L Sadeq*
๐ *JARUMAI WRITERโS ASSOCIATION * ๐
ุจุณู
ุงููู ุงูุฑ ุญู
ู ุงูุฑ ุญูู
*BOOK ONE*๐
๐
ฟ๏ธ...............23&24
Aira jinta tayi cikin Wata duniyar ta daban kafin tayi ihu ya k'ara kifeta da wani marin da yafi na d'azu k'ara ta fasa cikin gigicewa Abba ko ranshi yayi kololuwar b'aci Wayar dutsin guga ya ciro Tare da wullata kanta ya bugi da Bango Nan ya hau lafta mata ta ko ina ihu take tana neman d'auki Abba ko baimasan tanayiba Dukanta kawai yake kamar baitab'a saninta ba.
Duka mutanen dake d'akin saida suka tausaya mata Dan ko jakki aka yiwa dukan nan Yagamu da azaba dukda haushin Aira da Mamy keji Amma saida ta tausaya mata Cikin kuka taje ta rik'e Abba ta ce "Dan Allah kayi hakuri Abbansu Karka kasheta" .
Bankad'eta Abba yayi Kad'an Ya hana ta fad'i cike da masifa ya ce "Ai gwara ta mutu Da ta d'auko mun magana mutuwar ta ta fiyemun rayuwarta " Cigaba da laftarta yayi Aira ko suma ce kawai batayi ba Inna ma Tana kuka ta taso ta dinga ba Abba hakuri ya kyaleta Baimasan ta nayi ba.
Dak'yal dai Mama Halima ta rik'e Hannun Abba ta ce "Dan Girman Allah Yaya ka rabu da ita wlh ta daku karka mata illa nasan bata kyauta ba da ciwo amma kayi hakuri ka zauna " Dak'yal ta samu Abba ya zauna yana huci Aira ko Wajen Aunty Aysha ta ruga da gudu ta Rungumeta ta na kuka itama Rungumeta Ayshar tayi tana kuka Dan Duk wani mai imani saiya tausayawa Aira irin bugun da Tasha.
Cikin tsawa Abba ya ce "Munafuka K'aramar karuwa Har kinyi girman da zakibi namiji kuje ku kwana waje ni zaki tozarta ki kunyata a idon al'umma ni da daraja da kimata da komai "Abba ya fad'a yana nuna kanshi" Aira ko sosai Kalmar k'aramar karuwar tayi mata ciwo Kara fashewa tayi da kuka magana ma ba kasa Mamy ma kanta saida Kalmar Tayi mata ciwo "Fad'a sosai Abba ya shigayi Inda ya shiga ba ta nan yake fita ba yana cewa .
" Duk cikin y'ay'ana ban haifi y'ar iskaba tun daga kan Yayyunki saike y'ar karshe_Karshe Zaki gagareni ki bani matsala Tun yaushe na rabaki da d'an iskan yaron nan baki rabu dashi ba Abu har yayi k'amari kun Fara kwanan hotel hotel k'aramar yarinya dake ni zaki daukowa magana to baku isa ba Dagake har shi har ubanshi nafi k'arfinku wlh idan kuma da kene aka had'u aga bayana to ta Allah ba takuba kinja kin fita daga raina harna Fara tantamar ma Anya Nina Haifeki kuwa".
Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Mama Da Mama Halima suka fad'a a tare Mama ta ce "Haba Alhaji wannan wace irin magana ce Kai da ranka ya b'aci baka iya control d'in bakinka wannan Maganar Ba Abun yi bace " Mama Halima kuka ta sa ta ce "Haba Yaya Wannan wace irin rayuwace kaida d'an uwanka Amma kun zama kamar Annabi da kafiri kawai kun biyewa shaid'an yayi tasiri a cikin zuciyar ku Wlh saboda ku yasa ko garin nan Banason zuwa kun Riga kun b'ata mana zumunci Kun b'ata zumuncin y'ay'anmu ".
