Share this page
6 / 7
burmemiyar rigar me botira agaba,yau kam Amo harda guga tamata,ta fesa turare se tafiya take tana ɗage kafaɗa,hannunta riƙeda kuɗi da wani ƙaramin bakko zata kasuwar ƴan kaba, yau komai na kayan miya basu dashi,waken soyar ta ma ya ƙare shine aka ɗau na agwagwa za'a tafi kasuwa siyyya. Gitfa wasu ƴan mata tayi,suka kalleta suka kwashe da dariya, ɗaya tace wa sauran "Allah na tuba,yanzu wannan wai mace ce amma duk ta lalata jikinta da tafiyar maza,ita adole namiji ce", ɗayar ma tace "waifa soja take kiran kanta"hhhhhh suka kuma sheqewa da dariya,ta ukun kuwa tace nide birgeni take wlh,ga kyau,wannan idan zata nutsu wallahi mace ce me zati da diri" ta farkon ta kuma cewa ke dilla cen matsa,ina wani kyau anan wacce kullum take wuni cuɗanya da maza,mtwsss" ta biyun ma ta kuma cewa "kyau iya kyau amma na banza ba mashinshini,ni wnn anya ma akwai nonon arziki aƙirjinta kuwa?" Ta fada tana kama haɓa, wata dariyar suka kuma sheqewa da ita suna tafawa. Juyowa kande tayi afusace ta nufosu tana wani irin huci,tsayawa sukayi dan ganin me zata musu ita kaɗai sukuma har rai uku,tana zuwa ba wata2 ta haɗa kansu guri ɗaya dukansu,da wacce ke tsakiya da waɗanda ke gefe da gefe ta haɗe musu kai ji kake gub,agigice ta tsakiyar ta yanka ihu ta kwasa aguje kamar ta gigice, sauran biyun kuma suka tsugunna ko wacce tana dafe kanta dan sun gumu ba lefi, kallonsu tayi a sheqe ta nuna ɗayar tace "kikace ko akwai nonuwa akirji na ko?, to maza miƙe ko laluba kiji" tafaɗa tana finciko hannun budurwar wacce ta fasa ƙara tana bawa kande hakuri,fadi take "dan Allah dan Annabi kiyi hkr wlh Sherin sheɗan ne,dan Allah kiyi hkr,ni wlh bazan kuma shiga harkarki ba dan Allah kiyi hkr ",kande kuwa ta rike hannun budurwar chaf tace aifa seta taba kirjin taji ko akwai nono. Seda budurwa nan tagalabaita saboda kuka,fuskarta duk tayi kace2 da kuka sannan ta saketa dan ɗayar tuni itama ta cikawa bujenta iska,tace "arniya ƙaramar ƴar iska kawai" ta juya ta tafi gun aikenta. Tana tafiya tana tuna yadda ƴan matan nan suka rikice musamman wacce ta ruga aguje kamar ta gigice se murmushi take ita kaɗai,abin ya bata nishadi,shafar ƙirjinta tayi wanda take mance ma wai akwai wata halitta agurin, rintse ido tayi jin ta taɓa wasu halittu masu matuqar laushi,madedeta dan sunfi ƙarfin hannunta,amma yanayin yadda jikinta yake bata da faɗi ta sama se ta ƙugu ga yacce take tafiya a ƙobare hakan yasa bakowa ne ze iya gane yanayin cikar halittarta ba,uwa uba kuma shigarta,amma duk wannan abin bisa tilastawar inna yasa take saka half vest acikin burma burman kayan nata,wnn ma yaƙara temakawa gurin ɓoye cikar ƙirjin nata,wanda idan ba ido kasanya mata ba ma sam bazakace tanada su ba. Hura hanci tayi ta daki ƙirjin nata tace "munafukan abubuwa arnaye me zanyi daku ma,ni dama baku fito ba yasin,bakkuda wani use agun soja" ta wani cuno baki gaba,tana sake yin doro da bayanta irin karma akuma lura akwai su agurin. Sam