da kuɗi ne dan su dama burinsu ba wai Aryaan ya aureta bane burinsu Umar da bappah su ga this side of Aryaan da kyau, amma sam Aneela ba dai a zuri’arsu ba.
Bayan fitarsu palourn shiru ya sake ɗauka, daga Aryaan har bappah babu wanda yace komai, kusan mintuna uku kafin Aryaan ya miƙe tsaye a hankali, bappah ya bishi da kallo dan a tunaninsa tafiya zaiyi amma ga mamakinsa sai ya ga ya tafi bookshelf ɗin da ke palourn dake cike da littafan addini ya ɗauko Al’ƙur’anin bappah ya dawo ya zauna yana kallon bappah yace
“I know you are disappointed in me bappah, kuma nasan you wont believe ko miye zance, amma wallahi..” ya faɗa yana raising alƙur’anin slightly
“Ban taɓa having anything with her ba, ba wai ita kaɗai ba, ive never had anything with any woman!” Shiru bappah yayi yana ta kallonsa, ganin yayi shiru ya sa ya sake faɗin
“Trust me pls” gyara zamansa bappah yayi yana jin kaso mai yawa cikin ɓacin ransa na evaporating
“Meyasa baka faɗi haka a gaban parents ɗinka ba?” Shiru yayi ya gagara amsawa, bappah ya jinjina kai yana kallonsa yace
“Toh naji! Yanzu ina so ka faɗa min da bakinka who she is, miye kuma haɗinka da ita?”
“She was my girlfriend, kuma na san na aikata kuskure da hanyar bata too much access to rayuwata, da yin abubuwa da yawa da addinina bai lamunce mini in yi da ita ba amma wallahi bappah babu zina cikinsu duka”
Studying ɗinshi kawai bappah yake yi, duk da yasan ƙarya ba halin Aryaan bane dan tun yana ƙarami he’s a very straight forward person idan yayi abu yayi ne ko yanka shi za’a yi zai ce yayi, haka idan bai yi ba ko za’a halakasa bai yi ba. Ganin bappah yayi shiru yana ta kallonsa ya sake cewa
“I’m not lying!”
“I know!..” bappah ya faɗa yana cigaba da kallonsa,
“But still ina so in san dalilinta na aikata hakan”
“Saboda nace i cant marry her”
“Why cant you marry her?” Shiru yayi, bappah ya ɗanyi guntun murmushi yace
“Tashi kaje, i know exactly me zanyi ya kawo ƙarshen komai, idan ma gaskiya kake faɗa ko akasinsa” gyaɗa masa kai yayi a hankali ya miƙe ya mayar da Qur’an ɗin ya dawo ya nufi ɗakin Daada walking slowly….
Karatun alƙur’ani ya sameta tana yi tana ganinshi ta ƙarasa ayar da take karantawa tana murmushi tace
“Muhammad”
“Na’am” ya amsa ƙasa ƙasa yana ƙarasawa dogon kujera dake ɗakin ya kwanta ya lumshe idanunsa, shiru tayi tana kallonsa kamar zata masa magana kuma ta fasa ta cigaba da karatunta a hankali, tun yana jin karatun ƙasa ƙasa har bacci ya ɗauke shi..
Ko minti goma baccin baiyi da ɗaukarsa ba muryarta ya tashe shi, Har tsakiyar kansa yake jin muryar kamar wata gyare banda surutu babu abinda takeyi, tun daga palourn Bappah har ɗakin daada ana jiyota! Kuma ya san bazai wuce ita da bappah ɗin ba dan wannan wasa na jika da kaka tafi kowa yinsa da bappah kuma shima yake biye mata.