Mamy ko Itama kukan take sosai Maganar Abba ta k'ona mata rai cike da b'acin rai Ta tashi ta sab'i d'anta ta ce "Idan ba kai bane ubanta saika fad'i uban nata kokuma da ita nazo daga gidanmu Abun kuma ya tashi daga kanta ya koma kaina sharrima Ake neman K'ullamun kenan saikaje asibiti a Auna jininka da nata idan ba y'arka bace saika nemi ubanta ka maida mai"
sannan ta kalli Aira tace " Ke kuma hankalinki ya kwanta saiki zubda ruwa a k'asa kisha kinja Anyimun wulakanci burinki yau ya cika"Ta k'arasa fad'a cikin kuka tare da barin Palourn.duk saida sukaji ba dad'i musamman Aira da ta k'arawa kukanta Volume inna ko tsaki taja ta ce โmunafuka duk ba kece silar komai ba โ.
Abba baiko kula mamy ba saima ya tashi ya ce zanje wajen ubanshi na Mashi warning Rikeshi Mama Halima tayi ta ce Dan Allah kayi kayi hakuri kar kaje Bari a kirashi yaya Kabir d'in yazo a sasinta tunda haka kakeso wannan Maganar Ba ta waje ba ce tukwana ya zauna yana huci.
Aunty Halima ta kira Abbansu Arman Bayan sun gaisa ta ce "Yaya Dan Allah kazo gidan Inna yanzu tana son ganinka da Sauri" Subhanalla innarce ba lfy ko wa cewar Daddy"Lafiya qalu yaya kaidai kawai kazo "To gani nan yanzunnan" Cikin Sauri Daddy Ya taho Dan a tunaninshi Inna ce ba lafiya Kafin minti Ashirin Ya Iso gidan.
Suna zazzaune Kamar y'an zaman makoki Daddy Ya shigo Security d'inshi Ya umarta su tsaya a waje Har PA d'inshi Yana shigowa ganin Inna ya sauke ajiyar zuciya ya ce "Ai nama zaci Inna ce ba lfy hankali na harya tashi" .
Lafiya qlau Yaya ka zauna "Bayan Daddy Ya zauna Mama Halima na kuka ta ce " Yaya Dan Allah Dan Girma Allah ku taimakemu ko ba Dan mu ba Dan Allah Kuyi hakuri ku janye wannan gabar Dake tsakaninku da tashin hankalin nan kamar Ba y'an uwa ba karku manta yaya ciki d'aya ba wasa ba ne Wlh kullum Da Bakin cikin wannan abun nake kwana nake tashi Ku taimakemu ku fahimci Juna na tabbata hatta ran iyayenmu dake k'asa basajin dad'in abun nan na tabbatar da suna raye da bazaku mana haka ba ".
Abba ne Ya tashi cikin fad'a ya ce "Daman Halima dalilin da yasa kika kirashi kenan to babu wani saurin shiri tsakani na da mutumin nan Sannan ya kalli Daddy Ya nunashi da yatsa ya ce .
" Kashe ne zan maka Akan Lalataccen d'anka Jiya ya d'aukar mun y'a sun kwana waje Dan haka kajawa Dan iskan d'anka kunne ya rabu da y'ata na rabasu sunk'i rabuwa nan gaba na k'ara ganinshi da ita Zan d'auki mummunan matakin da kowa saiya koka Dan wlh ka sake d'anka ya lalatamun tarbiyar y'a ko yayi mata ciki Kotu ce Zata rabani dakai".
