mota ya ja da k'arfi da
niyyar ficewa daga wurin, dai_dai lokacin
Fadeela ta fito..........................
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)
WHATSAPP NO:
07039625239
M Twins 😍 & Auntie M.Jabo ✍🏾🍃
[4/11, 2:54 PM] 💫AN YI WALK'IYA 10&11
💫
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Bayan kwana uku Mufeeda da Fadeela suka yi
shirin zuwa gidansu Abeed don gaishe da Mumy,
sun taki sa a kuwa don sun tarar da Arfat da
afrat suna gida, su na yin sallama, Arfat ta taso
da sauri ta rungume Mufeeda tana fad'in
"oyoyo! Mufeeda yau a gidanmu" ?
Kafin ta yi magana, Mumy ta fito, nan da nan ita
da Fadeela suka zube su na gaisheta, cikin
fara'a Mummy ta amsa musu, sannan ta ce
"Mufeeda shiru kwana biyu kin daina lek'o mu".
Mufeeda ta ce "eh wallhy Mummy school ne ya
6oyeni", mummy ta ce " ayya!, nima nasan
Mufeeda akwai zumunci, to Allah ya ba da sa
a", suka ce ameen ".
Sai kuma ta kalli Fadeela ta ce da Mufeeda"
Wannan k'awarki ce "?
Murmushi Mufeeda ta yi tana kallon Fadeela ta
ce" eh,
Mummy k'awa ta ce " Allah sarki ya sunanta"?
Tace" Fadeela ", sannu Fadeela Mummy ta fad'a
tare da mik'ewa ta na cewa" Arfat haka za ku
bar bak'in naku ba d'an abun ta6awa "?
Afrat ta ce" Mummy dama yanzu na ke son
tashi", ya dai kamata Mummy ta fad'a tare da
shigewa kitchen.
Sun sha hira sosai, sannan daga bisani Mufeeda
take ce da Arfat ya Abeed na nan kuwa??
Arfat ta ce "a'a, ina za ki ga ya Abeed yanzu, ai
sai wurin k'arfe biyar yake dawowa daga
office". Mufeeda ta ce "ok, Arfat ta ce" ko ta
samu ne "ta fad'a tana murmushi, ita ma
Mufeeda murmushin ta yi, sannan ta ce "sosai
kuwa, Fadeela ce ke masifar son ya Abeed,"
Arfat ta ce "wow! ai kuwa ina ganin Fadeela na
ji ta kwanta mun a rai, Allah ya sa ya Abeed ya
amince, gaskiya da ya yi mata".
Sai kuma ta mik'e da sauri ta na fad'in bari na
je na sanarda Mummy ta zo ga sirikarta",
Fadeela ta hanzarinta ta rik'o hannun Arfat tana
Murmushi ta ce "don Allah kar ki gaya mata
yanzu bari sai mun tafi Allah kunya nake ji, ita
kanta Mufy ta san ba halina ba ne cewa ina son
wani kawai na d'auki son yayanki a wani
6angare na k'addarata, amma kwata_kwata
mace ta ce tana son namiji baya burgeni", ta
k'arashe maganarta da d'an guntun hawaye.
Dukan su jikinsu ya yi sanyi Arfat ta ce "in dai
mummy ce ba ta da matsala Allah ki daina ma
Jin kunya don ta saba ganin 'yan mata
kala_kala masu zuwa neman ya Abeed".
Har wurin k'arfe shida Abeed bai dawo ba, don
haka suka yi shirin komawa gida, mummy ta
had'a musu sha tara ta arziki, sannan ta saka
driver ya kai su gida.
Sai wurin k'arfe bakwai ya shigo gidan , bayan
ya yi wanka ya ci abinci, mummy ta same shi
tace ta na son yin magana da shi. Murmushin
gefen kumatu ya yi sannan ya ce "ina Jin ki
Mum".
