fara barinmu rik'e waya ba musamman Na yaji kai ka bani"Ashe baki da wayau Baby karki sake ko da wasa wani ya ganta bare har ma asan ni nasai maki nima nasai maki ita ne badan komai ba saidan nadinga jin muryarki koda na koma Wajen aiki amma kinsan nima banason Abunda zai dinga Zame maki matsala a gida ni zan wuce yanzu sai gobe Idan na leko" .
Thnks yaya insha Allah ba Wanda zai ganta ta fad'a cikin murna tukwana ta dauki sayayyar da sukayi tayi cikin gida sai murna take wai yau itace da waya wayarma y'ar yayi Koda tashiga tayi sa a ba kowa Sai inna Nan ta bawa inna Sayayyar da Arman yayi mata tukwana tayi ciki Sai tsallen murna take nan take ta jona ta chaji saida ta cika tukwana ta bud'e tana budeta taga ya turo mata 10gb cikin zumudi ta shiga Ta dinga d'akko apps har su what's app da Instagrams su tiktok saida ta d'auko a ranar ta fara setting d'in komai a Daren ranar ma saida suka kusan raba dare suna shan hira da Arman Saida yaga ta fara jin bacci tukwana yayi mata saida safe .
Washegari tunda safe Bayan tayi Sallar asuba harta koma saiga kiranshi saida ya tambaya lafiyarta Daga nan bata koma ba da d'auko numbobin class mates d'inta Wanda take dasu a Littafi duk ta Kwafe ta bud'e what's App duk tayi musu sallama zumudin wayar ya hanata komawa bacci ta shiga nan ta shiga Chan sai wajen 12 ta fito Bayan tayi wanka ta saka Riga marar nauyi gaishe da Inna taje tayi tukwana ta wuce bangarensu.
A Babban palour ta tarar da Abba ta duk'ursa ta gaishe da shi ya amsa mata cikin sakin fuska taa cewa "lafiya qalau Mamana ya exams din yau bakuyi ko?" Alhmdllh Abba sai gobe zamu fara neco din "Masha Allah Allah taimaka ku dage kinji Allah muku Albarka" Cikin jin dad'in Addu'ar Abba ta amsa da Ameen tukwana ta wuce cikin bedroom d'in Mamy ta gaisheta tare da yi mata ya jiki ta amsa da sauki.
"Mamy ba abunda za a miki bakya buk'atar komai? Eh Aira ba abunda nake buk'ata mai aiki tagama komai Saidai zan aikeki gidan Maman Zarah kawar tau nan dake d'orayi kingane gidan ko?Eh Mamy na gane ta Ai muna zuwa tare " yawwa to Chan zaki da kinje kice Nina aikoki ta baki sak'on ki kawomun ki gaisheta "Sannan ta zaro dubu d'aya a Jakarta tace " gashi kihau napep "to Mamy saina dawo ta fad'a saida taje ta d'auko doguwar Hijab d'inta har k'asa tukwana ta tafi.
Ta na zuwa bata jima sosai ba ta amsowa Mamy sak'on ta fito ta na tsaye ta na jiran mai napep wata dalleliyar mota ta faka a gabanta Gaba tayi mai motar ya bita yana mata magiya Dan girman Allah ta tsaya ta saurareshi jin ya had'ata da girman Allah ya sanyata ta tsaya saida ta k'are mai kallo ta ganshi baida laifi dogone baki cike da magiya ya ce " ki shigo na rage maki hanya bai kamata mace kyakyawa kamarki rana na gallarta ba.
"Yi tayi kamar bada ita yakeba " Saida ta yi ta had'ata da Allah tukwana ta shiga Dan ta lura zatasha wahalar samun abun hawa nan tayi mai kwatancen Inda zai kaita har kofar gida ya kaita ta fito ta ce Nagode "Me kyau baki bani number ki kuma ba?Kamar ta shakeshi Dan Haushi ta ce.