kande ita a yanzu halittar mata akanta bata birgeta,zata iya rantse wa tana mantawa ita mace ce se idan tazo kama ruwa ko yin wanka,dan tunda Allah ya sa ta girma ta cika mace bata taɓa yin jinin al'ada ba,shekarunta ashirin da ɗaya,zata iya rantse wa ma tamanta mata suna wani abu wai al'ada,dan idan inna tana al'ada ƙaryar mutum yagane,ko lokacin sallah ya yi seta waske,mlm habu ne kaɗai ze iya sanin tana cikin halin rashin tsarki,hakan ya ƙara sanya wa kande ta manta da wata aba wai al'ada,balle a yanzu da inna ta dena yi kwata2. A dede wani lungu wanda ze sada kande da kasuwa taga wani me baro a kwance aƙasa yanata sheqa amai,jikinsa banda rawa ba abinda yake,da sauri kande ta matsa kusa dashi tace "subhanallahi sannu mlm, bakada lfy ne?" Be iya ce mata komi ba, ya jingine da bangon gurin yana mayar da numfashi,jikinsa se rawa yake idonsa ya yi ja sosai,daganinsa yanajin jiki,ga barronsa a gefe,da sauri ta tashi taje gaban bore hole ɗin dake kusada su ta ɗebo ruwa a wani bucket data gani agurin ta kawo masa tana masa sannu,ya amsa ya wanke fuskarsa ya zuba akan sa,duk ya bata tausayi,a ranta tace oo Allah neman halak da wuya,kalli wannan babban mutum dashi amma yana na barrow,ko lafiya bashida ita amma ya fito neman halalinsa,* kande mutum ce me tsananin tausayi,ita kanta batasan tana da tausayi ba,wani abin ma bata sanin tanayi. Gdy mutumin ya mata ya miƙe bayan yaɗanji karfin jikin sa,yaja barrow dinsa harya fara tafiya Jiri ya ɗebesa yafaɗi agurin a sume,da gudu ta tashi ta ruga ta isa inda yake a kwance ta na irin kiran bawan Allah,wasu masu barrow ta hango a tsallaken titi ta tallafo kansa tana bubbuga kumatunsa tana kiran bawan Allah bude idonka amma baya cikin hayyacinsa, tashi tayi ta ruga tsallaken ta kira masu barrow nan tace ga wani ɗan uwansu cen ya faɗi ya suma kamar ma bashida lfy ne,da sauri kuwa suka biyota zuwa inda yake kwance aƙasa a sheme,suna zuwa suka gansa da sauri ɗaya ya tsare musu napep suka kamashi daƙyar suka sanya aciki,dake sunada yawa se mutum uku suka shiga napep ɗin biyu abaya suka rikeshi se ɗaya ya shiga kusada direba suka tafi asibiti,sauran kuma suka zauna suka ajiye wa wanda suka tafi asibiti barrow ɗinsu,kande tana tsaye tana kallonsu har suka ƙulewa ganinta,jiki a sanyaye ta tashi ta shiga kasuwa tayi siyayyarta ta juyo hanyar gida,har lokacin fuskar mutumin nan me barrow bata bar idonta ba,duk tausayinsa dama talakawa ya rufe ta,ita de tasan su bamasu kuɗi bane,amma sunada wadatar da abinda zasuci daa na bukatar yau da kullum be gagaresu ba,harma wani kan iya jingina dasu shima ya wadata. Tana tafiya tana tunanin halin tsadar rayuwa da yadda talaka kullum yake shan wahala,kamar ance ta ɗaga kai kawai idonta ya faɗa cikin na mahaukacin ta data sanya wa suna kirezi. Ta daɗe bata ganinsa,kusan sati biyu rabon da ta gansa,amma da kullum yana biye da ita duk inda zata to seta gansa agurin, ta danganta hakan da kila dan tana bashi