sha gabansa tana fad'in "haba yaya Abeed ba
ka ce komai ba, ba ka ga yanda yarinyar take
mutuwar sonka ba".
Ai kuwa sai dai ta mutu in dai ni ne, I hate her,
ya fad'a tare da shigewa mota ya ja da k'arfi da
niyyar ficewa daga wurin, dai_dai lokacin
Fadeela ta fito..........................
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
M Twins 😍 & Auntie M.Jabo ✍🏾🍃
[4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: 💫AN YI
WALK'IYA 10&11 💫
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Bayan kwana uku Mufeeda da Fadeela suka yi
shirin zuwa gidansu Abeed don gaishe da Mumy,
sun taki sa a kuwa don sun tarar da Arfat da
afrat suna gida, su na yin sallama, Arfat ta taso
da sauri ta rungume Mufeeda tana fad'in
"oyoyo! Mufeeda yau a gidanmu" ?
Kafin ta yi magana, Mumy ta fito, nan da nan ita
da Fadeela suka zube su na gaisheta, cikin
fara'a Mummy ta amsa musu, sannan ta ce
"Mufeeda shiru kwana biyu kin daina lek'o mu".
Mufeeda ta ce "eh wallhy Mummy school ne ya
6oyeni", mummy ta ce " ayya!, nima nasan
Mufeeda akwai zumunci, to Allah ya ba da sa
a", suka ce ameen ".
Sai kuma ta kalli Fadeela ta ce da Mufeeda"
Wannan k'awarki ce "?
Murmushi Mufeeda ta yi tana kallon Fadeela ta
ce" eh,
Mummy k'awa ta ce " Allah sarki ya sunanta"?
Tace" Fadeela ", sannu Fadeela Mummy ta fad'a
tare da mik'ewa ta na cewa" Arfat haka za ku
bar bak'in naku ba d'an abun ta6awa "?
Afrat ta ce" Mummy dama yanzu na ke son
tashi", ya dai kamata Mummy ta fad'a tare da
shigewa kitchen.
Sun sha hira sosai, sannan daga bisani Mufeeda
take ce da Arfat ya Abeed na nan kuwa??
Arfat ta ce "a'a, ina za ki ga ya Abeed yanzu, ai
sai wurin k'arfe biyar yake dawowa daga
office". Mufeeda ta ce "ok, Arfat ta ce" ko ta
samu ne "ta fad'a tana murmushi, ita ma
Mufeeda murmushin ta yi, sannan ta ce "sosai
kuwa, Fadeela ce ke masifar son ya Abeed,"
Arfat ta ce "wow! ai kuwa ina ganin Fadeela na
ji ta kwanta mun a rai, Allah ya sa ya Abeed ya
amince, gaskiya da ya yi mata".
Sai kuma ta mik'e da sauri ta na fad'in bari na
je na sanarda Mummy ta zo ga sirikarta",
Fadeela ta hanzarinta ta rik'o hannun Arfat tana
Murmushi ta ce "don Allah kar ki gaya mata
yanzu bari sai mun tafi Allah kunya nake ji, ita
kanta Mufy ta san ba halina ba ne cewa ina son
wani kawai na d'auki son yayanki a wani
6angare na k'addarata, amma kwata_kwata
mace ta ce tana son namiji baya burgeni", ta
k'arashe maganarta da d'an guntun hawaye.
Dukan su jikinsu ya yi sanyi Arfat ta ce "in dai
mummy ce ba ta da matsala Allah ki daina ma
Jin kunya don ta saba ganin 'yan mata
kala_kala masu zuwa neman ya Abeed".
Har wurin k'arfe shida Abeed bai dawo ba, don
haka suka yi shirin komawa gida, mummy ta
had'a musu sha tara ta arziki, sannan ta saka
driver ya kai su gida.
Sai wurin k'arfe bakwai ya shigo gidan , bayan
ya yi wanka ya ci abinci, mummy ta same shi
tace ta na son yin magana da shi. Murmushin
gefen kumatu ya yi sannan ya ce "ina Jin ki
Mum".