Mummy ta fara magana "Abeed dama akan
maganar aurenka ne, gaskiya ya kamata ka
nutsu kasan mai kake yi zuwa yanzu, ka ajiye
duk wani shirme da ke ranka, ka za6i matar
aure ka yi aurenka ya fiye maka, kuma mu ma
zamu fi samun kwanciyar hankali, don na gaji da
zaryar da 'yan mata ke mana a cikin gidan nan".
Juyo da dubansa ya yi sosai gareta, sannan ya
ce "Mum yau ma wata ta zo kenan"?
Mummy ta ce "eh yarinya mai hankali da kunya
da za ka bi maganata da ka nemeta, don daga
gani ' yar gidan mutunci ce".
Yace "Mum ba ki gane ba ne ni fa duk 'yan
matan da ke zuwa gidan nan ba ni na ke cewa
su zo ba,in fact wasu ban ma ta6a ganinsu ba,
kuma har yanzu ban samu wadda na ke so ba,
please Mum adaina takura ni akan wad'ancan '
yan matan wahala ce bata ishe su ba that's all".
Da haka ya mik'e yana shirin tafiya Mummy ta
ce "yanzu Abeed za ka so ' yan uwanka su
Arfat su fad'a irin Wannan halin a fad'i irin
abinda ka fad'a a kansu, don nasan yadda ka ke
son su".
Ya ce "no Mummy nasan ba za su yi irin
wannan halin ba, Mummy ta ce" shi kenan dai,
idan Daddynku ya dawo za mu tattauna akan
maganar, je ka kawai"..............
Mum Twins 😍 & Auntie M Jabo 🍃
[4/11, 2:54 PM] 💫AN YI WALK'IYA 21&22💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Haka kuwa aka yi, don bayan teema Daddy ya
nemawa Abeed auren 'yan mata sun kai uku,
duka' ya' yan abokan sa ne , amma yanda ta
kasance da sauran suma haka takasance da su,
don duk a cikinsu bai katarin samun yarinyar da
ya ke mafarkin aura ba, don haka bai yi k'asa a
guiwa ba, wajen neman mafita ba, d'aya bayan
d'aya sai da ya nemi hanyar rabuwa dasu.
Daddy kuwa ransa ya kai k'ololuwar 6aci, don
Abeed ya kunya ta shi a idon abokan sa, kuma
ya watsa masa k'asa a ido, yanzu haka yana
cikin fushi da shi, kuma har yanzu yana nan
akan bakansa, na sai an yi auren kafin lokacin
da ya ce ya cika.
Yau kamar had'in baki, Mrs Saif dani M Jabo
duk mun makara zuwa gidansu Abeed don
d'auko muku rahoto, sai after 10pm muka isa
gidan, kaitsaye babban parlourn gidan muka
nufa, sai dai wayam ba kowa a ciki, said k'arar
A.C da kuma T V da ke ta 6a6atu ita kadai, ni
kam d'aya daga cikin kujerun dake parlourn na
samu na zauna, na juyo da dubana in da Jabo
ke tsaye, na ce
"Anya Auntie jabo yau za mu samu wani labari
kuwa"?
Jabo ta ce
"ni ma abinda na ke tunani ke nan maman
Twins, kalli fa hatta 'yan aikin dake saraftu ko
yaushe ba kowa duk sun shige, ko motsin su ba
a ji."
Na ce
"ko dai d'aki za mu bi su ne kawai"? Jabo ta
ce
"haka ma za mu yi, maybe baza mu rasa wani
abu acan ba, nan da nan kuwa na mik'e, muka
nufi d'akin Abeed, ko da muka shiga mun tarar
ya baje a lafiyayyen gadonsa sai sharar barci sa
yake yi, adole muka fito daga d'akin, tunda babu
abun rubutu a nan, d'akin su Arfat muka nufa
daga nan, sai dai suma duk maganar d'aya ce,
don kuwa suma sharar barcinsu suke yi hankali
kwance, bayan mun fito daga d'akin su afrat,
Jabo ke cewa "ni kuwa Mrs Saif lafiya mutanen
gidan nan yau suka yi barci da wuri haka"?