" Bani da waya"Ta juya kenan ta Hango Motar Arman yayi tsaye jikin mota Rungume da hannayensu ya na kallonta "Cikinta ne ya duri ruwa Dan idan bata mance ba yaya Arman ya jima da mata kashedin akan karta yarda ta kula samari ko ya ganta da wani Wanda hartayi mashi alkawarin bazata kula kowa ba gashi idan ma tayi mashi bayanin rage mata hanya kawai yayi ba fahimtar ta xaiyiba .
Taku Biyu Arman yayi kamar wani Zaki haka ya nufosu Fuskarnan tashi murtuke kamar bai tab'a Dariya ba ita kanta saida ta tsorata da ganinshi haka wani irin kallo ya watsa mata tare da data mata tsawa ya ce wuce ciki" A firgice ta wuce hada gudunta Dan sosai ta tsorata da yanayinshi "Arman ko kallon saurayin yayi ya ce.............✍🏿
*Share fisabilillah *
*_Miss Hajo ce_*🤙🏿
[5/28, 21:04] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏
Hot love story♥️🔐
```MALLAKAR```
*Hajara L Sadeq*
📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚
بسم الله الر حمن الر حين
*BOOK ONE*📔
🅿️...............11&12
....." Malam wa ya baka izinin d'aukar yarinyar Chan a mota?cikin gaskiyarshi saurayin ya ce "Kayi hakuri na ganta ne a hanya ta rasa abun hawa shine na rage mata hanya kuma sonta nake ba son yaudara ba so na Aure Dan tunda na ganta Naji ta tafi da imani na " Wani irin wawan kallo ARMAN ya gallamai ji yake kamar ya shakeshi ta maza kawai yayi ya ce "Matar Aure ce Dan haka karka k'ara bibiyarta ko kaji a ranka kana sonta Wata alaka ta k'ara shiga tsakaninku zan kulleka hope ka gane ya na gama fad'ar haka ya juya ya shige ciki shiko saurayin sosai yayi mamakin jin cewar Matar Aure ce har yana murna yayi Babban kamu cike da jin haushi ya juya.
Aira ko ta na shiga Bangaren inna ta yi sai rarraba idanu take kamar wata marar Gaskiya Daga Amma sai inna a palourn Amma nayiwa Inna Karin karatu tsaye tayi jikin Bango ta kasa ko motsawa ta na haka ARMAN ya shigo daga ganinshi.kasan ranshi yayi mugun b'aci kanta yayi gadan gadan kafin ta juya ya chafkota Cikin zafin nama ya murde mata kunne k'ara ta saki Dan taji zafi sosai Karanta ta jawo da hankalinsu Amma cike da masifa ya ce " Uban waye wancen d'in Wanda ya saukeki a mota "Cikin kuka Aira ta ce " Yaya nima bansanshiba Dan Allah kayi hakuri Bazan sakeba ka sakarmun kunne da zafi"
"ke harkinyi girman da zakishiga motar wani k'ato ko ?ina alkawarinmu dake daman idan bana nan irin abunda kike ko?k'ara fashewa tayi da kuka ta ce "a a yaya wlh yau dinma tsautsayine" Sakin murdewar yayi tare da wurgata ta durkushe ta fasa kuka mai tab'a zuciya har cikin ranshi yake jin kukan nata ganin irin kukan da take ya sanyashi sanyaya zuciyarshi dan ba abunda ya tsana sama da kukan Aira Shima durkusawar yayi cikin kwantar da murya ya ruko hannunta ya ce "Sorry " Bama ta saurareshi ba saici gaba da kukanta da tayi murza hannayenta ya fara ya ce "Sorry my cutie bazan sakeba kema karki sake kinji kinsan banason ganinki da kowani d'a namiji shiyasa na kasa control d'in zcyta please karki sake in baso kike zuciyata ta tarwatse ba " Rungumeshi tayi cikin kuka ta ce "Bazan sake ba yaya kayi hakuri " Shafa bayanta yafara nan ya fara Lallashinta kamar ba shine ya gama zafutartaba.