Mummy ta fara magana "Abeed dama akan
maganar aurenka ne, gaskiya ya kamata ka
nutsu kasan mai kake yi zuwa yanzu, ka ajiye
duk wani shirme da ke ranka, ka za6i matar
aure ka yi aurenka ya fiye maka, kuma mu ma
zamu fi samun kwanciyar hankali, don na gaji da
zaryar da 'yan mata ke mana a cikin gidan nan".
Juyo da dubansa ya yi sosai gareta, sannan ya
ce "Mum yau ma wata ta zo kenan"?
Mummy ta ce "eh yarinya mai hankali da kunya
da za ka bi maganata da ka nemeta, don daga
gani ' yar gidan mutunci ce".
Yace "Mum ba ki gane ba ne ni fa duk 'yan
matan da ke zuwa gidan nan ba ni na ke cewa
su zo ba,in fact wasu ban ma ta6a ganinsu ba,
kuma har yanzu ban samu wadda na ke so ba,
please Mum adaina takura ni akan wad'ancan '
yan matan wahala ce bata ishe su ba that's all".
Da haka ya mik'e yana shirin tafiya Mummy ta
ce "yanzu Abeed za ka so ' yan uwanka su
Arfat su fad'a irin Wannan halin a fad'i irin
abinda ka fad'a a kansu, don nasan yadda ka ke
son su".
Ya ce "no Mummy nasan ba za su yi irin
wannan halin ba, Mummy ta ce" shi kenan dai,
idan Daddynku ya dawo za mu tattauna akan
maganar, je ka kawai"..............
Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃
M Twins😍& Auntie M. Jabo ✍🏾🍃
💫AN YI WALK'IYA 8💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
K'arasawa ta yi in da Mufeeda ke tsaye kamar
an dasata ta ce "mufy ya na ganki a tsaye,
bayan ya tafi dama nasan ba lallai ya amince da
buk'ata na ba".
Cikin yak'e Mufeeda ta ce "kar ma ki yi wannan
tunanin Fadeela, zai so ki da yardar Allah, yanzu
ma don bai ganki ba ne na tabbatar idan ya yi
ido hud'u dake ba abinda zai hana ya so ki".
A jiyar zuciya Fadeela ta yi, sannan ta ce "ta
yaya zan kuma had'uwa da shi bare har ya
ganni?? Kar ki manta, ko sunansa ban sa ni ba,
bare in da ya ke".
Murmushi Mufeeda ta yi, ta ce " idan akan
wannan ne ki kwantar da hankalinki kamar
tsumma a randa, idan kullum kike son ganin
Abeed za ki gan shi da yardar Allah."
Cikin mamaki Fadeela ta ce "wow! nice name,
sunansa kenan"?
Mufeeda ta gyad'a kai alamar eh, Fadeela ta
cigaba da fad'in "amma mufy ta yaya zan gan
shi duk lokacin da na ke so ya gaya miki sunan
unguwarsu ne, ko wurin aikinsa ?"
Dariya Mufeeda ta yi sosai sannan ta ce"
wannan kuma sai kin ba da wani abu sannan
zan gaya miki, "6ata rai Fadeela ta yi cikin sigar
wasa ta ce" dad'ina da ke kenan, yanzu za ki
fara ja mun rai tunda kin ga ina son ji ".
Tafiya Mufeeda ta fara tana cewa" shi kenan
tunda ba kya son ji, da tuni kin mik'o wani abu,
"gabanta Fadeela ta tara tare da cewa" haba
friendy ko haka ki ka bar ni ai kin ja mun rai,
don Allah ki gaya mun", ta k'arashe maganar
kamar za ta yi kuka.
Mufeeda ta ce "don't cry k'awata, he's my
cousin", waro ido Fadeela ta yi tare da daka
tsalle ta rungume Mufeeda tana cewa "don
Allah da gaske kike yi mufy"?