Cikin b'acin rai Shima Daddy Ya tashi cikin masifa ya ce "Daman saboda wannan dalilin ne kuka kirani sannan Shima ya nunashi da yatsa ya ce " Karka k'ara kiran d'ana da lalatacce y'arka ce lalatatta tunda har ka kasa bata tarbiyar da har ta bishi ta kwana Sannan kai zakayiwa y'arka kashe ba ni ba Idan ka isa da ita Kai zaka rabata dashi ba ni ba bazan rabasu d'inba Kuma da kake maganar abun Kunya ,y'a mace ke abun Kunya ba d'a namiji ba Dan haka idan ma yayi mata cikin kai da y'arka kukayi abun Kunya ba ni da d'ana ba Hope ka gane "
Yana gama Fad'ar Hakan Fuuu yayi waje Duka Wanda ke Palourn Babu Wanda bai koka ba Musamman Mama Halima da take ganin tazo kiran gyara gashi an k'ara b'arna Shima Abba cikin b'acin rai da k'unar rai ya tashi ya fice daga palourn Tabbas yau Aira ta Ja Amfad'a mashi magana masu ciwo Aira ko Sosai take kuka ita kam ta shiga Ukkunta ya zatayi da rayuwarta da gudu tayi d'aki ta haye Gado ta na kuka mai tab'a zuciya.
Yinin ranar Kowa sukuku ya yishi Haka dai akayi soye Rai duk babu dad'i musamman Mamy da zata iya cewa ranta yafi na kowa b'aci Aira ko ranar yinin D'aki tayi ko abinci bata iya ciba Tasha kukanta Har ta gode Allah ga shaftun bulalun Abba da suke mata mugun rad'ad'i.
Daddy ko cikin b'acin rai ya nufi gida yana zuwa Ya d'auke Arman da Mari Arman da jin Marin kawai yayi a sama dafe kumcinshi yayi ya tsaya yana kallon Daddy karo na farko kenan a tsawon Rayuwarshi da Daddy Ya tab'a daga hannu ya dakeshi cikin fad'a Daddy Ya ce.
"Ubanme yasa ka d'aukar musu y'a ina ka kaita har kuka kwana Waje Kaja yau an fad'amun maganganu masu zafi a saboda kai To daga yau bakai ba y'arsu na Rabaka da ita indai nine mahaifinka bakai ba ita tunda ba kanwar uwarka ba ce "Arman sosai ranshi ya b'aci Daman shi bai iya b'acin raiba " yace "Daddy daman A saboda Aira ne ka dakeni?Cikin fad'a Daddy Ya ce " A saboda ita d'in zan iya k'aramaka fiye da Wanda na maka Tukunnama fad'amun wata alak'ar ce Ke tsakaninku da bazaka iya rabuwa da ita ba "
"Daddy sonta Nake Kuma Auranta zanyi itace matata bazan rabu da ita ba kome zakuyi Saidai Kuyi Amma bazamu tab'a rabuwa da junan mu ba Fad'anku bazai shafemu ba " So Mummy da Daddy suka fad'a a tare Bai jira sun Sake cewa wani Abu ba cikin b'acin rai yayi Hanyar waje Mummy na kirashi ta na cewa
"Son dawo ina zaka kuma" Dan tasan Halin d'anta bai iya b'acin raiba musamman da har daddy ya mareshi shiyasa basusan b'ata mai rai Dan Duk maganar da tazo bakinshi fad'a yake "Amma ko juyowa Arman baiyiba Mumy zata bishi Daddy cikin fad'a ya ce " ke kuma ina zaki bishi ki rabu dashi mana yaje duk inda zaije yaro ne"
"Cikin marairaicewa Mummy ta ce "Alhaji kasan halin Arman Da zuciya ka bari na bashi hakuri" Tsaki Daddy yaja Ya wuce yabar mata palourn Mummy bin ARMAN tayi lokacin da ta fita harya ja mota yabar Harabar gidan ba yanda ta iya ta koma ciki cike da tunanin Arman d'in Daman Aira ce yake so shiyasa duk lokacin da ta yi mashi maganar Aure yake cemata yana da wadda yakeso cikin ranta ta ce .