Inna ko da Amma suna nan suna kallon Ikon Allah "Murmushin jin dad'i inna ta yi ta ce " Allah nagode maka Tabbas mafarkina ya kusa zama Gaskiya Allah cikamun burina na ganin Auren Hajara da Muhajid Tabbas nasan ta silar hakan ne kad'ai za a iya samun sulhu tsakanin iyayensu.
Da misalin k'arfe 10 na dare Aira sanye take cikin kayan bacci Nan ta d'auko wayarta ta ta boye cikin locker ta fiddota ta bud'e data nan tayi ta ganin message d'in mutane na shigowa frnds d'inta na mata congrats Number yaya Arman da tayi save da "My yaya ta shiga taga rabonshi da online one.week kenan Hakanan kawai tayi mai slm Dan daman ya fad'a mata shi chat bai dameshiba gwarama Twitter yana shiga yaga labarai.
Amma ce ta shigo d'akin Aira bata lura ba maza tayi zata boye wayar da sosai ta tsorata Ta ce " Amma Me kikazo yi"Cikin in ina take maganar murmushi kawai amma tayi ta zauna ta ce "hmm Aira kenan ni bantaba tunanin akwai abunda zaki iya b'oye munba Kinsan tun muna yara bama boyewa junanmu komai kuma muna rik'ewa junanmu sirrikanmu to me yasa kwanannan kike neman chanzamun kinsan dai ko mutum muka kashe bamaiji" Ajiyar zuciya Aira ta sauke tasan hakane tun suna yara basa b'oyewa junansu komai a hankali ta ce "Sorry sis "ya wuce amma ta ce sannan ta Amsa wayar hannun Aira ta ce " Wow Sis 13 ce fa "Dariya Aira tayi ta ce " Kina mamaki ne "Sannan taje ta rufo kofar Dan kar Wanda ya shigo " Amma ta ce wa ya baki 13 Aira "yaya Arman ta bata amsa kai tsare dare da dawowa ta zauna" Arman "Amma ta fada sannan ta ce "Kai amma Allah yiwa Yaya Arman albarka Gaskiya Yaya ARMAN ba k'aramun sonki yake ba Aira" wara idanu Aira tayi ta ce "So fa kikace sis" So kuwa sis Arman ya jima da fara sonki fahimta ce kawai bakiyiba amma Arman ba k'aramun so yake maki ba ko ince kuke yiwa junanku.
"kamo hannunta Aira ta yi ta ce " sis kina nufin yaya Arman sona yake"kwarai kuwa Ke wace irice Aira da baki gane so ,baki ganin kishinki b'arob'aro a idanunshi Abunda ya faru dazu ma Kad'ai ya isa ya k'ara tabbatar maki da irin son da Arman yake maki Bayan nan ma alamomin soyayyarki da yake gwada maki a fili suke ba a boye ba Aira ko k'aramun yaro zai iya fahimtar soyayyar dake tsakaninku ni a zato na kinjima da ganewa kiyi tunani ki gani".
Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da lulawa duniyar tunani tun daga rayuwarsu ta baya har zuwa yanzu ,me yasa a cikin gidan ita kadai yake sakewa,me yasa ita kadai yake farantawa,ita kadai ya damu da ita,ita kadai yake kishinta ita kadai da dama Tabbas sai yanzu ta gane Yaya Arman sonta yake sosai gabanta ya fad'i kallon Amma tayi tace "To sis ni kuma ina sonshi? Ta k'arasa fad'a cikin sigar shagwaba Dariya Amma tayi sosai ta ce .
" ke sis wlh baki rabo da abun Dariya ni zaki tambaya ai zuciyarki zaki tambaya"Turo baki tayi ta ce "To fad'amun menene alamomin so?Alamomin so suna da yawa Aira Amma zanfada maki Kad'an daga cikinsu saiki duba kiga idan kina daga cikinsu " Shak'uwa tayi yawa tana daga cikin Alamun so,damuwa da halin da dayan ku yake ciki "Damuwa da rashinshi a kusa dake koda kuwa na y'an dak'ik'a ne,kishi,shine babbar alamar Zurmiya a cikin soyayya,kyautatawa,ko da yaushe idan kika kalleshi kiji farinciki ya mamaye zuciyarki koda kuwa a waya Ne,jin bazaki iya rabuwa dashi ba duk rintsi duk wuya " ga sunan da yawa Aira kiyi tunani.