Tashi yayi zaune a hankali ya dafe kansa da hannu biyu, Daada ta dubeshi tana rufe alƙur’anin tace
“Ta tasheka koh? Ai wannan yarinya Salwa kam sai a hankali” shiru ya mata bai ce komai ba saboda ciwon da kannasa ya fara masa, dai dai lokacin ta buɗe ƙofar ɗakin Daada, tun daga bakin ƙofa tace
“Daada am” tana shigowa cikin ɗakin ta nufi Daada, sai dai wanda ta gani a zaune dafe da kansa yasa ta ja ta tsaya sai kuma ta juya ta nufi ƙofa, Daada na mata magana ma ko juyowa batayi ba ta fice a ɗakin, ya ɗan ja guntun tsaki tare da miƙewa ya nufi ƙofa shima Daada ta bishi da kallo…
Yana fitowa palour ya tarar bata nan, bappah yace “kai ka korota hala?”
“Ita wa?” Ya tambaya a hankali yana zama a kujera,
“Zaka santa soon” shiru yayi bai ce komai ba, bappah yace
“Baka da lafiya ne?” Ya ɗan gyaɗa masa kai yana nuna masa kansa
“Sannu kaje ka sha magani ka kwanta, bari in ga ko daada na da paracetamol” ya faɗa yana miƙewa ya nufi ɗakin Daada.
Sai da ya sha maganin kafin ya wuce masallaci tare da bappah dan sallar Maghriba kafin ya wuce gida.
A hankali salwa ke haura stairs ɗin without making any sound dan bata son ko su Lailerh su san ta shigo, sannan sai da ta tabbatar Ameen ya tafi masallaci kafin ta shigo, successfully ta gama haura benen ta buɗe ƙofar ɗakin Ameen ta shige ta rufo ƙofar tare da riƙe kunkumi tana kallon ɗakin, bata ma san miye ya kawota ko miye take nema ba abinda kawai ta sani shine duk wani abu nashi mai muhimmanci yana nan, ta fara kalle kalle, ɗakin is very clean babu tarkace bare ta gane inda kayansa suke, wadrobe ta buɗe ta ƙare ma kayan ciki kallo kafin ta rufe, ta ɗan ja tsaki dan bata ga wani abu mai muhimmanci da idan ta lalata masa zai ji haushi ba.
Har ta juya zata fita idanunta ya sauƙa akan laptop ɗinsa dake gefen bed, ta san wannan ba laptop ɗin Ameen bane so definitely nasa ne, haka kawai taji this is it, ta nufi laptop ɗin da sauri ta zauna gefen bed ta janyo laptop ɗin ta buɗe tana faɗin
“Lets see what u got here” wani murmushi tayi ganin screen ɗin babu password this seems easier than she imagine.
“He’s actually stupid, wa ke barin stuffs ɗinsa without password yanzu..” ta faɗa a hankali tana gyara zamanta a kan gadon.
Tana buɗe screen ɗin taga already it was opened to his work, ta zuba ma screen ɗin idanu tana kallon kyakkyawan 3D model na zane dake kan screen ɗin da bata wani gane kansa ba, abinda kawai ta sani shine it was beautiful and massive too, ɗan matso da fuskarta tayi kusa da screen ɗin sosai tana kallo ba ƙaramin birgeta zanen yayi ba
“Whats this..” ta faɗa amused, ba wai building bane kawai, zane ne da ta gagara gane miye ne, abubuwan da ta gane a ciki kawai highways da yayi mapping, inda yayi indicating ruwa, da kuma skyscrappers, ko ma dai menene wannan ba ƙaramin abu bane, komai was engineered to perfection. a can saman screen ɗin taga an rubuta
Arewa crown development
pan african financial and cultural district
Lead architect: Aryaan Umar Turaki
Ɗan buɗa idanunta tayi tana cigaba da kallo a zuciyarta tana mamakin shi yayi duka wannan ɗin? Tanƙwashe ƙafafunta tayi ta cigaba da kallo tana clicking tana buɗe other files ɗin, babu abinda bai tsara ba, interior layouts, phase of construction, and many more.
Babu tsoron komai ta hau deleting files ɗin tana yi tana kallon ƙofa sai da ta goge su tass har waɗanda bata buɗe ba kafin ta miƙe da sauri jin taku outside door ɗin dai dai lokacin ya turo ƙofar ɗakin ya shigo….