Mufeeda ta ce" yes da gaske ne ko gobe ki ke
so zan kaiki gidansu ya Abeed, "Fadeela ta
kuma k'ank'ameta tare da cewa amma na ji
dad'i Allah ya sa hakan ya zama silar cikar
burina." Mufeeda ta ce "ameen, sannan ta duba
agogon wayarta ta ce" gaskiya Fadeela dare
yayi fa, gashi lunching d'in an fara a makare bari
na kira driver ya zo, sai ya fara kai ki gida,
sannan sai mu wuce ".
Fadeela ta ce" gaskiya kam don kar ayi mana
fad'a kinsan hajiya idan ta fara," suka saka
dariya.
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
[4/11, 2:54 PM] : 💫AN YI WALK'IYA 12&13
💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Ana kiraye_kirayen sallar isha'i Daddy ya dawo,
kaitsaye masallacin manne da gidan ya nufa
domin sauke farali, bayan an idar da sallah tare
suka fito da Abeed zuwa cikin gidan, suna tafe
suna hirarsu irin ta d'a da uba, Mummy suka
tarar a parlor ta na jiran k'arasowar mai gidan
nata, cikin fara'a da girmamawa ta yi masa
sannu da zuwa, tana fad'in "dama na ce yanzu
haka masallaci ka wuce", Daddy ya ce "eh na
shigo ana shirin ta da sallah na ce bari na yi
sallar in yaso kawai na shigo gaba d'aya" ya
fad'a yana murmushi
Mummy ta ce "gaskiya kam, yanzu dai ga abinci
nan an kammala kai kawai mu ke jira", ok, bari
na je na watsa ruwa takun, Daddy ya fad'a ya
na shirin barin wurin.
Sai wurin 8:30 suka zauna cin abincin, bayan
sun kammala ne kowa ya yi hani'an, don su
Abeed har sun bar wurin, Mummy ke sanar da
Daddy maganar Abeed, ta k'arashe maganar da
cewa "gaskiya Alhaji ya kamata a d'auki mataki
akan maganar Abeed, don yanzu kusan
sa'anninsa duk sun yi aure, wasu har sun fara
tara yara, amma shi shiru ko zancen auren ba
ya yi, ni abinda ma ya fi damuna shine k'udirin
da ya d'auka ya saka a zuciyarsa na lallai shi
sai 'yar gidan hamshak'in mai kud'i zai aura,
bayan da talaka da mai kud'i duk na Allah ne".
Gyd'a kai Daddy ya yi, ya ce "haka ne, amma kin
san abinda za a yi"?
Mummy ta ce " a'a, ya ce "dama Alhaji Usman
tun kwanakin baya yake maganar mu had'a
Abeed aure da 'yar wajensa Hafat, na ce da shi
sai na yi shawara da ke, da kuma shi Abeed
d'in, don bana son na takura shi akan abinda
baya so, shi yasa na ba shi dama duk tsawon
wannan shekarun, amma tunda abun na shi haka
ya zama, lallai_lallai ki gaya masa ya je ya ga
yarinyar su daidaita kansu, tunda ai yasan gidan,
don Alhaji Usman ba 6oyayyene ba a wurinsa."
Mummy ta ce "Allah dai ya sa ya amince, don
lamarin na Abeed sai addu'a", Daddy ya ce "da
kakkausar murya za ki gaya masa ni na ce ya je,
idan dai ban da k'uruciya yaran gidan Alhaji
Usman mai za a nuna musu, suna da tarbiya ga
hankali ga ilimi, amma shi ya tsaya neman
k'yale_k'yalen duniya da ba zai anfaneshi da
komai ba sai wahala".
Mummy ta ce " wallahi kam, ai yaran yanzu
ba sa gane abinda ake hango musu, sai abinda
zuciyarsu ta raya musu shi suke yi, bayan
bahaushe yace " son zuciya 6acinta".