abinci ne,se kuma a ka ɗauki sati biyu bata gansa ba se yau. Suna hada ido aikuwa ya sinne kai kamar ya yi rashin gaskiya,tsallaka titi tayi tashareshi ta nufi hanyar gida,kamar yadda tayi tsammani kuwa yana bayanta yana binta a hankali,amma suna da nisa da juna,wata kwana tashiga,ta ɓoye ta ɓace masa,ai kuwa aguje ya rugo ya biyo kwanar shima yana dube dube alamar ita yake nema. Be ganta ba kawai ya kwaɓe fuska ya ɓata rai ya juya ze wuce kawai ya ganta a bayansa tace masa "woooooo" ,kamar ba mahaukaci ba seda ya firgita dan babu zato ya ganta akusa dashi,dariya ta fara ƙyaƙyata wa ganin yadda kirezi ya firgita se zare fararen idonsa yake,a sace ya saki murmushi shima se kuma ya kwaɓe fuska ya sauke kai alamar fushi yake,dariya take seda tayi me isarta yatsare ta da manyan idanuwansa yanata kallonta,baƙaramin kyau tayi ba yadda take sheqa dariyar,1 side dimple dinta kamar a zuba abu aciki ya zauna tsabar yadda ya loɓa, kallonta yake sosai ya shagala,ji yake kamar ya shafa kyakkyawar fuskarta,gashi ta ta sharɓa basilin ga hasken rana yana haske fuskarta se wani walƙiya take kamar wacce take amfani da glowing products. Gimtsewa tayi tace "hi kirezius Ina ka shige ne?,2 sleep I no see u,were u go, eh" na sha ma ƴan uwanku ne suka kwalfeka,ashe de har yanzu kana nan a layi kana gararamba". Ko mi be ce mata ba se sunkuyarda kai da yayi,kama hanya tayi tace "kai kirezi yau banda ko asi kawai ka ware nima nayi nan",ta kama hanyar gida,kirezi kuwa yau duk inda kande ta saka ƙafa shima seya saka,tayi2 ya tafi yaƙi,duk inda ta wuce se an kauce ganinta da mahaukaci,ko ita kaɗai ba me tarar hanyarta balle yau an ganta da mahaukaci,har gida ya bita,a ƙofar gida Ikilima ta fito taci kwalliya da alama fita zatayi,se yauƙi take tana wani gyatsine,tayi kyau abinta itama fara ce kyakkawa,yanzu ta gare shiga shirgin kande tauda de taga ba riba,koda yaushe idan ta haɗo su itace take shan wuya,kuma ba wani mataki da ake ɗauka shiyasa tayiwa kanta karatun ta nutsu. Ai tana hango kande da wani rusheshen mahaukaci ta tsallara ihu aguje ta koma cikin gida tana ihu,malam dake zaure da dalibansa da sauri suka fito waje dan ganin abinda ya tsorita Ikilima haka,ai kwa darewa suka farayi suma ganin kande da wani ƙaton mahaukaci. Tsayawa tayi tana cewa "kirezi tsaya anan barin gani ko inna ta gama tuwo,kuma kana cinyewa ka kama gabanka tom", kamar me hankali yako tsugunna agurin,mlm habu yana tsaye yana kallon ikon Allah. Juyowa tayi zata shiga gida taga mlm da ɗalibansa sunyi cirko2 suna kallonta. Sallamar ɗaliban mlm ya yi bisa dole,kafin ya janyo hannun kande yashiga da ita cikin gida,ɗaki ya kaita ya nemi guri ya zauna ya ƙura mata ido,kallonta yake sosai itama kallonsa take cikin ido,kallonta mlm yake yana karanta wasu addu'o'i itama kallonsa take ido cikin ido,sosai mlm yake addu'o'in nan,idonta ne yafara tara jini nan take idonta yakoma kamar an zuba nuna mata jini,saurin rintse ido tayi gumi na karyo mata ta ko'ina. Cikin buɗaɗɗiyar murya ta fara magana hankali kwance,tace.... # 🌹kANDE🌹 (_The tomboy_) Paid book. Na.