Na ce
"hmm! Ke ma ke fad'a kin riga ni fad'a ne
kawai, amma nima tunanin da na ke yi ke nan,
amma bari mu koma part d'in Mummy mu gani
ko akwai wani abun d'aukowa a can".
Side d'in mummy muka nufa gadan_gadan,
parlor muka fara shiga, ba kowa, daga nan muka
sulale muka fad'a bedroom d'in ta, nan ma shiru
ba kowa, sai muka yi zaton ko tana toilet ne,
muka d'an saurara amma ba mu ji alamar
mutum a ciki ba , almost 10mnts muna tsaye
muna jiran fitowar Mummy ammma shiru, har
sai da muka tabbatar wa kanmu cewa Mummy
bata part d'in ta kwata_kwata.
Ni kam Mrs Saif har na fara tsorata, na juya na
cewa
"Jabo gaskiya gidan nan ba lafiya ba".
Auntie jabo tace
"Nima abun ya d'aure mun kai, amma idan ba
lafiya ba, ta yaya su Abeed za suna sharar barci
irin haka"?
Na ce
"Da haka kuma, nima ga shi har na fara Jin
barci,gaskiya mu je kawai gobe ma dawo, M
Jabo tace "ni kaina barcin na ke ji".
Har mun fito, da niyyar tafiya sai muka ji kamar
sautin kukan Mummy yana tashi daga part d'in
Daddy, kasancewar ba nisa tsakaninsu, inkiya
Jabo ta yi mun akan na k'araso na ji kunsan
Jabo ba Dama wajen jin kwakwaf, sai da na
matsa daf da windown da ke d'akin na tabbatar
da Mummy ce ke shar6ar kuka, kallon_kallo
muka tsaya yi, muna tunanin mai ya saka
Mummy kuka irin haka, a cikin Daren nan,
maganar Daddy ce ta katse mana tunani, don
son Jin abinda ya ke fad'a ba mu San lokacin
da muka fad'a parlourn ba, Allah ya so suna
cikin d'aki, da asirin mu ya tonu.
Abinda muka ji Daddy na fad'a ne, ya tilasta
mana saka hannayen mu akan bakunan mu,
kada mu yi baran 6aramar fitar da sauti har su
an kara da mu a wajen.
Mummy muka jiyo tana yiwa Daddy magiya akan
ya hak'ura da maganar, koda Abeed zai tabbata
bai yi aure ba, Daddy ne ya fara magana a
hassle ya ce
"kin ga maryam, maganar nan dole a fade ta,
don komai lokaci ne, kuma ita magana lokacin
fita ne da ita, idan lokacin fitar ta ya yi, dole ta
fita."
Mummy muka hango ta yi baya ta zauna sharaf,
mu ma muna ganin haka, muka tattara inamu
inamu muka yi waje. Bayan mun fito ne muke
tattauna girman maganar da muka ji su Daddy
na yi, Auntie jabo ce ta ce
"gaskiya Mum Twins maganar nan ta d'aure
mun kai,"
na ce
"Ai ba ke kadai ba, nifa da ba tare muke ba da
sai nace ba daidai naji ba, ni kai na burina bai
wuce Allah ya kai mu gobe ba, mu zo mu ji
yanda maganar take dalla_dalla ba,"
M Jabo ta ce
"Ai ni ji na ke yi kamar yau na kwana a gidan
nan, don kar mu makara zuwa,"
na ce
"Ai kam dai.
Kuma readers sai ku biyo mu don Jin abinda za
faru.....
Mum Twins 😍 & Auntie M. Jabo 🍃
💫AN YI WALK'IYA 💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
K'arfe bakwan safe a gidansu Abeed ta yi mana,
ko da muka shiga gidan suna ta hada_hadar
had'a breakfast, kasancewar ta weekend, Arfat
da Afrat muka hango a kitchen suna ta faman
aiki, tare da 'yan aikin gidan, don mummy ta riga
ta sabar musu da aiki musamman girki don duk
ranar da ba school tare suke shiga kitchen har
Mummy.