Shiru tayi tare da Zurmiyawa duniyar tunani Tabbas inko hakane so ta jima da afkawa kogin soyayyar yaya Arman soyayyarma ba ta wasaba cike da damuwa ta ce "Tabbas sis najima da Fara son yaya Arman koma Ince da soyayyarshi na ginu tun bansan kaina ba nakejin Duka abubuwan nan da kika lissafo game dashi ina tsananin sonshi son ma bana wasa ba a da haukana na d'auka duk wannan din shakuwa ce saida kika lissafo nagane Abunda ake nufi da so da Chan shirmen banza na kawai nake sannan ta kamo hannun ta tace.
" Sis ya zanyi help me please ina sonshi sosai ya zanyi kin tabbata shima yana sona"Cike da tausayin y'ar uwar tata ta ce "Karki damu sis son da yake maki ya linka son da kike mashi Wanda na gani a idanuna kedai kawai ki bari har zuwa lokacin da zai furta miki" Hakika indai kika samu Yaya Arman sis kingama samun wani jin dad'i a duniya Dan nasan zaiyi wuya a samu Wanda zai kula dake ya nuna maki tsantsar k'auna da soyayya Bayan yaya Arman Dan Arman mutum ne da kowace mace ta sameshi ta more ,Abu d'aya kawai nake Tsoro kuma nake jiye muku Iyayenmu na tabbata Abba Da Daddy bazasu tab'a yarda Kuyi Aure ba inba wani ikon na ubangiji ba shine Babban abunda yake tsoratani"Hawaye sosai Aira take ta ce "Ina sonshi sis Bazan yarda a rabamu dashi ba Abba bazai iya rabamu ba Inajin da sonshi aka halicceni a yanzu bana jin tsoro ko shakkun komai da zan tunkara indai akan a rabamu da yaya Arman ne na gwammace Ranar na mutu".
ta fad'a tana fashewa da kuka " Sosai Amma ta tausayawa y'ar uwar tata Rungumeta tayi ta ce "Insha Allahu sis babu mai rabaku sai mutuwa nan tayi ta Lallashinta ranar daki daya suka kwana Wanda Aira baccci kauracewa idanunta yayi sakat tunanin Arman ya hanata bacci da kalaman y'ar uwarta Tabbas tasan indai hakane so to baiyi mata kamun wasa ba yayi mata kamun da ita kanta bazata iya control d'in zuciyarta ba sai Bayan asuba bacci ya d'auketa hakan yasa washegari tayi ranar bacci sai 12 ta tashi.
©©©©©©©©©©©©©
B'angaren Arman Shima hakan ta kasance Dan Sosai yakejin son Aira a ranshi Wanda shi kanshi bazai iya kwatanta shi da komai ba Sosai yakejin Haushi idan ya tuno ganinta da yayi da wani a tsaye tunani yake akan ya fito ya furtawa Aira abunda ke ranshi koko ?zata amince dani ko akasin haka? Ta na sona kamar yanda nake sonta ko har yanzu Kallon yaya takemun?Daren ranar bacci kauracewa Idanunshi yayi Yasan son Da yakewa Aira daga Allah ne Dan koda bai shiga zuciyar zukatan masoya ba yaji yanda sukejiba ya tabbata son da yake yiwa Airanshi babu wani mahaluk'in masoyin da zai iya yiwa masoyiyarshi kalarshi ba.
Washegari jiki ba kwari ya tashi koda mumy ta tambayeshi lafiyanshi qlau kawai yace mata nan take fad'a mashi Daddynshi jirginsu ya taso tun d'azu sun kusa isowa sai sannan ya d'anji sanyi sanyi a ranshi Dan sosai yakeson ganin Daddy Mummy tace yaje ya shirya nan da 30 minutes zai k'arasa.