Daddy ya ce "sosai Allah dai yasa mu ga
ne", mummy ta bi shi da ameen".
*********
Tun da safe Abeed ya yi shirin zuwa office
kamar yadda ya saba, duk safiya kafin ya wuce
office sai ya je ya yiwa mummy sallama ita da
Daddy in dai ya na gari ko bai yi sammakon fita
ba.
Bayan ya shiga mummy ke sanar da shi
yanda suka yi da Ddynsa akan maganar neman
auren 'yar gidan Alhaji Usman, zaro ido waje ya
yi yana fad'in "Mum wai wani Alhaji Usman"?
Mummy ta ce" akwai wani Alhaji Usman bayan
aminin Daddyn ku"?
Mere baki gefe ya yi, sannan ya ce "Mum mun
San fa komai gameda Alhaji Usman kawai dai
muna shiru ne."
Fito da ido waje ta yi, ta ce" mai ka sa ni game
da shi? yana da wani mugun Hali ne"?
Abeed ya ce "no ba abinda na ke nufi ba kenan,
kawai dai a takaice yaron Daddy ne, don dai
Daddy ya taimaka masa ya ba shi companyn sa
da ke bompai ne ya na kula da shi, shi ne kawai
ake ganinsa wani mai arzik'i, kin ga kuwa Mum
kamar ni haka, ta yaya zan auri 'yar yaron
babana!!! Ai na ci baya sosai, gaskiya mum
bazan ma iya ba."
Mummy da tunda ya fara magana take tafa
hannu tana sallati tace "yanzu Abeed tanan ka
6ullo kuma"?
Ya ce " Mummy don dai kin san Daddy da rik'on
abokanai ne na tun k'uruciya amma ba don haka
ba, ina laifin ko a cikin manya_manya attajiran
garin nan ya nema mun 'yar wani perhaps da na
amince na yi manage da ita."
Mummy kam tuni ta dask'are a gurin don
mamaki, tace "au maneji ma za ka yi da ita"? To
bari Alhaji ya dawo na gaya masa, gaskiya ya
nemo mai ruk'iyya ya duba ka don ina ga ba
zaka rasa jinnu ba".
Dariya sosai Abeed ya yi sannan ya ce
"Mum wallahi ras na ke, kawai dai na gaya miki
abinda ke zuciya ta ne," sai kuma ya kalle
agogon dake daure a hannunsa ya Ce "Mum
gaskiya na makara bari na tafi sai na dawo,"
Mummy tace "Allah ya kiyaye hanya", yace
"ameen tare da ficewa daga
d'akin......................
Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃
[4/11💫AN YI WALK'IYA 9💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Cikin 6acin rai Abeed ya koma gida, parking
kawai ya yi ko kulle motar bai yi ba, ya wuce
part d'in sa, ransa a dagule yake gaba d'aya,
yana tunanin wai yaushe ne burinsa zai ciki, ya
samu yarinyar da ta dace da shi, wacce ya ke
mafarkin samu, domin shi kansa yanzu ya
hak'ik'an ce da ya na buk'atar aure, amma
matsalar duk 'yan matan da ke sonsa yanzu ya
raina arzikin iyayensu, duk da cikin su babu
wadda za a d'auka ace babanta matsiyaci ne,
don dai shi ya d'auki k'atoton buri ya sakawa
zuciyarsa, dole sai 'yar mai hannu da shuni,
lokaci d'aya ya tuna da wacce akace tanasonsa,
wai babanta yayi rik'on logal government, dai
rainin wayo, wani dogon tsaki yaja, yadan juya
kwanciyar sa, ya kalli a gogon d'akin yana
lumshe ido.