Arfat ce ke wanke hannunta a jikin sink, afrat ta
je ta ce da ita
"ya Arfat na ga har yanzu mummy bata fito
ba, ko lafiya "?
Arfat ta ce
"Yanzu nima na ke shirin dubata, ki cigaba
da duba girkin bari na je, na dawo".
Afrat ta ce
"to "
Sallama Arfat ta ke ta kwad'awa tunda ta shiga
parlourn Mummy, har ta K'arasa bedroom,
sannan ta jiyo muryar Mummy tana amsawa
kasa_kasa, da sauri Arfat ta K'arasa kan gadon
ta yaye bargon da Mummym ta kudundune a
ciki, tana fad'in
"Mum lafiya,?"
Cikin raunananniyar murya Mummy ta ce
"lafiya lau"
Arfat ta ce
"Amma shine Mummy ba ki fito ba tun
dazu"?
Mummy ta ce
"jikin ne yau bana Jin dadin sa, amma je ki
ga ni nan zuwa".
Jiki a sanyaye Arfat ta ce
"to mummy sai kin fito,"
tare da Jan k'ofar d'akin. Amma a can k'asan
zuciyarta tana tunanin mai ya samu Mummyn su
don ba ta saba ganinta a irin wannan yanayin
ba.
Bayan sun kammala breakfast ne Daddy ya ce
su zauna dukan su yana da magana, Mummy
kuwa da tun shigowarta, ta kasa sakewa don ko
abincin kirki bata ci ba, haka su Arfat ba su iya
tsayawa sun ci abincin ba kamar yadda suka
saba, saboda don duk sun takura ganin halin da
Mummyn su ke ciki.
Daddy ne ya yi gyaran murya ya fara magana
da cewa "Muhammad!"
Yanayin yadda ya fad'i sunan ya saka
Abeed saurin juyawa ya ce
"Na'am," wadda sautin ta bai fita ba, don ko
Arfat dake zaune kusa da shi bata san ya fad'a
ba.
Daddy ya cigaba da fad'in
"Tunda abin na ka ya zo da haka, ka riga
kasan alkawarin da na yi akan aurenka, kuma
kasan ba zan ta6a warware shi ba, don haka
muka yanke shawara ni da mahaifiyarku akan
za mu had'a aurenka kai da 'yar uwarka
Arfat,......!!!"
Tashin hankali muka gano a idanunsa k'arara,
don kuwa ba Abeed ba har Arfat ta shiga rudani,
don wata zabura ta yi, wadda ta yi dai_dai da
tashin Abeed, hakan ya haddasa gwaruwar
kawunansu, lokaci d'aya suka yi baya, kowa
dafe da kan sa.
Ita kuwa Mummy wasu zafafan hawaye ne, suka
biyo kumatunta, don tasan a rina.
Abeed ne ya yi k'arfin halin cewa
"Dad ban gane mai ka ke nufi ba?, ka
fahimtar da ni, Dad ko ka manta we are the
same blood, if am not wrong, Arfat ita ke bina
fa. sannan nan k'aramar k'anwar mu Afrat".
Arfat kuwa da gudu ta je, ta fad'a jikin Mummy
tana kuka, ta ce
"Mummy ban ga ne abinda Daddy ya ke
fad'a ba, how comes zan auri yayana, the same
Mum & Dad fa, ban ta6a ji ba, ko a lokacin
jahilan farko ba,....!!!"
Wata iriyar tsawa Daddy ya daka mata tare
da cewa
"Me kike nufi?, kin fi ni sanin abinda ya
kamata na yi ne?? "
Mummy ce ta ce
"Alhaji sanin kan ka ne, idan yaran nan suka
ji wannan maganar sai sun dimauce har su kasa
controlling kan su, don haka hak'uri za ka yi abi
komai a hankali."