Arman da kanshi shida Mummy suka taryo Daddy daga Airport Hannun Daddy rik'e da na Arman Dan ko Wanda bai saniba yasan irin tsananin son da Daddy ke yiwa Arman kasancewarshi shi d'aya tilon d'anshi a duniya.
Bayan Daddy ya huta yaci abinci Mummy sai Nan nan take da mijin nata Kallon Arman yayi ya ce "Son ya London d'in Fatan ka dawo lafiya" Lfyqlau Daddy "Masha Allah yaushe kuma zaka koma wajen Aikin naka" ran Monday sukace Daddy nama zata zasu d'an bani Hutu tunda kaga su suka turani London d'in nadawo na zata sunbani ko hutun 2weeks ne amma jiya sun kirani suke ceman Monday suke Son na koma"Dafa kanshi Dady yayi ya ce "Toh nan kusa kenan Kaga yau muna Friday to Allah ya kaimu Monday din Ai nasan d'ana jarumine Shiyasa basason suyi missing d'in aikishi ".
Murmushi Arman yayi Dan sosai yakejin dad'in yanda Daddy kullum ke kod'ashi shi d'anshi jarumine jajirtaccene tun yana yaro haka yake cemashi shi jarumine Ranar Yini sukayi suna Hira da Daddy Dan ko gidan Inna bai lek'a ba Yau cikin hirar ne yake cewa "Daddy Inna na ta nemanka" murmushi yayi ya ce "Insha Allahu gobe idan na huta zanje na gaisheta.
Washegari Daddy da Arman su kaje ya gaishe da Inna shida Security d'inshi Wanda koda yaushe suna biye dashi Arman bai samu ganin Aira ba dan Inna tace mai suna makaranta kasancewar da safe sukaje daga Chan suka wuce asibitoci Dan duba marassa lafiya sannan yayi musu alheri sosai wannan na Daga cikin abunda yasa mutanen jahar suke tsananin sonshi da son mulkinshi danshi mutum ne mai kirki da kuma tausayi ga Gaskiya da rukon amana.
Ran Sunday da dare Arman ya je gidan Inna Dan bankwana da Airanshi koda ya fad'a mata zai koma wajen Aiki kuka ta sanya mashi ita batason yake nesa da ita dak'yal ya lallab'ata yace zasu dinga Video call kullum kuma suna waya duk saiyaji bayason ma Tafiyar Dan dai ya zama dole Amma shi Zama da Airan shi ya fiye da mashi komai.
Tunda Arman ya tafi kullum cikin waya suke da video call kamar ma suna tare Aira suncigaba da Jarabawarsu ta neco ita da Amma sosai suka maida hankalinsu ga karatunsu har yanzu babu Wanda yasan da wayar Aira a cikin gidan Bayan Amma koda yaushe son Arman Kara ninkuwa yake a cikin Zuciyarta.
Ranar da Arman ya cika sati Biyu da tafiya Ranar Su Aira suka gama neco d'insu sai farinciki suke suda class mate d'insu ana tashan hotuna a wayar Aira nan Duk wasu suka amshi numbobinta ranar ji suke kamar karsu rabu daga karshe suka sha kuka musamman Aira ita da frnds d'inta Khady bestynta sosai suka shaku koda yaushe a school tare suke yawo nan sukayiwa juna Alk'awarin ziyartar juna akai akai Sai wajejen 6 suka gama hotuna da bankwana suka fito Bakin gate domin tafiya gida Suna fitowa Wata wulfefiyar Mota Fara me masifar kyau Aira ta gani parke .