*********
Goggo wacce nake tunanin y'ar uwar Dadyn su
Abeed ce, zaune take tareda Mumy suna hira,
Abeed ne ya shigo ya gaishesu cikin sakin fuska
sannan ya wuce d'akin sa, nan suka fara hirar
yau da kullum, har Goggo ta gangaro akan
abinda ya dad'e yana damun ta,
"hajiya yaran yanzu sai a hankali, sam basa
tunani basa naziri, yanzu za ku ga wasu yaran
masu kud'i idan za su yi aure sai su rik'a
hangen wadda mahaifin ta ya dame nasu ya
shanye da naira, don zilama, maimakon su nemi
dai_dai su, tunda Malam bahaushe ma ya ce
"dai_dai ruwa dai_dai tsaki, kuma kowace
k'warya da abokin burminta" sannan ma ina
laifin su yi k'asa_k'asa su nemi 'yar talaka
bawan Allah suma su samu su lasa, kinga ai an
taimaki juna an rufawa juna asiri ta wannan
hanyar, amma ba a yi saboda buri ya cikawa
masu irin wannan halin zuciya, kowa sai dai-dai
shi," Mumy tace "Wallhy zancen ki dutse
Goggon yara, nima abin yana damuna,
musamman idan naga halin yaronnan banajin
dad'i sam, amma kinsan kosu talakawan akwai
nasu sabida sai su k'wallafa dogon buri wa
yaran su, su mayar da yayan nasu kamar jari,
domin wasu sai ka ga sun zaune jiran mai d'an
maik'o_maik'o har yarinya ta tsofe a gida, ba
iyayenba ba ' ya'yan ba, kije gida ki rasa gane
uwa da yaran gida, akwai wani gida da mukaje
ta'aziya, a gidan naga mata 'yar kyakyawa,
wacce nake tunanin zata haifi yara biyu ko uku,
nake tambayar matar gidan, an mata amarya ne,
dan tare na gansu, sai take cemin ai 'yar kice
wance, wallhy saida na kai zaunedDan mamaki,
na tuna yarinyar sa'ar Muhammad ce fa! Amma
har yanzu tana gida," Goggo ta saka dariya, "
kin bani dariya, wai an miki amarya ne" itama
Mumy dariyar tayi suka ci gaba da hira" wannan
zamanin kowa kwad'ayi ya yi masa yawa, bayan
sun mata Allah ke yin komai, domin kowa an
riga an rubuta k'addararsa tun kafin ya zo
duniyannan, we just trace, sai ka ga budurwa ta
zauna jiran Mr right har ta tsofe tun tana samun
masu zuwa har lokacin ta ya wuce ya zamana
bata samu, ta tashi a tutar babu, k'arshe sai ta
auri wanda bataso, sabida da yawa masu
wannan burin, wallhy basa auren mazan da
zuciyar su takeso, saidai dan kud'i, su tashi ba
wan ba k'ani, ta yi haihuwar guzuma 'ya kwance
uwa kwance, ba mai d'an maik'o_maik'o ba mijin
kwatakwata" nan ma saida suka dara, Goggo
tace, " nifa kina magana kina saka engilishi,
kuma kinsan ba ganewa nakeyiba," sukayi dariya
gaba dayan su, Goggo tace, " Allah ya sa masu
wannan halin su gano su bari dan ba alkhairi
acikinsa" ameen Mumy ta amsa dashi,
Na kalli M Twins nace "nifa al'amarin Abeed
yana bani mamaki domin ya d'ebo da zafi, kace
sai 'yar wane ko wane," M. Twins tace " ?kedai
bari Aunty Jabo, Allah na d'auka irin wannan
abin matane kawai keda wannan hali, ashe har
maza ma sunayi, abin kunya, amma hausawa
sun ce "kowa ya d'ebo da zafi bakinsa"..........."