*SADIKA IBRAHIM.* *MOMSANI* *Marubuciyar*: # saurayin yayata free # sirikara free And now # kANDE paid. Not edited Free page:11 Bismillahirrah manirrahim. Cikin buɗaɗɗiyar murya ta fara magana hankali kwance,tace "malam Abubakar bin Hamza,meyasa ka kasance me gaggawa ne a wasu lokuta? Tabbas kai ɗin cikakken ɗan Adam ne, gaggawar ka ta kuma tabbatar mana da hakan,idan baka mantaba abaya shekaru sha ɗaya da suka shuɗe mun taɓa faɗa maka akwai sirri dunƙulalle a tattare da goɗiya,to a yanzu sirrikan sun fara bayyana tabbas wannan mahaukacin ba mahaukaci bane, cikakken mutum ne me hankali,kuma ba ƙaramin mutum bane,sannan ta dalilinsa ƙofar sirri zata buɗe,mun baka gajeren haske,sauran kuma kaine da kanka zaka nemo,tabbas kai ɗin ubane na gari,kuma kaso abinda bakada alaqa kota kusa bare nesa,tabbas zakaga sakamako,mahaukaci sunansa A'ZAM(ma'anar sunan the greatest),ka tunkaresa kai tsaye kuma ka nuna masa kasan yanada hankali,tabbas zakasan duk wani abu da kake da buƙatar sani,dukkan wani sirri ze bayyana,amma ko ka sani lokacin bayyanar sirrin wa goɗiyar beyi ba,kai kaɗai kake da damar sanin wannan sirrin,.. malam Abubakar bin Hamza tabbas zakaga sakamakon alherin ka,ka bar damuwa da yanayin rayuwar goɗiya,tunda kayi hkr na tsawon shekaru to haƙiƙa ribar ka akusa take,komi ya kusa zuwa ƙarshe,sannan sirrin cikin gidan nan ma ya kusa bayyana,duk ka zuba ido zakayi kallo kuma zakayi mamaki,abinda ka sani da wanda baka sani ba duka zasu fito fili,Ni zan tafiiii,kuma zan dawo kamar de yadda aka saba". Hamma me tsayi kande ta yi kafin ta lumshe idonta a hankali kuma ta kwanto a jikin mlm, maida hannunsa ya yi ya rungumeta idonsa na zubar da hawaye masu zafi,tabbas shi yasani dole wata rana abinda yake gudu ze faru,amma be ɗauka abin a kusa yake ba,ji yake kamar bayason wannan ɓoyayyen sirrin ya bayyana,inama wannan abin da suka binne ze iya zama sirrin da har abada baze bayyana ba,inama inama,amma ba yadda ya iya,shi yasani dole ne abinda yake gudu seya faru,yasani wata rana dole hakan zata kasance. Kallon kyakkyawar fuskar ƴar tasa ya yi wacce ta jiƙe sharkaf da gumi,jikinta duk ya saki,juyowa ya yi ya kalli inna wacce ta takure se sharbar kuka take,tunda aljanin kande ya fara magana ta shigo ɗakin,dan ta zaga ne sanda mlm ya shigo hannunsa riƙe da kande, fitowar ta ne ta gansu acikin yanayin da kande bata hayyacinta. Itama taji duk abinda kande ta faɗa ko ace iskanta ya faɗa. Shimfiɗera mlm ya yi,seda ta kai kusan magrib tana bacci kafin ta tashi a gajiye, jikinta duk ya mutu,akasalance ta kalli inna da Amo wanda suke zaune akan ta hannun Amo da carbi,se ja take tana zare ido,duk a tsorace take,kamar ace kyat ta fece aguje. Inna kuma hannunta riƙe da wayarta keypad ta kunna kira'a sun ajiye a gefe. Da sauri kande ta tashi zaune,tace subhanallahi inna