"Kaikam son Soyayya batazo maka cikin Sauk'i ba ka kamu da son wacce iyayenku bazasu bari ku mallaki juna ba Sosai tashiga damuwar halin da D'an nata zai shiga Dan tasan Arman ba k'aramun so ne yake yiwa Aira ba Tunda har ya iya furtawa iyayenshi kai tsaye.
Arman kai tsaye Airport ya nufa Yana zuwa ya yanki ticket na zuwa Abuja Allah ya taimakeshi akwai jirgin da zai tashi Kafin 1 hour jirginsu ya d'aga Abuja.
B'angaren Aira har 6 tana daki ga wani zazzafan zazzabi da ya zubar mata Aysha ce ta je ta sameta Da kyal ta lallab'ata ta fito tana rik'e da hannunta a palour ta zaunar da ita ta na mata Sannu tukwana ta d'auko abinci ta dinga bata a baki dak'yal ta samu take karb'a kadan taci tace ta k'oshi.
Man zafi Aysha ta d'auko ta dinga shafa mata tukwana ta b'alla mata magani dak'yal ta samu ta Had'iye kallon Aunty Aysha tayi ta ce " Thnks Aunty"Amma ce dake zaune ta ce "Sannu Aira" tsaki Aira taja tare da kauda kai Dan Duk haushin mutane take ji".
jan bakinta amma tayi shiru dan tasan Aira akwai huce haushi,Hafsa ma dake gefen Inna ta ce "Ko baki lafiya Sis" Itama banza Aira tayi mata ,Aiysha ce ta ce "Kwanta Kan kujera ki huta kinji kanwata" gyada mata kai tayi tare kwanciya ta kalli sama ta rufe idanunta Tunanin yaya Arman ne kawai yazo mata a kwalwa taya ma zaiyu ace su rabu da juna duk wannan dukan da tasha batajin zata iya rabuwa dashi ga haushinta na zarginsu da Abba sukayi Abba hada cemata karuwa sosai ranta ke mata k'una gashi tasan Momy ba k'aramun fushi tayi da ita ba .
Hafsat ce ta kalli inna ta ce "Inna Dan Allah Na tambayeki Allahsa ki fad'amun" Inajin Hafsatu fad'amun tambayarki"Inna wai me ya had'a Daddy da Abba basa jituwo nidai tsawon Rayuwata tunda na tashi a haka na sansu Kuma Idan Na tambayi Mama dalili saitak'i fad'amun ta ce Wai Family issue d'insu ne basainajiba Abun Yajima yana d'auremun kai Dan Allah Inna fad'amun"
"Gyara Zama Inna tayi tare da cewa "Aiko yau zakiji labari tiryan tiryan y'ar nan ki gyara zama kisha labari inbanda abun Halima meye abun boye a Lamarin nan da duniya ma ta sani sannan ta fara da cewa..........โ๐ฟ
*Tofa Abu ya rikice ya kuke tunanin Abba da Daddy zasu d'auki al'amarin nan kowannansu yad'au zafi*
*Ya makomar soyayyar ARMAN da AIRA zata kasance nan gaba Bayan al'amari ya k'ara rikicewa*
*Tofa ga wata sabuwa Hafsa tayi tambayar da kowannenku ke jiran Amsarta bari mu gyara zama Dan shan labari wajen Inna Dan nasan harkun k'agu kuji dalilin wannan gabar*๐
Share fisabilillah
*_Miss Hajo ce_*๐ค๐ฟ
[6/5, 18:30] Hajo: ๐ *NI DA YAYA ARMAN* ๐
Hot love storyโฅ๏ธ๐
```MALLAKAR```
*Hajara L Sadeq*
๐ *JARUMAI WRITERโS ASSOCIATION * ๐
ุจุณู
ุงููู ุงูุฑ ุญู
ู ุงูุฑ ุญูู
*BOOK ONE*๐
๐
ฟ๏ธ..............25&26
.....Kabir Da Abubakar y'an uwane Wanda suka fito ciki d'aya ma'ana uwa d'aya uba d'aya su Ukku ne a wajen iyayensu Abubakar ne Babba Sai Kabir da Abubakar ya bashi shekaru Ukku a duniya sannan Autar su Halima da har an cire ran Haihuwarta.