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
M Twins 😍 & Auntie M. Jabo ✍🏾🍃
[4/11, 2:54 PM]💫AN YI WALK'IYA 14&15 💫
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Daddy na dawowa Mummy ta kwashe yanda
suka yi da Abeed ta fad'a masa, ai kuwa ya yi
ta fad'a, nan take ya d'auki waya yace "da
Abeed duk abinda ya ke yi ya ajiye ya zo yana
kiransa", Abeed ya ce "to Daddy ga ni nan
zuwa" don dama ya san sai an yi haka, cikin
abinda bai fi 10 minutes ba ya shigo gidan,
kaitsaye parlourn Daddy ya nufa, bayan ya
gaishe su, Daddy ya fara magana "Abeed ka
saurare ni ka ji abinda zan gaya Maka, domin
maryam ta gaya mun duk yanda ku ka yi da ita,
to bari ka ji bazan d'auki wannan shashancin ba,
dole ka bi maganata idan ba haka ba, ka sanni
sarai".
Rausayar da kai Abeed ya yi ya ce "Daddy
dama abinda ya............" dakatar da shi Daddy
ya yi ta hanyar d'aga masa hannu, yace "ba na
son jin wata magana yanzu kawai tashi ka je ka
yi abinda na saka ka".
Jiki a sanyaye Abeed ya tashi yana fad'in "to".
Daga nan dakinsa ya wuce, amma zuciyarsa a
cunkushe take yana tunanin meye mafita, don
dai shi ya hak'ik'ancewa zuciyarsa ba zai ta6a
auren 'yar gidan Alhaji usman ba, ya san
kwata_kwata ba ajinsa ba ce, da wannan
sak'e_sak'en har barci ya yi awon gaba da shi.
Ko da ya tashi da safe fuskar nan tasa ba
annuri, su Arfat ma da suka ga yanayinsa tuni
suka kama kan su, tare da gimtse dariyar da ke
cin su, domin mummy ta gaya musu duk abinda
ake ciki, bayan ya fita ne Arfat ta kalli Afrat ta
ce "ni wallahi gwanda da Daddy ya yi wa ya
Abeed haka ko ya maida hankali ya yi auren, mu
ma mu fara ganin babies a gidanmu".
Afrat ta ce "ni kuma gani na yi da Daddy ya
kyale shi ya za6a da kan sa, idan ya ga bai
samu wadda ya ke so ba ai dole ya yi hak'uri ya
auri wata,kuma ni yaran gidan Alhaji Usman ba
su yi mun ba, sai gwalli da iyayi amma ba su da
wani kyau".
Murmushi Arfat ta yi sannan ta ce "Ai k'arshen
mai ruwan ido ke nan".
Bayan ya dawo daga aiki mummy ta takurashi
akan ya je su gana da Hafsat, dole ba yanda ya
iya ya yi shirin zuwa gidan Alhaji Usman.
Duk da ya saba shiga har cikin gidan a duk
lokacin da ya je, amma wannan zuwan da ya yi
tsayawa ya yi a inda ya yi parking motarsa, sai
da mai gadin gidan ya ga ba shi da niyyar shiga
ciki don ya ga ya dade a tsaye sannan ya je ya
ce da shi, "yalla6ai Alhajin ya na ciki ka k'arasa
mana", juyawa ya yi ya kalleshi ya ce "ai ba
wurinsa na zo ba, ka je ka ce ana kiran Hafsat"
Mai gadi ya ce "to bari na je na gaya mata" bai
fi minti biyu da tafiya ba, ya dawo ya ce "ta ce
tana zuwa".
Hafsat kuwa tunda mai gadi ya sanarda ita ana
sallama da ita, ta tambaye shi waye ya ce da
ita Abeed ne, ta shiga tsallen murna, dama ba
ta dad'e da fitowa daga wanka ba, nan da nan
ta hau kwalliya a fenta can a manna can har ta
gama, ta fito cas da ita.
Dama mai gadi ya gaya mata yana bakin gate so
direct can ta nufa, ana tafe ana yauk'i, kamar
ba za a taka ba, sai kuma jikinta ya yi sanyi
lokacin da ta fara hangoshi, don yanayinsa ya fi
kama da wanda aka aikowa sak'on mutuwa, sai
ta fara tunanin ko wani mugun sako ya kawo
mata ne! Daurewa ta yi ta k'arasa inda ya ke
ta masa sallama tare da fad'in "sannu da zuwa",
sallamar kawai ya amsa ya yi shiru, sun yi
kusan 4 minutes ba wanda ya k'ara cewa komai,
sai can Hafsat ta ce "ai da ka zo mun k'arasa
ciki ko"?