Mikewa Daddy ya yi tare da nuna Abeed da
hannu ya ce
"Kai ka jawo duk abinda ya faru , don haka
ka shirya d'aukan duk abinda ya biyo baya."
Daga haka bai kuma cewa komai ba ya fice
daga parlourn. Abeed K'arasawa ya yi gurin da
Mummy ke zaune ya ce
"Mum sai yanzu zuciyata ta fara hasko
mun, abinda tun d'azu na kasa ganewa, tabbas
na fuskanci akwai wani B'OYAYYEN AL'AMIRI
(Bebeelo ) da ya shafe mu, amma ba ku sanar
da mu ba, don Allah Mummy ki fad'a mana mai
ya ke shirin faruwa da mu ne"??
Mummy kam ba ta san lokacin da ta rushe da
wani irin kuka ba, dama tun d'azu take rike shi,
gaba d'ayansu rungume Mummym suka yi, suna
rarrashinta ,, duk da Arfat da afrat suma kukan
suke yi.
Arfat ce ta d'ago da kanta ta fara magana cikin
kuka ta ce
"Mummy gaskiyar ya Abeed, don ni kaina na
fara wannan tunanin, ko ma miye Mummy
gwanda ku gaya mana, akan ku bar mu cikin
duhu."
Dakyar mummy ta samu ta tsaida kukan da take
yi, ta ce
"ku yi hak'uri 'ya'yana, za ku ji komai, tunda
har Alhaji ya taso da maganar nan, tabbas na
san zai gaya muku duk abinda ya faru, don haka
ku kara hak'uri zuwa an jima za mu k'ara wani
zaman".
Ba don ransu ya so ba suka amince, kowa ya
tashi ya nufi nasa guri zuciyoyinsu cunkushe da
tunani kala_kala........
Mum Twins 😍& Auntie M Jabo 🍃
[4/11, 2:54 PM] 💫AN YI WALK'IYA 16&17
💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Adaidai k'ofar shiga parlourn su ta tsaya don
daidaita natsuwarta, don kar a gane yanayin da
take ciki, sabida lokacin da zata fito tana ta
gwalli da iyayi, a dole ga matar Abeed, bayan
tasan tana da 'yan adawa don akwai
stepsisters d'in da suke sa'anni, kuma kowacce
ta so ace ita Abeed zai aura, amma sai Abbansu
ya ce hafsat aka ba shi, don haka tasan idan
suka san yadda ta kasance musu da Abeed lallai
za su yi mata dariya, ai kuwa tana shiga
kaitsaye d'akinsu ta wuce, ta fad'a gado sharaf,
tana tunanin mafita don gaskiya tana son Abeed,
domin tasan idan ta yi nasarar aurensa ta more
miji kuma ta tsere sa'a.
Amma da ta tuna kalamansa sai jikinta
ya yi sanyi, wannan shi ake kira ga k'oshi ga
kwanan yunwa.
********
Abeed kuwa bayan ya koma gida, wanka ya yi
sannan ya ci abinci, ya yi shirin kwanciya barci,
a sannan ne yake tariyar abinda ya faru
tsakanin sa da hafsat, tsaki ya ja, sannan ya ce
"idan ban da abun Daddy ta yaya waccen
yarinyar zata had'a kan ta da ni, ai kwata_kwats
ba aji na ba ce" ni da na fison mace natural
beauty, amma ga shi ita duk kyan na ta artificial
ne, amma haka ga ni ta ke yi ta had'u, ba ta san
ni ganinta na ke yi kamar wata horror ba," ya
kuma Jan wani tsakin, tare da rarumo pillown sa
ya k'ak'ume da niyyar fara barci, nan da nan
kuwa ya lula duniyar masu barci, mu kuma mu
ka ja masa k'ofa muka fice daga d'akin.
Kusan 6 weeks da zuwan Abeed gidansu Hafsat,
amma ko da wasa bai kuma lek'awa ba, kullum
da uzirin da ya ke bawa Mummy idan ta yi masa
maganar, har ta gaji ta saka masa ido.