karfe nawa ne,kallon juna inna da Amo sukayi kafin inna tace "karfe Shida da hamsin ne auta, ya akayi ne?,me za'a kawo miki kici?", saurin miƙewa tayi tana faɗin "innalillahi,inna garin yaya nayi bacci me yawa haka kuma baki tashe ni ba,wlh wani mahaukaci ne yaketa bina, kullum duk inda naje seya bini,ko dan ina bashi abin ci ne,yau ma har gida ya biyoni,nace zan duba ko kin gama abinci in bashi,ashe kwanciya nai, kai innalillahi,Allah sarki kirezi kilama ya tafi" tayi maganar a shagwaɓe kuma sak muryarta tun tana yarinyar ta kafin ta haɗu da lalurar iska. Kallon Amo inna tayi,itama haka,duk da cewa Amo bataji me kande ta ce ba sbd kunnenta,amma yadda kanden ta kwaɓe fuska cike da shagwaba yabata mamaki,balle inna da ta ji abinda tace da kuma yanayin yadda muryarta ta fita,cikin ɗan murna wacce ta fara kama inna tare da tunanin ko addu'ar su ce ta karɓu ta ce "mahaukaci kuma auta a ina kika samo sa ke kuwa?" Kamar an mintsineta tace "Allah wlh kuwa inna,wani kirezius ne ya mini ta kaska,duk inda na dire legediz dita seya ɗora tasa agun,bansan shi bafa, amma ya nanemin,duk inda naje yana biye,shine yau ya biyo ni harnan da alama tsumagiya ce ta fyaɗosa,dan be taba biyoni har gidaba se yau," ta dubi inna wacce jikinta ya yi sanyi murnar ta ta koma ciki ganin yadda ta kuma komawa kanden ta me kamar maza,ta kuma cewa "ya ake ciki ne tuffar dagus akwai tuwon ne na ɗan sanmasa ya lomata shima?,kila ma ya tafi yaganni shiru kamar an aiki bawa garinsu, Allah sarki kirezius" ta fada tana sakkowa daga kan gadon. Acen waje kuwa bayan mlm ya fita,da sauri ya leqa waje dan tabbatar da abinda aljanin kande yace,wayam ba kirezi ba alamarsa, jinjina kai Malam ya yi,tabbas wannan mahaukacin akwai ayar tmby akansa,amma tunda yake bibiyar yarinyar sa yasan dole da manufa,kuma dole ze dawo,yanzu dole shima yasaka ido sosai akan ƴarsa. * Niger state minna* _mariga way_ Tafiya suke amotar sunata mayarda zance akan yadda sace sacen mutane yazama ruwan dare,kawai se a ɗauke mutane ayi daji dasu kamar dabbobi,wasun su suna ganin lefin gwaunati ɗari bisa ɗari kan taɓarɓarewar tsaro,ga tsadar rayuwa kullum rayuwa daɗa ƙunci take,kullum talaka shine a wahala amma dan ɓacewar basira da rashin lissafi da talakan de za'ayi amfani asakasu su yaƙi junansu,su kashe junansu,hallau acikinsu ne ake samun waɗanda sunfi ma masu garkuwa da mutanen bala'i wato informants. Wasu suka suna ganin kawai mafiya aksarin kidnappers son zuciya da dogon buri ne yake sanya su faɗawa cikin harkar,sunyi nisa sunata tattaunawa akan matsalolin rayuwa,ba zato sukaji direbansu yaja wani wawan birki yana salatin duk da yazo bakinsa, faɗi yake "yau munshiga uku tamu ta ƙare kowa yayi ta kansa,se a sannan kowa ya lura da abinda ke faruwa agurin. Motoci ne iya ganine hange,duk an fitar da mutane an tarasu aguri ɗaya kamar shanaye,wasu mutane ne sun rufe fuskar su da baƙin abu,jikinsu sanyeda kayan sojoji,mashinansu kusan guda hamsin