A'a kawai ya ce da ita, ta ce" ai tsayuwar ce ba
dad'i, ko za ka zo mu koma daga can wurin ta
yi nuni da wani wuri d'an nesa da su kad'an da
aka sawa rumfa tare da resting chairs, ya ce
"ba zama zan yi ba, don yanzu haka bai fi 5
minutes na tafi ba", Hafsat a ranta ta ce anya
kuwa Abeed ya na sonta? wata zuciyar ta ba ta
amsa da cewa ai da yana sonki da tunda kika zo
kin gani a fuskarsa, kawai dai........... Abeed ne
ya katse mata tunani ta hanyar yin magana,
yace "ba sai na miki dogon bayani, don na San a
gida an miki bayanin komai, duk da dai ke ban
san tunaninki akaina ba, amma ni zan gaya miki
gaskiyar abinda ke zuciya ta, ni ban yarda da
wannan auren had'in ba, kuma ba zan iya
bijirewa maganarsu ba, kuma ke kin san duk
burin mace bai wuce ta samu miji mai sonta da
kaunarta ba sannan yake kuma tausayinta ba,
don shi ne a kowane irin hali zai kasance tare
da ita, idan dai ki na buk'atar hakan to kada ki
kuskura ki amince da aurena, shawara ce na ke
ba ki idan ki d'auka kin taimaki kan ki, idan
kuma ba haka ba a shirye na ke da d'aukan duk
wani k'alubale sannan zan aureki, smma zaki
rasa duk wayanchan abubuwan idan kin shirya
bismillah!!".
Bai jira abinda za ta ce ba, ya fad'a mota ya
yi mata key ya fice daga gidan.
Hafsat kuwa ta fi k'arfin 10 minutes a tsaye a
wurin tana maimaita kalamansa, sai da ta ga
hakan ba mafita ba ne ta shuri k'afafuwanta ta
shige ciki.............
Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃
[4/11, 2:54 PM] 💫AN YI WALK'IYA 6&7 💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Tun da safiyar ranar mubarak yake ma Abeed
waya akan kada ya manta please, yamai SMS ba
adadi, k'arshe ya yarda zai tafi, dan har ya
shirya dojewa.
Sai wurin k'arfe tara da minti ashirin da biyar
Abeed da tawagarsa suka shiga hall d'in, cikin
takun isa da k'asaita yake tafiya, ya rufe idonsa
da wani shade bak'i kaitsaye gurin da aka
tanada domin zaman su suka nufa.
Wohoho! Ku zo ku ga 'yan mata yanda suka
zuba masa na mujiya suna kallo, kai basu kad'ai
ba har mazan dake gurin kallonsa suke yi
tamkar sun ga wata sabuwar halitta, shi kuwa
gogan naku ko kallo ba su ishe shi ba, tafiyarsa
kawai yake cikin isa da izza har ya isa wurin
zaman su.
Tun shigowarsa wata yarinya mai amsa sunan
Fadeela, muka ga duk ta rud'e ta rikice, sai wani
dube_dube take kamar mai neman wani abu.
Sai can kuma muka ga ta nufi wani side na
musamman, domin an yi decorating gurin sosai
fiye da inda take zaune,
Da sauri ta k'arasa wurin har tana tuntu6e, tare
da rik'o hannun wata budurwa wadda ba zata
wuce sa'arta ba, sannnan ta ce "Mufy ta so don
Allah ki gan shi shine wanda na ke yawan yi
miki maganarsa" ido Mufeeda ta zuba mata na
d'an lokaci sannnan ta ce" wai ki na nufin guy
d'in da ba ki da aiki sai na maganarsa shine ya
zo nan gurin,"?