Ganin mai fitowar ne ya sanyata wara idanu sosai yayi cikin sky blue din shadda ta tasha Aiki hular kanshi hadaddiya wadda a k'alla zata kai 100k Rungume yake da hannayenshi da suke sanye da Wrist din zinare kara wara idanu tayi Dan tabbatarwa da shi d'inne koko Gizau ne shiko kafeta yayi da idanu murmushi kawai yake sakar mata sosai tayi mashi kyau cikin unifoam dinta Light blue Hijab da Dark blue din wando y'ar k'aramar hijab dinta tare da rafar rigarta da ta sauko har gwuiya anyi mata hular hijab d'in da yadin wandon jelar rigarma haka ji yake Kamar ya je ya rungumota Aira ganin da gaske shi d'inne de gabanta ai batasan lokacin da ta saki Hannun Khady ba ta ruga a guje tayi wajenshi tare da Rungumeshi tama mance ta tsiraran mutanen class d'insu dake wajen Cike da murna da farincikin ganinshi ta ce My yaya........✍🏿
*Share fisabilillah*
*_Miss Hajo ce*_🤙🏿
[5/30, 23:01] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏
Hot love story♥️🔐
```MALLAKAR```
*Hajara L Sadeq*
📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚
بسم الله الر حمن الر حين
*BOOK ONE*📔
🅿️...............13&14
Cikin zazzak'ar muryarshi Mai cike da kassala a hankali ya ce "My Cutie baki girma har yanzu ko kin manta gaban mutane muke kike rungumeni " ya fada kamar bashi yayi maganar ba murmushi tayi tare da sakinshi ta ce "Sorry yaya murnar ganin kace ta sa na ma manta da mutane a gurin" Aike gimbiyace bakya laifi my cutie "Uhm My yaya ammafa Gaskiya kayi surprise Dina da yawa bantab'a tunanin zaka zoba" Ranar graduation d'in Cutie na guda ace banzoba ai Abu baiyi dad'iba yanzu dai ki shigo mu tafi gida ma ida maganar a hanya ko"to my yaya bari naje nakira Amma Tana barin wajen ya zagaya ya shiga mota.
Aira na komawa khady tayi mata Dariya tace “ummm kwt har anfara love kenan kice mu fara shiri kece bikin farko a mate “harara ta galla mata tace “sa’idinawa kawai yaya nane to sannan tace muntafi sai mun had’e online “tukwana sukayi hug din juna suka rabu Amma na baya Aira na gaba haka suka tafi a hanya sai satar kallonta yake harsuka isa ba mai cewa uffan sunzo daidai bakin gate din inna sukaga fitowar motar Abba ta gate d’in gidansu cikin faduwar gaba Aira tayi k’asa da kanta dan kar Abba yaganta abunda bata saniba tuni yaganta saida taga wucewarsu tukwana ta dago tana sauke ajiyar zuciya Shidai Arman girgiza kai kawai nan ya gyara parking a waje Amma ta fita tare da cewa thnks Aira zata bude motar taji kulle juyowa tayi ta kalleshi saita sakar mai murmushi shima ya mayar mata tare da cewa.
“Ina kika saka wayarki jiya nayi ta kira a kashe”uhm yaya wlh wayarce kasan boyeta nake bana yawo da ita ko tsakar gida dan kar wani yagani shiyasa tana locker d’ita tun jiya sai da zamu sch nadaukota dan muyi hotuna “.
“Ajiyar zuciya ya sauke ya ce “nazata ba lafiya shiyasa na taho saida nazo nan nake tambayar haidar a bangaren inna yacemun kuna sch yau kuke last paper “wayyo yaya wai saboda baka sameni ba a waya kawai ka taho i’m sorry “ta fad’a ta na langabar da kai”Shitttt Kin manta bakya laifi komai kikayi daidaine my cutie “sannan ya dauko wata karamar waya daga cikin kwali tana gani ya daga ya saka wani sabon sim card tukwana ya bude ta yace “amshi wannan karamace saikidinga yawo da ita yanda duk sanda na kira zan sameki “murmushin jin dadi tayi tace Thnks my yaya”banson godiyarnan fa daman kinsan yau kuke graduation shine baki sanar daniba “uhm yaya na manta shiyasa “Allah bada sa a Ya fitar da sakamako me kyau kawai yace sannan yace “zan wuce dear baki bukatar komai”Eh yaya bana bukatar komai ganinka ma ya wayadas Bazaka shiga ku gaisa da inna ba “dazu mungaisa ai zanje na hutane kafin gobe na wuce “kamar zatai kuka tace “yaya gobe kuma yayi kusa ai”Zandawo soon yanzun akwai aikin da na baro shiyasa I am sorry gobe idan ba jirgin Safe zanhau ba zanbiyo muyi bankwana idan kuma na samu na safe na wuce kawai “hawaye ne suka fara zubar mata tace “shikenan yaya Allah ya kiyaye ya tsaremun kai “handkerchief ya d’auko ya fara share mata hawayen ya ce “Idan nazo kinamun kuka idan zan koma zandaina yawan zuwa dan bakisan yanda nakejin kukanki a cikin zuciyata ba “cikin sauri ta had’iye kukanta da take shirin cashews’
“sorry yaya bazan sakeba banson kana nesa dani ne shiyasa idan ka tafi yaushe zaka dawo “shima ji yake kamar yayi kukan yace “nafi kowa bukatarki a kusa dani dan bayanda zanyine next week insha Allah zanshigo na kwana biyu “to my yaya Allah ya maidoka lafiya “ki kulamun da kanki kinji my cutie “murmushi tayi tace “kaima ka kulamun da kanka sun dan taba hira kadan tukwana yayi mata bankwana ya wuce ji suke kamar karsu rabu da juna.