#Banidahujja
#Maimoon
09041426598
https://whatsapp.com/channel/0029VbB1qGBFMqrVuPRZ5f2Q
🌺BANI DA HUJJAH🌺
Assalamu alaikum lovelies Bani da hujjah is a paid book, free pages kuma basu da yawa sosai, pls support me by making your payments kafin end of free pages! Thank you so much as you do, ga masu bukatar biya zasu tura 500 kacal zuwaga
7039695535
Palmpay,
Maimunatu Abdullahi muhd
Sai ku tura min evidence of payment ta 09041426598 on whatsapp
Idan kuma katin waya ne zaku tura 500 zuwa ga 07039695535
Thank you❤️
11.
Daga sama har ƙasa ya ƙare mata kallo ganin yadda tayi tsuru tsuru a tsaye, kana ganin idanunta ka ga mara gaskiya kafin ya juya ya kalli gadon inda laptop ɗinsa ke ajiye a buɗe, bai san sanda ya haɗe girar sama da ta ƙasa ba yana takawa zuwa cikin ɗakin sosai, Ameen dake biye da shi a baya shima ya ƙaraso ciki yana kallon Salwa yace
“Me kike yi anan?”
“I….i…na zo ne… ina so..” ganin Aryaan ya ɗauki laptop ɗin tayi hanyar ƙofa da gudu zata fita, shi dai Ameen bai ga sanda Aryaan ya ajiye laptop ba sai gani yayi ya cafko ta, ta fasa ihu tare da tsugunawa ƙasa tana kallonsa har ta fara hawaye
“Wallahi ban sani bane yaya…” da Sauri Ameen ya matso yana faɗin
“Sake mata hannu mana dan Allah kar ka karyata miye ta maka?” Janyota ya soma yi zai mayar da ita gaban laptop ɗin, ta lanƙwashe a ƙasa tare da taƙarƙarewa ta kurma ihu ko Mami zata ji ta ta zo ta taimaketa!
Ameen that is confused ya sake biyo sa yana faɗin
“Wai miye ta maka ne? Meyasa idan bakayi mugunta ba baka jin daɗi” ko kula Ameen baiyi ba, yana riƙe da hannunta da hannunsa ɗaya ita kuma tana tsugune a ƙasa ya buɗe laptop ɗin, he was so shocked da bai san sanda ya sake hannunta ya dafe bakinsa ba, tunda ya ga laptop ɗinsa a buɗe yasan ta taɓa kuma ganin zata gudu ya san ɓarna ta masa amma bai taɓa expecting abinda ta aikata kenan ba, project ɗinsa na wata da watanni? Idan bai halaka ta ba sai dai idan ba sunansa Aryaan ba, a zuciye ya juyo sai dai wayam har ta tattare skirt ɗinta ta gudu ta bar ɗakin, Ameen ya matso ya leƙa screen ɗin yana faɗin
“Wai miye tayi ne” kanshi da already ke ciwo yaji ya sake sara masa, idanunsa suka kaɗa lokaci ɗaya yana kallon Aryaan kamar wanda baya son yayi believing abinda ya gani yace
“She deleted Arewa crown development project” zaro idanu Ameen yayi yana kallonsa yace
“No way! you dont mean it… innalillahi” ya faɗa yana janyo laptop ɗin yana dubawa, Aryaan ya samu waje ya zauna a gefen bed ya dafe kansa, project ɗinnan bai taɓa babban project irinsa ba, his hardwork for months ta goge cikin mintuna? Wace iriyar yarinya ce Salwa?