Hafsat kuwa kullum sai ta kirashi, shi kuma ya
yi ta mata wulak'anci da cin fuska, daga k'arshe
ma sai ta daina samunsa, don karya sim card
d'in ya yi , ya chanza wani, don karya layi a
gurin Abeed ba wani abu ba ne, halinsa ne ya
saba haka tuntuni, da ga ya yarinya za ta
takurashi da kira zai chanza wani layin.
Hafsat tun abun baya damunta har ya fara
damunta, don har 'yar rama ta yi, ga shi ta kasa
gayawa kowa maganar har ummansu.........
Auntie M Jabo 🍃& Maman Twins💫AN YI
WALK'IYA 17&18 💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
A kwance ta ke a d'aki tana aikin na ta, na
neman mafita, kwatsam ta jiyo muryar babbar
aminiyarta, Safiyya tana kwad'a sallama, a
hanzarce ta mik'e ta rungumeta tana fad'in
k'awata yau a gari? Kamar kin san ina neman ki,
don da gobe na ke sa ran zuwa gidanku".
Murmushi Safiyya ta yi ta ce "kamar da gaske"?
Hafsat ta ce" wallahi da gaske na ke yi, domin
akwai wata muhimmiyyar magana da na ke son
gaya miki ki ba ni shawara".
Safiyya ta ce "ok, to gaya mun ina Jin ki, tunda
ga ni na zo", nan da nan Hafsat ta juyewa
Safiyya abinda ya faru tsakanin ta da Abeed, a
jiyar zuciya Safiyya ta sauke, sannan ta ce
"Hafsat shawara kike so na ba ki ko? Hafsat ta
ce eh"
Safiyya ta cigaba da fad'in "kin san ita gaskiya
d'aya ce tak, kuma d'aci ne da ita, i hope idan
na gaya miki za ki daure ki yi amfani da ita?"
Hafsat ta ce" eh insha'Allah"
Safiyya ta ce "ni a gani na ki hak'ura da Abeed
zai fi, don alamu sun nuna ba ya son ki, kuma
baya muradin zaman aure da ke, to hak'ura da
shi zai fi alkhairi, don gaba na ke jiye miki, ki
manta da duk wani buri da ki ka Sakawa
zuciyarki akan auren Abeed, ki yi watsi da
maganar, ki nemi za6in Allah kawai".
Jinjina na kai kawai Hafsat ke yi, alamum
maganar ta shigeta, ta ce "dama nima zuciya
ta, tana ta mun waswasi akan maganar, amma
tun da yanzu kin haska mun inda na kasa ga ni,
insha'Allah na janye daga yau, dama umman mu
tana ta tambayata akan maganar tana son ji
yadda mu ka yi da Abeed, ina ta mata
hanya_hanya, tunda abun ya kasance haka zan
sanarda da ita na fasa kawai, ta sanar da
Abbanmu, tunda dama ba dole aka mun ba, za6i
aka ba ni".
Safiyya ta ce "gaskiya kam, Allah ya sa hakan
ya zama alkhairi," ameen k'awar kirki Hafsat ta
fad'a tare da mika mata hannu suka tafa su na
dariya.
*****
Yau Daddy tunda ya dawo ya ke zabga fad'a,
mummy ce ta sauko tana fad'in Alhaji lafiya?
tun daga sama na ke jiyo maganar ka, mai ya
faru ne? Daddy ya ce "ni da yaron nan ne
Muhammad, d'azu Alhaji Usman ya ke gaya
mun, wai yarinyar wajensa ta janye maganar
aure tsakaninta da shi, kuma na san ba komai
ya saka ta yi hakan ba, sai dan bak'in hali da ya
ke nuna mata, tunda tun fil'azal ya nuna baya
son aurenta kawai dai tilasta shi mu ka yi".