Aira koda ta shiga gida bata iske kowaba sai Ummy da Haidar da amma da suka dawo tare “Ya Ummy ina y’an gidan naga ba kowa bangaren inna ma bata nan”ta fad’a tana Waige waige “Suntafi kai Mamy asibiti “wara idanu tayi tace “Asibiti kuma me ya sameta “Haihuwa zatai “langabar dakai tai tace “wayyo Allah sauketa lafiya ranar bangarensu ta kwana sai addua take Allah sauke mamy lafiya dakyal bacci b’arawo yayi awon gaba da ita.
************
Arman kai tsaye guest house dinshi ya wuce dan yasan ya biya ta gida Mummy saisunji dalilin da yazo to yace musu saboda Aira ko me hakan yasa ya wuce chan bayan yayi wanka t-shirt kawai ya sanya da gajeran wando fresh milk kad’ai yasha tukwana yabi lafiyar gado dan akwai gajiya sosai tattare dashi yau jinshi yake cikin farinciki saboda ya hadu da Airanshi lumshe ido yayi a hankali ya ce “I love her so much Cox she’s beautiful “tunowa lokacin da yaganta cikin unifoam yake kyakkyawar fuskarta kawai yake ta hangowa da yanda take sakar mai murmushinta mai narkar da zuciya tuno lokacin da ta rungumeshi yayi ji yayi tsikar jikinshi ta tashi kamar wanda aka tsunkula haka ya zabura rumtse idonshi yayi sosai kafin ya bude su mikewa yayi ya dauko wani hotonta sosai tayi kyau cikin Wata black laffaya daga gani hoton bai jima ba kafe hoton yayi da idanu bako kiftawa kafin ya fara shafa hoton yana murmushi shi kad’ai yace “I love you my Aira ina sonki sosai Airata ki soni please ko kadan ne yafada yana marairaicewa (🤣nikam nace Arman karfa ka haukace)rungume hoton yayi a haka baccci me dad’i ya daukeshi cike da mafarkin Airanshi.
*********
Washegari Su Aira su na bacci Ummy ta tashesu cikin murna tace ku tashi yanzu mama ta kira Mamy ta haihu “Aira kamar an tsikareta haka ta tashi tace “da gaske Ya Ummy me ta Haifa”nima ban tambaya ba yanzu dai Mama ta kira tace da asuba ta haihu mu gyara gidan tare da Laure(yar aikin su)ba jimawa zasu dawo.
Cikin murna Aira ta tashi da dinga murna nan suka gyara gidan wajejen 12 su Mamy suka dawo gida inna dauke da jaririn mamy ko duk tayi lakwas Aira sai murna take ganin k’anin nata shima fari me kyau dan duka d’iyan Mamy su ukkun fararene Haidar ne ma baiyo hasken mamy sosai ba nan yan barka da yan uwa suka fara shigowa.
Aira ko bayan flowers ta koma