Fuskar Ameen cike da alhini yace
“Subhanallah kuma baka da any back up” shiru yayi kawai ya gagara magana.. Ameen ya miƙe yana sake jinjina lamarin yace
“Kayi haƙuri haka Allah ya ƙaddara…” wani banzan kallo ya masa daga sama har ƙasa kafin ya miƙe yana kallon Ameen yace
“Ai wallahi idan kaga abinda ya hanani karya yarinyarnan rasuwa nayi, gobe ko tsinke aka ce mata nawa ne zata kiyaye sa..” yana gama faɗin haka ya nufi ƙofa zai fita, Ameen yayi saurin shan gabansa yana kallonsa yace
“Kar ka taɓata please yarinya ce…” bai san sanda ya hankaɗa Ameen ba yana huci yace
“Motsin gado ce ba yarinya ba, kasan girman Allah ko da kuɗi aka bata ta bi hanyar da na bi ma bazata sake bi ba..” Ameen dake ta kallonsa yace
“Akan project ɗin banza zaka taɓa lafiyarta ta?”
“Ba na banza bane, its my hardwork, wahalata ce na months, why am i even explaining it to you? Ka zauna kana son Yarinya ƙarama shiyasa duk inda raini yake ta rainaka to billahi ƙaryarta ta rainani ba sunana Al’ameen ba kuma banyi mata kama da saurayinta ba..” sororo Ameen ya tsaya yana kallonsa har ya kai ƙarshe kafin yace
“Bismillah je ka, idan ka barta da rai yau baka cika Aryaan ba, kuma sanin kanka ne ni ba soyayya nake da ita ba bare kace saboda haka ta raina ni infact respect ke tsakanina da ita more than you could imagine, to idan ma soyayyarce why is it your problem? Ko dan Albarkacin son da ka san ina mata ba zaka mini kara ka mata uzuri ba? Amma a gabana kake cewa zaka daketa?”
“Ai ka san girman Allah ko kai ne ka goge abinnan duka zan maka bare wata wacce kake so na banza da hofi…” yana faɗa ya raɓa gefensa ya fice a ɗakin Al’ameen ya bishi da kallo
Ganin yadda ta shigo cikin palourn tana ƙoƙarin haurawa sama da gudu ya sa Ammi dake shirya dining faɗin
“Zo nan..” sai da ta kalli sama ta kalli ƙofa kafin ta nufi wajen Ammi jikinta na mazari, dan daga yadda taga yayi reacting ba ƙaramin ɓarna ta aikata masa ba
“Miye haka? Meyasa zaki shigo mini gida da gudu wa ya biyo ki?” Tana yi tana kallo ƙofa tace
“Babu!”
“Bazaki faɗa mini wa ya biyo ki ba sai na kwaɗa miki cokalinnan...” Ammi ta faɗa tana dakatawa da jera abincin..
“Ammi dama yaya ne ban sani ba na…..” dai dai lokacin ya buɗe ƙofar palourn ya shigo, ta kurma ihu ta nufi sama da gudu, Ammi ta bita da kallo, amma ga mamakinta sai taga Aryaan ya bita saman, Ammi tayi saurin ajiye spoon dake hannunta tana faɗin
“Lafiyanku kam?” Ta faɗa tana nufar saman itama, a bakin ƙofar ɗakinta ta same shi salwa ta shige ta rufe da makulli, Ammi ta tsaya tana kallonsa kafin tace
“Laifi tayi hala?” Sai da ya sauƙe ajiyar zuciya kana ganinsa kasan ransa a ɓace yake kafin ya juyo ya kalli Ammi yace
“Ina wuni”
“Lafiya lau miye tayi maka?..” ta sake tambaya tana kallonsa
“Babu!” Kawai ya faɗa yana nufar stairs ta bishi da kallo har ya gama sauƙa ƙasa kafin ta nufi ƙofar salwa ta buga tace
“Zo ki buɗe mini..”
“Ammi yaya yana nan?”
“Ban sani ba ki zo ki buɗe mini nace” a hankali ta buɗe ƙofar Ammi ta tura ta shiga tana kallonta tace
“Me ya haɗaki da shi da ya biyo ki har nan?”
“Wallahi Ammi ni babu abinda na masa kawai dan na ɗan taɓa laptop ɗinsa ne shine….”