fake agefe daya,wasu mahaukatan bindigogi ne ahannun su,se fitar da mutane suke daga cikin motocinsu suna tattara su gefe ɗaya,cikin sanɗa direban wannan motar ta saulale ya fice daga motar yabar fasinjoji sunata sallallami,direban nan yana sanɗa acikin ciyayi yanason ya samu ya gudu,ba zato yaji bindiga akansa an ɗana masa ana cemasa ya miƙe ko a harbesa. Cikin tsananin firgita ya miƙe tsaye yana haɗa me bindigar da Allah karya kashe shi,wlh yanada iyalai da marayu wanda suka dogara da shi,kaɗashi akayi tare da sauran fasinjojin da ya kwaso har inda aka tara mutanen da aka fara kamawa,yana juyowa idonsa akan wanda ya sanya masa bindiga,cikin tsananin mamaki yaga ɗaya daga cikin Mutane da ya ɗakko ne, wanda dashi akayi ta zancen ƴan garkuwa da mutane,ashe shima ɗaya daga cikin su ne. Kusan duk motocin da aka kama acikin fasinjojin akwai kidnapper aciki,sune suka Sanar da ƴan uwansu nakan hanya cewar motoci sun taso da yawa,kasancewar ranar cin kasuwar mariga ne,har sukayi nasarar kame mutane da yawan gaske,mafiya yawancinsu ƴan kasuwa ne,wasu da kayan da zasu kai don cin kasuwar,wasu kuma da uwar kuɗaɗe ajikinsu don zuwa cin kasuwa,amma cikin hukuncin Ubangiji duk anyi garkuwa da su. Seda ƴan bindigan nan suka haɗa mutane masu yawan gaske,kafin suka kaɗasu zuwa daji,bayan sun amshe musu kuɗaɗe da kayan abinci,haka suka tasa ƙeyar jama'a da dama. Ga tafiya ba karama ba,wasu a hanya sukayi ta suma,wasu harbinsu akayi saboda sunyi yunkurin guduwa. Seda sukayi tafiya me nisan gaske wacce ta shafe awoyi da yawan gaske kafin su isa wani ƙaramin gari inda ƴan bindigan sukeda zama,haka aka dinga amsar numbobin iyalan bayin Allahn nan ana kiran su ana sanar musu anyi garkuwa da ƴan uwansu,duk wanda akayi cinikin sa haka za'a waresa gefe,haka suka dinga cinikin mutane kamar dabbobi. Wadanda ba a samu cikakken bayani agurin ƴan uwansu ba,da waɗanda sukace su basu da kowa suma aka waresu gefe,su nasu hukuncin na daban ne,mafiya yawansu saida sassan jikin su ake,wasu kuma kashesu ake,wasu kuma se ajuyar da tunaninsu suma su koma ƴan bindiga. ******* _United Arab Emirates _ DUBAI. _Durah jungle _ Dubai special force vanguard. Wasu manya manyan sojoji ne da hukumar soja ta dubai suka ware waɗanda ake baiwa horo na musamman,a wuri na musamman,durah jungle wani sansanin soja ne dake nesa da garin sosai,su waɗannan sojojin bakowane lokaci ake fita dasu aiki ba,duk wani aiki me mugun haɗari shine aikinsu,kamar shiga ƙungiyoyin manya manyan daba irinsu, ISIS, mafias,ko kuma manyan sindicates wanda suka gagari duniya,irin wannan aikin ake tura su domin kawo ƙarshensa,chief commanda RAYYAN RAHMAN,shine tsaye yana kallon yadda atisayen ke wakana, tabbas lokacin da yake jira ya kusa ƙaratowa,shi da wasu zaƙaƙwuran sojoji irinsa wanda suka wahala kuma suka bautawa ƙasar su,sune suka fitar da wannan reshen na sojojin sirri tare da goyon bayan shuwagabannin kasar na ƙwarai. Ofishin sa ya koma