Mummy ta ce "yi hak'uri Alhaji, bari ya zo, na
tambaye shi yanda suka yi da yarinyar,"
Cikin 6acin rai Daddy ya ce "ba na son Jin
komai daga gare shi, kawai idan ya dawo ki
sanar da shi cewa na yanke hukuncin ba zai
kuma yin wani azumi a gidannan ba, sai a gidan
aurensa, don haka ya shirya kafin azumin nan
mai zuwa za a yi aurensa , gobe_goben nan zan
sanar da shi yarinyar da zan kuma nema masa,
don haka ya yi gaggawar zuwa su shirya kansu".
Daga haka bai kuma cewa komai ba, ya wuce
fuuuu ya haye sama, Mummy kam tsayawa ta yi
baki bud'e, don tasan mutumin na ta, idan ya ce
eh, baya ta6a dawowa ya ce a'a......
Mujee zuwa
Auntie M Jabo 🍃 & Maman Twins 😍
: 💫AN YI WALK'IYA 19&20💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Abeed na dawowa, Mummy ta same shi domin
isar da sak'on Daddy, nan take ta zayyana masa
hukuncin da Daddy ya yanke akan maganar
aurensa, zare dara_daran idanunsa waje ya yi,
tare da fad'in
"Mummy kafin azumi fa kika ce ni duk kun bi
kun saka min ido ga mata nan ba'a tsangamesu
ba saini, tsakani da Allah azumin da bai fi 3
months ba, how comes zan iya aure kafin
lokacin, bayan na san ko yanzu wadda Daddy zai
nema mun ba lallai ta dace da ra'ayina ba,"
Jinjina kai Mummy ta yi tare da fad'in
"Abeed har yanzu ba ka hak'ura da
wannan mummunan k'udirin naka ba ko?, nidai
kan gani nake Ka yi hakuri ka kar6i za6in
mahaifinka ya fiye ma ka."
Abeed ya ce
"Mum ba wai na k'i bin maganar Daddy ba
ne, Noo, ki gane mana, nima fa ya kamata a
duba uzurina a yi mun adalci, don ni ba k'aramin
yaro ba ne, da za a ce bani da hankalin da zan
za6i matar da ta dace da ni, kuma ni ba mace
ba bare a mun auren dole,"
ya had'e hannayensa wuri d'aya, ya cigaba
da fad'in
"please mum ki taimaka ki gayawa Daddy ya
hak'ura da zancen auren nan yanzu, har sai na
samu irin macen da na ke son aura".
Ajiyar zuciya mummy ta sauke, sannan ta ce
"Abeed ka san halin Alhaji sarai, tun da ya
taso da maganar nan, Allah kadai zai hana a yi
aurenka a tsukun lokacin da ya fad'a , ni dai
shawarar da zan ba ka, ka daure ka amince da
abun da mahaifinka ya fad'a".
Ba don ransa ya so ba, ya ce
"to"
saboda ya fuskanci ita ma mummy ta kasa
fuskantar in da ya sa gaba.
K'ofa mummy ta nufa tana fad'in
"Ni dai sai da safe, don har na fara Jin
barci,"
Abeed ya ce.
"Allah ya tashe mu lafiya".
Tunda safe Daddy ya sa aka kira masa Abeed,
nan da nan kuwa ya hau kora masa bayani akan
yarinyar da ya kuma nema masa don sun riga
sun gama magana da mahaifin ta, ya ce
"Muhammad ai kasan Alhaji sulaiman ko"?
Gyd'a kai Abeed ya yi don kaf abokan Daddy ba
wanda bai sa ni ba, Daddy ya cigaba da cewa
"To ya baka babbar 'yar sa, sai ka je ku
daidaita kan ku, shiru Abeed ya yi na dan lokaci,
sannan ya ce "
to tare da mik'ewa ya na fad'in
"Bari na je na yi shirin zuwa office kada na
makara".
Daddy ya ce
"ya yi kyau, Allah ya taimaka", Abeed ya ce
"Ameen" tare da fitowa.