“Ƙarya kike yi akan haka ba zai biyo ki har nan ba na san halinsa, ba za dai ki raba kanki da wasan banza da mazan gidannan ba koh? Ban hanaki ba? Idan ya karyaki a banza wa yake da asara? Ki janyo babanki yayi ta jarabar da ya saba koh bayan ke kike fita kike nemo duk wani abu da ke samunki koh? Na rabaki da hamza kinki ji yanzu kuma Aryaan kike neman maganarsa? Baki san har yanzu haushin ɗaukarki da yayi nake ji ba? Da kinji maganata a lokacin kin hakura da zuwa da zai ɗauke ki ne? Yanzu uban miye ya haɗaki da laptop ɗinsa ko sa’anki ne shi da kike wasan banza da shi har yake biyoki har nan zai dokeki”
“Ammi fa…” gwaɓe mata baki Ammi tayi ta dafe bakin tare da fashewa da kuka
“Na rabaki da su wallahi in banda gaisuwa na sake ganinki da su kina wasan banza sai na ci miki mutunci mara hankali kawai” tana gamawa ta fice a ɗakin ta barta a durƙushe tana kuka..
sake leƙowa Ammi tayi tana harararta tace
“kuma wallahi ki rufa mini baki tunda ba dukanki nayi ba kar ki fusata ni in miki shegen duka dan ubanki, tunda dalilin kuka kike so ni zan baki dalilin yin kukan mai lasisi..” tana faɗa ta rufe ƙofar ta sauƙa ƙasa dan ƙarasa aikinta.
Ƙunshe kanta salwa tayi a ɗaki taƙi saukowa har sai da Daddynta ya dawo, itama Ammi ko bi ta kanta bata sake yi ba.
Uncle Ameenu bayan yayi wanka ya sauƙo dan cin abinci, har ya zauna ya kalli Ammi dake ƙoƙarin serving ɗinsa yace
“Ina princess..”
“Tana ɗaki” Ammi ta faɗa fuskarta ba yabo ba fallasa
“Why is she in her bedroom by this time? Bata da lafiya ne?”
“Lafiyarta ƙalau yallaɓai..” tura kujerar yayi baya ya miƙe ba tare da ya kuma kula Ammi ba ya nufi sama, Ammi ta bishi da kallo kawai dan ta san miye zai biyo baya…
A kwance ya sameta ta lulluɓa da bargo har kanta, ya ƙarasa ya zaune gefen gadon yana kallonta yace
“Princess” jin shiru ya sauƙe bargon kanta, gani yayi idanunta a lumshe tana bacci, tayi parking gashinta Ya kwanta lub a goshinta, shiru uncle Ameenu yayi yana kallonta kafin ya kai hannu ya taɓa goshinta jin ba zafi ya taɓa wuyanta shima ba zafi hakan ya sa ya miƙe ya nufi ƙofa, Ammi na ta jira taji ya fara faɗa dan ta tabbata kukan da ta wuni tanayi tun magribh idanunta ya kumbura amma taji shiru. Ta ɗaga kanta tana kallonsa jin takunsa har ya ƙaraso ya zauna a kujerar da ya tashi ya soma cin abincinsa, bata tambayesa ba itama kawai ta zauna ta soma cin nata, two spoons kaɗai yayi ya sake kallonta yace
“Amma taci abinci ne kafin ta kwanta..” Ammi ta girgiza kai bata ce komai ba
“Ta yaya za’a yi ki bar yarinya tayi bacci bata ci abinci ba fisabilillah? Idan ulcer ya kamata what are you going to tell me? Kina abu kamar ba ke kika haife ta ba? Haba dan Allah” ko kallonshi Ammi bata yi ba ta cigaba da cin abincinta, ya ture kujeran ya miƙe tare da goge bakinsa da tissue ya kurɓi ruwa ya wuce sama abinsa, sai da ta kalli abincin da ya bari kafin ta cigaba da cin abincinta abinta….