Saida khabir ya bata sama da shekaru sha biyu Halima Nada wata Ukku Allah yayiwa mahaifinsu Malam Umar rasuwa Mahaifiyarsu Hajara ita taci gaba da kula da su Iliminsu,cinsu,shansu,suturarsu da koman su Tasha wahala sosai akansu Dan dangin ubansu Tunda mahaifinsu ya rasu basu tab'a taimaka musu da komai ba .
Nida Hajara uwammu daya ubanmu ubanmu daya mu biyu kenan a wajen Iyayenmu Koda Allah yayiwa mijin ta rasuwa Saina dawo Wajenta daman mijina ya jima da rasuwa bantab'a haihuwa ba na d'auki y'ay'an Hajara tamkar nawa suma haka suka daukeni tare muka cigaba da kula dasu har Allah ya kawo girmansu.
Sun taso cikin Had'in kai da son juna Abubakar tun yana Yaro yake da sha'awar siyasa yayinda shi kuma Kabir yake da sha'awar kasuwanci Koda Abubakar ya gama jami'a ya fad'a kasuwanci Sosai ya habaka Inda Har yayi Aure ya auri Zainab y'ar nan kano ce mace mai hakuri Shima Kabir yana kammala karatunshi ya fad'a harkar kasuwanci kafin kace me sun Tara arziki me yawa Su suka dinga kula da ni da Mahaifiyarsu tare da kanwarsu da suke ji da ita.
Shima Kabir yayi Aure ya Auri Fatima y'ar gidan Wazirin Adamawa a Chan ya ganta ya aurota itama mace ce y'ar gidan mutumci ana haka ne Abubakar ya fad'a harkar siyasa yayinda shi kuma Kabir yake cigaba da kasuwancinshi Dan harkokinshima yawaici a waje yake yinsu.
Kabir d'anshi d'aya a duniya Muhajed (Arman )tundaga kanshi bai sake haihuwa ba Abubakar ya rik'e mik'amai da dama a cikin wannan jahar tamu A siyasa kuma ya tab'a Senator A shekarun Baya .
Zainab ta haifamai Yara Biyar Umar,Maryam,Aisha,Fauziya(Ummy),sai autarta Halimatu da aka sanya mata suna na" ana haka ne Allah yayiwa Mahaifiyarsu Rasuwa mutuwar da ta girgiza Al'umma musamman ni da Y'ay'anta munshiga damuwa sosai daga karshe kuma mukayi tawakkali ga Allah Yaranta suncigaba da daukata tamkar uwa Inda Abubakar lokacin da ya Gina wannan gidan Da muke ciki ya waremun bangarena guda Sosai suke kula.dani shida Kabir.
Ana hakane k'watsam Kabir Ya had'u Da Rahama y'ar asalin Garin Agadez Bayan rasuwar iyayenta take zaune wajen Babban Yayanta tare da matarshi dake zaune a nan kano yake kasuwancinshi Fara ce sosai ga kyau irin jajayen buzayen nan masu masifar kyau Tunda ya ganta Kabir ya rud'e ba k'aramun so yake mata ba Nan ya samu suka sasinta ita ma har ta Fara sonshi .