ya fara fitar da list na sunayen waɗanda za'a tura domin zama ɗaya daga cikin ƙungiyoyin dabar da sune a jadawalin su a yanzu,su waɗannan ƙungiyoyin sun gagari duniya ta fannoni daban daban,a kuma ƙasashe mabanbanta,acikin ƙasashen da za'a tura waɗan nan sojojin akwai Dubai ɗin kanta se phillipines,China,south Africa, Russia,Ghana da kuma linjeriya kasarmu ta gado🤣. _Nigeria,Kano state_ *Sannu kaji mamuda, jiki ya yi kyau ai alhamdulillah,kaida muka kawoka ranga ranga kamar zaka sheqa, baka fa san waye akanka ba,Allah sarki wata yarinya ce me shigar maza shigar ta ta gwanin ban dariya,ita ce tazo tace mana ga wani me baro cen ya faɗi,shine fa muka rankayo aguje ashe kaine,ai yarinyar nan ta temaka wlh,da wata ce guduwa zatayi taga mutum a kwance kamar bashi da rai,uhum kaide mamuda Allah ya kara afuwa,wai nace mamuda bakada ƴan uwa ne,ni har yau kwananka biyu amma banga kowa yazo da sunan dubiya ba da ga fanni ka?" "Wlh jabir kacika ɗan banzan surutu,haba mutum yana kwance bashida lfy amma ka sanya shi agaba se famar ratattako batu kake babu birki,sekace an buɗe dam din ruwa,haba dan Allaha" "Kaiko lurwanu daɗi na da kai kenan ka cika saka ido da yanƙwana mutum,haba kalli fa yadda ƴan matan cen suka kakkallo ni, se wani faɗa kake min acikin jama'a dan na tambayi mamuda ƴan uwansa,naga ai gsky na faɗa,tunda muka kwaso shi ranga ranga muka kawosa nan bawani daga nasa da sukazo da sunan duba jikinsa,kuma dan na tambaya shike nan nayi lefi haba du Allah du Annabi lurwanu". Se cecekuce samarin suke a tsakaninsu,wanda aka kira da mamuda kuwa yana kishingiɗe akan gadon marasa lafiya ya lumshe idonsa,ƙala be ce musu ba amma duk abinda suke fada yana saurare,har suka gama faɗan nasu kuma suka koma fira. ..... Moscow, Russia.... Wani irin gidane cable front acen cikin wani guri wanda ya yi nesa da cikin garin Moscow ɗin,kusada wani madedecin tafki,wasu manyan security ne suke shawagi agurin,duka ƙofofin gidan masu password da thumbprint ne,wasu manyan motocine kusan guda goma sha ɗaya suka parker a waje gidan,biyar agaba biyar abaya,se wata golden lemo a tsakiya,kusan atare ƙofofin motocin suka buɗe banda ta tsakiyan wacce ta kasance lemo. Kusan mintuna asirin kafin aka buɗe daya daga cikin ƙofofin lemo din,wani ingarman namijine ya fito daga cikin motar,jikinsa sanyeda wasu simple Pakistan wear farare tas,se wani madedecin makawuya daya naɗa akan hular kansa wacce take baƙa, ƙafarsa sanye cikin takalma sau ciki baƙake,hannunsa sanyeda wani danƙareren agogo me matuƙar tsada,fararen yatsunsa sanyeda wani zobe baƙi me fuskar zaki,ya riƙe wata sanda kamar da gold me shegen kyau se walwali take,saurin buɗe masa lema akayi saboda snow ɗin da ke sauka agurin. Fuskar mutumin kadai idan ka kalla seka kuma kallo,mutum ne majiyi ƙarfi, ingarman namiji ne sosai,fatarsa har wani yello take,fuskarsa cike da beard me ɗaukar idon me kallo,yanada kyau me suna kyau*wild king Rolex*kenan,tafiya ya