“Happy birthday to you! Happy birthday to you…” pausing yayi yana kallon Al’ameen, siyama da Lailerh a palourn dukansu kayan bacci ne a jikinsu sai hular birthday dake kansu da cake a hannun Siyama, shi kwata kwata ya manta ma birthday ɗinsa yau ne, ya ƙarasa saukowa ƙasa sanye da workout wears ɗinshi yana ƙaƙalo murmushi yace
“Ba zaku makaranta bane?” Lailerh ta ƙaraso tana ƙoƙarin saka masa birthday cap tace
“Bamu da early lectures dukanmu! Happy birthday Yaya” ya bari ta gama saka masa cap ɗin kafin ya ɗan bata side hug yace
“Thank you lil sis” itama siyama ajiye cake ɗin tayi ta zo gabansa tana faɗin
“Happy 30th birthday Yaya, Allah ya ƙaro shekaru masu albarka”
“Thank you” ya faɗa yana kallon Ameen da shima yace
“Happy birthday” a taƙaice ya amsa da “tnks” yana cire cap ɗin ya ajiye yace
“Ku je ku shirya ku tafi school” Mami ta fito daga kitchen tana kallonsu da murmushi a fuskarta, ƙarasawa yayi kusa da ita yace
“Good morning Mami”
“Morning, Allah ya ƙara maka shekaru masu albarka, ya ƙaro maka hankali ya baka mata ta gari cikin shekararnan”.
“Amin” ya amsa a hankali.. dai dai lokacin kuma aka turo ƙofar palourn aka shigo, duk kallonta suka kamayi, Abida ta shigo cikin palourn tana shining teeth tace
“Happy birthday yaya Aryaan, my favourite cousin” yana murmushi yace
“Thank you Abida how are you”
“I’m fyn fav” kafin ta juya ta kalli Mami tace
“Good morning”
“Morning” Mami ta amsa tana kallonta rabonta da gidan ta manta amma bata yi mamaki ba dan ba ita Mami kaɗai ba kowa ma ya san meya kawota! ‘Aryaan’
Ɗan kallon Ameen tayi tace “good morning yaya Ameen”
“Morning Abida, ya shaheeda kuna waya?”
“Eh munayi” ta faɗa tana bin bayan Aryaan da ya nufi ƙofa zai fita, duk suka bisu da kallo, Lailerh da siyama suka taɓe baki tare da nufar sama abinsu…
Jerawa Abida tayi da shi tana ta masa hira telling him how much she missed him da baya gidan, ya ɗan kalleta yace
“Ke baki da school yau ne”
“Kawai bazan je bane yaya i’m tired of this school wallahi” ya gyaɗa kai kawai bai ce mata komai ba suna cigaba da tafiya a jere, Salwa dake saman balcony ɗin gidansu sanye da kayan bacci dan tashinta kenan Ammi tace taje tayi watering flowers dake wajen sai hamma take yi, hammar ce ta katse hangosu da tayi suna tafiya a jere suna magana ta bisu da kallo tana zuba ruwa a flowers ɗin, haka kawai jininta sam bai haɗu da Abida ba, ko ga maciji basa yi ita da Abida ganinsu yanzu tare da Aryaan yasa ta ja dogon tsaki ta ajiye butan ruwan, a ƙasan ranta tana faɗin
“Birds of the same feather…” ta wuce ta buɗe slide door dake wajen zata shige cikin gidansu, dai dai lokacin ya kalli side ɗin balcony ɗinsu, bayanta kawai ya gani da gashinta da ta tufke ta shige ciki ta juyo zata rufe door ɗin suka haɗa ido, murguɗa masa baki tayi ta rufe ƙofar, yayi shiru yana kallon door ɗin da ta rufe kafin ya ɗauke idanunsa tare da gyaɗa kai kawai ya cigaba da tafiya sam baya ko jin abinda Abida ke faɗa….
Har sai da ya gama duk wani workout da zaiyi Abida na biye da shi, ji yayi kamar ya kore ta amma dai ya rabu da ita.
“Wai yaya har ka gama” ta faɗa ganin he’s heading home
“Eh” ya bata amsa a taƙaice fuskarsa a haɗe, ta bishi a baya jikinta a sanyaye ganin yanda ya amsata kamar suna faɗa.