Bayan ya dawo daga office, wannan karon bai
jira Mummy ta yi masa maganar zuwa ganin
yarinyar da aka kuma ba shi ba, ya shiga shirin
zuwa, nan da nan ya fesa wankan shi, ya d'auko
wata dakakkiyar shadda grey colour ya saka, ya
murza hularsa kalar shaddar, ya sha perfumes
masu sanyin k'amshi, ya fito fes da shi, a parlor
su ka had'u da mummy ta kalleshi ta ce
"sai ina kuma"?
Murmushi ya yi wanda bai kai ciki ba, ya ce
"Mummy wurin yarinyar da kuka ba ni
mana"
murmushin Jin dad'i mummy ta yi, ta ce
"yawwa my boy, haka na ke so, Allah ya
kiyaye hanya, Allah kuma ya dawo mun da kai
lafiya,"
ya ce
"Ameen Mum," tare da ficewa daga
parlourn.
Driving ya ke yi, yana sauraren wani cool music,
amma duk da haka zuciyarsa ba ta daina masa
tuk'uk'in da ta ke yi ba, don dai ya fito zancen
nan ne don ya cimma burin da ke zucuyarsa,
lokaci d'aya kuma sai ya saki wani murmushin
Jin dadi don tuna abinda ya k'udire a zuciyarsa,
hakan ya yi dai_dai da k'arasowarsa gidan Alhaji
Sulaiman...
Auntie M Jabo🍃 & Maman Twins 😍
💫AN YI WALK'IYA 💫
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Horn ya yi mai gadi ya wangale masa gate ya
shige, wannan karon direct parlourn gidan ya
nufa, bayan ya shiga sun gaisa da mutan gidan,
aka ce ya zauna a turo masa yarinyar mai amsa
sunan Teema, gaishe shi ta yi cikin kunya da
ladabi, ba laifi shima ya d'an saki fuskarsa, don
ya ga alamun zata yi hankali, amma duk da haka
natacciyar zuciyarsa na masa hud'ubar tsiya,
don haka nan da nan ya fuske, ya hau zayyana
mata sharuddansa,ita ma ba ta tsaya wani
dogon nazari ba tace da shi dama tana da
wanda take so, don dai babanta ya zo da
maganarsa ne shi yasa ta amince, amma tunda
abun haka ne idan don ita ne ta janye akai
kasuwa, murmushin cin nasara Abeed ya yi, don
dai ya lura ba za a samu matsala ba a wurin
teema ba, don haka cikin wayo da dabara irin na
d'a namiji ya nuna mata, ta sanarda daddynta ya
yi hakuri ya janye maganar auren su, tunda tana
da wanda ta ke so, teema ta ce
"Ba damuwa idan dai Daddy na ne bai da
matsala zai fahimce ni".
Murmushi Abeed ya yi tare da mik'ewa ya ce
"To ni zan ta fi"
teema daga nan zaune ta ce
"Allah ya kiyaye hanya".
Ya ce
"Ameen"
tare da fitowa daga parlorn, cikin nishadi ya ke
driving d'in sa har ya zo gida.
A parlor ya tarar da Mummy a zaune, tana
kallon T.V, ta ce
"welcome back, yarona har ka dawo ke
nan"?
Ya ce
"Eh mummy ba ki yi barci ba ne "?
Tace
"Eh ina nan, ina jiran dawowarka ne, amma
daga ganin alamun fuskar nan ta ka an dace,"
dariya ya to tare da fad'in "i hope so", Mummy
ta ce
"Allah ya sa"
yace
"Ameen "
tare da fad'in
"Mummy bari na je na kwanta, wallahi duk a
gajiye na ke".
Mummy ta ce
"Ai ko ni tashi zan yi, don su Arfat tun d'azu
suka yi barci, nima don na tsaya jiranka ne. "
Yau ta kama asabar daga Daddy har Abeed ba
wanda ya je aiki, suna hutawa a gida, don haka
sai can wajen yamma Alhaji Sulaiman ya yi
tattaki zuwa gidan don sanarda da Daddy halin
da ake ciki game da auren Abeed da teema,
tunda ya gaya masa baya son a