Fadeela ta ce "eh tare da langa6ar da kanta
gefe,"
Mufeeda ta yi farr da ido,sannnan ta ce "gaskiya
fady kin ban kunya, duk yanda kika h'adun nan,
kuma kike gwara kan samari son ranki amma ki
6ige da baran soyayya akan saurayin da ko
sunansa ba ki sa ni ba".
Dafa kafad'arta Fadeela ta yi tare da cewa
"friendy ba ki ga guy d'in ba ne that's why kike
wannan maganar, kin san first class guy, full
options to shi ne, ni tsoro ma nake kar ki gan
shi ki kasa controlling kan ki ki je ki shigar da
kan ki ba ni ba" ta k'arashe maganar tare da
sakin dariya!
Duka Mufeeda ta kai mata, ta goce sannnan ta
ce "an gaya miki akwai wanda ya isa ya ture
gwamnatin k'albina ne," Mufeeda ta cigaba da
fad'in "ni dai zo ki nuna mun in da ya ke, ga
ganshi, na cigaba da abinda na ke yi".
Fadeela ta ce "na ga dai sun nufi wurin da aka
tanada don manya_manya abokan ango" ta
fad'a tana d'an kalle-kalle
OK, "to ta yaya zan yi na gane shi??" Cewar
Mufeeda, nari mu je na nuna miki shi ko daga
nesa ne, d'an nesa da su Fadeela ta tsaya take
nunawa Mufeeda shi, ba tare da ko na kusa da
su sun gane abinda suke yi ba.
Tun da Mufeeda ta hangoshi take wasiwasin
wani abu a zuciyarta, sai da ta zo daf da shi
sannan ta tabbatar da abinda take zato. Sallama
ta yi sannan ta ce "sannu yaya Abeed" Jin an
kira shi da yaya, ya tilasta masa d'agowa da kan
sa domin ganin mai magana.
Fuskarsa ya d'an saki sannan ya ce " yawwa
sannunki", ta cigaba da fad'in ashe kai ma ka zo
bikin k'awarmu"?? Jin bai ce komai, ta ce
"angon ne abokinka ke nan"??
kai ya gyad'a mata kawai, ta ce" ai ni amaryar
ce close friend d'ina".
Jin ya kuma shiru ta ce "yaya ba ka son zuwa
gidanmu su Arfat ne kawai ke zuwa".
Hmm! kawai ya ce, nan ma shiru ne ya kuma
ratsawa, sai da ta ga shirun yayi yawa ta ce
"dama akwai maganar da ta kawoni wurinka
idan ba za ka damu ba ka ba ni 5 minute's
please", kamar ba zai yi magana ba, sai can ya
mik'e ya yi mata nuni da su fita daga gurin.
Gefe suka koma, sannan ta fara masa bayanin
abinda ya kawota, ta k'arashe maganarta da
cewa don Allah yaya ka taimakawa k'awata ba
ka ga yadda ta ke sonka ba."
Bud'ar bakinsa sai ya ce "waye mahaifinta"?
Cikin rashin fahimtar maganarsa Mufeeda da ta
ce" Babanta dai d'an siyasa ne", ya ce
"muk'amin meye da shi"?
eh, to ni dai abinda na sa ni ya ta6a rik'on
k'warya a local government".
"What!" ya fad'a da k'arfi, yana had'e fuska,
daga haka bai k'ara cewa da ita komai ba, sai
ga ni ta yi yana niyyar fita daga hall d'in ba ki
d'aya. Da sauri ita ma ta bi bayansa,bayan ya
isa in da ya ajiye motarsa yana k'ok'arin shiga,
ta sha gabansa tana fad'in "haba yaya Abeed ba
ka ce komai ba, ba ka ga yanda yarinyar take
mutuwar sonka ba".
Ai kuwa sai dai ta mutu in dai ni ne, I hate her,
ya fad'a tare da shigewa