Suna shigowa layin ya hango motar driver ɗin salwa a pake a wajen gate ɗinsu yana jiranta, ya juya ya kalli inda ya ganta ɗazu kafin ya kalli gate ɗinsu, daidai lokacin ta fito dressed beautifully ta rataya expensive tote bag hannunta riƙe da labcoat da dama shi ta manta ta shiga ɗaukowa, kallo ɗaya ta musu ta shige motar tana kallon driver ɗinta tace
“Yi sauri mu tafi kafin su yaya su iso” tada motar yayi yana amsa mata da “toh” ya ja suka wuce su, Aryaan yayi guntun smirk dan a yanzu ko lokacinta bayi da shi amma tabbass zaiyi lokacintane ta gama guje gujen…
Abida ta tsaya a bakin gate ɗin Mami tana kallonsa tace
“Zan wuce gida Yaya Aryaan”
“Okay” kawai ya faɗa yana tura gate ɗin ta bishi da kallo har ya shige kafin ta wuce abinta.
A compound ya tarar da Siyama da Lailerh musa zai kaisu makaranta suma, ya wuce su ya shige cikin gidan ba tare da ya ce musu komai ba dan gabaki ɗaya idan ya tuno project ɗinnan ji yake ransa na lalacewa.
#Banidahujja
#Maimoon
09041426598
https://whatsapp.com/channel/0029VbB1qGBFMqrVuPRZ5f2Q
🌺BANI DA HUJJAH🌺
Last free page….
Assalamu alaikum lovelies Bani da hujjah is a paid book, free pages kuma basu da yawa sosai, pls support me by making your payments kafin end of free pages! Thank you so much as you do, ga masu bukatar biya zasu tura 500 kacal zuwaga
7039695535
Palmpay,
Maimunatu Abdullahi muhd
Sai ku tura min evidence of payment ta 09041426598 on whatsapp
Idan kuma katin waya ne zaku tura 500 zuwa ga 07039695535
Thank you❤️
12.
Sai da yayi wanka kafin ya zauna ya janyo laptop ɗinsa trying to see idan zai iya recovering wani abin, ya buɗe screen ɗin ya tsaya yana kallon folder ɗin aikinsa amma empty ba komai a ciki, ɗaya bayan ɗaya ya duba files ɗin duka empty ya lumshe idanunsa a hankali tare da jingina kansa da headboard sai da yayi taking deep breath kafin ya buɗe idanunsa ya maida su kan laptop ɗinsa ya fara danne danne, duba recycle bin da recently deleted yayi yaga duk ta goge a wajen, ya shiga duba system files da temporary folders amma duk babu wani abu mai anfani a wajajen, at that moment ya sake tabbatar da cewa its gone! Wayarsa ya janyo a hankali ya buɗe ya fara scrolling bai san sanda ya sauƙe gajeren ajiyar zuciya ba, duk da ba wai duka komai ne yake kan wayartasa ba but atleast wasu abubuwan na nan ɗin, hotuna, screenshots da folders da ya tura wayarsa weeks ago ba dan yana saka ran zai yi anfani da su ba yanzu gashi sune zasu yi saving life ɗinsa..
Ya shiga zooming yana bin detail ɗin komai da ke jiki da kallo kamar mai haddacewa, thank God yana da structural note a wayarsa still shima zai taimaka duk da theyre still not enough amma theyll go a long way.
Ajiye wayar yayi ya koma kan laptop ɗin ya buɗe sabon file ya fara sabon aiki afresh, ya san ba lallai ya gama before date ɗin presenting ba which is next week! Amma duk da haka he’ll try his luck sannan zai demanding for extention of submission ɗin idan Allah ya taimakesa he’ll make it.
Wuni yayi aikin, sau ɗaya ya sauƙa yaci abinci shima Mami ce ta zo har ɗaki ta matsa masa ya zo yaci abinci, ciwon da kansa yake masa ya ƙaru sosai dole ya ajiye laptop ɗin around four dan zuwa Sallahn la’asar, a palour ya tarar da Ameen da ya dawo aiki ya baje a palour yana gisting Ammi akan law firm