fara cikeda izza irinta maza majiya ƙarfi,duk inda ya gifta se securityn wurin sun rungume hannunsu ɗaya a ƙirji tare da sunkuyarda kansu. Yana zuwa gaban main entrance na shiga gida kofar tayi scanning na idonsa,bakinsa ɗauke da fito ya danna kansa cikin falon wanda ya ɗauki ɗumi me daɗi da ƙamshi,wata matace zaune fara me dogon gashi ta juya baya,hannunta ɗauke da wata ƙatuwar mage fara me kyau. Takawa yake yana nufar inda take zaune,bakinsa yana fito,yana isa inda take gaban wasu duwatsu masu ci da wuta irin room heater ɗin nan na jikin bango amma wannan wasu irin duwatsu ne masu kyau da sheqi kamar normal dutse suna fitar da zafi de ɗumama daki. Hannu yasa yana shafar dogon gashinta me kala biyu baƙi da roɗi roɗi kamar fari kamar milk,ko gezau bata motsa ba,ya cigaba da shafar sumarta har zuwa dogon wuyanta,hannu yasa ya juyo da kanta da ƙarfi ya juyo da fuskarta...ba zato wayar ɗauko rahoto ta faɗi saboda ganin fuskar matar nan.. Jama'a kande ce faaaaa, a Moscow😱😱😱 End of free pages kuma book 1. ************************* Shin menene ainahin asalin kande? Wanene wannan mighty wild king Rolex din? Wanene chief commander RAYYAN RAHMAN? Wani lokaci yake jira? Wanene mamuda me barrow wanda ke kwance a asibiti? Wanene general Asim? Wanene mahaukaci kirezi? Wai ma suwanene mlm habu da inna? Wani sirri suka sani akan kande,wanda aljanin kanta yake yawan nanatawa? Meye alaqaar da aljani yace akwai tsakanin kande da kirezi? Wani mission ne RAYYAN RAHMAN ze tura special force ɗinsa? *Duka wannan amsoshin suna dunƙule acikin littafin kande kashi na biyu wato book 2.* # love # hate # crime # black money # soccery # betrayal # illegal trafficking # smuggling # comedy # romance # momsani✍️ _Ina masoyan MOMSANI ina wanda suka daɗe suna jiran wnn zazzafar tafiyar ta labarin kANDE,zaa kanwar maza,zaa soja,zaa kAND,to albishirinku yaude Allah ya nufa kuma yakawomu acikin wnn daddaɗan labarin me suna kANDE,bakijiba ne nace kANDE zaa tomboy_ _shin dake akayi daddaɗar tafiyar nan ta labarin Asma'u da Muhammad Mahii ,SAURAYIN YAYATA,kin karanta labarin SIRIKATA,ko a'a,to albishirinku yauma momsani tasake dawo muku da wani daddaɗan labarin me dogon zango wato kANDE THE TOMBOY,in Sha Allah hajiyata bazakiyi nadamar karanta wnn labarinba_ _zazzafar tafiyace me ɗauke da zazzafan darasi,tare da nishadi,haɗi da ban tausayi,tattareda zazzafar soyayya,gamida cin amana dakuma butulci,bazan cika baki ba,bakuma zan cikaku da surutu ba,amma in Sha Allah karki bari ayi wannan mysterious journey din batare dakeba_ *kANDE littafin kuɗi ne akan farashi me sauki, Naira ₦400 kacal,idan kin shirya ki tura kudinki fa wnn asusun0591819457 SADIKA IBRAHIM gt bank,seku tura shedar biya ta wnn layin 07088282153,se na jiku masoya,i promise u will never regret* Masoya ƴan amana Sena jiku,mom sani tana jiran ganin kauna daga gareku,love you all😘 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note

Chapter 6 of 7