Wasa wasa magana ta fara k'arfi Wanda har iyaye suka shiga Aka kai kud'in gaisuwa wajen yayanta ganin yanda Kabir ya rud'e kullum zancenshi Rahama Ya sanya Abubakar cewa shikam ya kaishi yaga wannan rahamar da zata haukata mai k'ani Nan Kabir ya jashi ya rakashi Har gidansu Rahama Koda ta fito Abubakar ya d'ora ido a kanta Yaji duk duniya baitab'a ganin macen da tayi mishi a rayuwa ba sama da ita
Lokaci guda ya kamu da matsanancin sonta Dak'yal ya iya daidaita kanshi suka gaisa tare da musu fatan Alkhairi Kabir yayi mata bayanin yanda suke da Abubakar ta gaidashi cikin girmamawa Har lokacin ya kasa Daina kallon ta .
ita kanta saida ta tsargu tunda Abubakar ya ganta kullum da tunaninta yake kwana yake tashi Ana Hakane Tafiya Ta kama kabir China akan kasuwancinshi Nan ya mik'awa Yayan nashi ragamar komai game da rahama tare da cemai Dan Allah ya dinga kula mai da ita har ya dawo sannan duk abunda take buk'ata ya dinga zuwa yanaji Dan a lokacin waya bata wadata ba.
Tunda Kabir yayi Tafiya Abubakar ya dinga zarya gidan su Rahama Kulawa ta musamman yake bata fiye da wadda Kabir ke bata Tun bata sakewa dashi har tazo ta sake dashi Cikin Dabara Abubakar yayi yanda yayi ya sace zuciyar Rahama A lokacin taji ba Wanda take so saishi.
nan suka k'ulla soyayya mai karfi wanda har akazo ga maganar Aure dukda yayanta da farko ya hana saida ya lura Rahamar na mugun so shiyasa ya hakura ya ce abubakar ya turo iyayenshi Koda yaxomun da maganar korarshi nayi na shiga f'ada Inda na shiga ba tanan nake fitaba Ba yanda baiyi ya shawo kainaba amma naki Nace ba ruwana a maganar Auren cin amana .
Dangin mahaifinshi ya sama ya saye su da kudi su sukaje suka nema mai Auran Rahama cikin k'ank'anin Lokaci ba ayi wata guda ba aka d'aura musu Aure har lokacin Kabir na China Ranar Da aka daura Auren Ranar ya dawo garin Inda ya tarar da wannnan tashin hankalin Wanda ya girmi tunaninshi Yayanshi uwa d'aya uba d'aya ya ci amanarshi ya Aure mai Matar da zai Aura .
Ranar munga tashin hankalin da bamu tab'a gani ba Dan Kabir dukansu shida Abubakar daman suna da zafin kai Shak'e Yayanshi Kabir yayi Ya hau zaginshi da Tsine mashi Wanda dak'yal na samu maza suka rabasu Tofa tun daga lokacin nan suka k'ulla D'aurarriyar gaba da k'iyayya a lokacin Kabir yafi d'aukar abun Da zafi Inda Yayi Aniyar saiya yi mashi ramuwar gayyar abunda yayi mai.
Rahama da Zainab sun had'e kansu sosai dukansu basu da tashin hankali sosai Rahama ke girmama Zainab haka d'iyan Zainab suna girmama Rahama sosai baka tab'a cewa kishiya da kishiya ne dukda kuwa lokacin Mijinsu Yana rid'in Rahama Dan yaso ya nuna yafi sonta a fili amma rahamar Ta k'iya ta nuna batason gwara ya dinga musu adalci kar ya rikita musu Zama .
Ana Hakane Rahama ta samu ciki Sosai Ya d'ora son duniya akan cikin saikace lokacin ne za a fara Mashi Haihuwa Haka Rahama tayi ta rainon cikinta sosai take samun kulawa daga wajen mijinta da kuma Zainab Dan ni haushinta nake ji tunda ta zama silar had'a y'ay'ana fad'a har cikinta ya isa haihuwa ranar wata Juma a ta haifi y'arta kyakyawa Fara Sol wacce ta dameta fari da kyau Tunda aka haife yarinyar kowa ke sonta yayyinta kamar su cinyeta musamman Aysha .
Ranar suna Yarinya taci suna "Hajara sunan Mahaifiyarsu kenan " A lokacin da Aka haifeta Mujahid duk Juma a yana kawomun ziyara Da mahaifinshi ya hanashi zuwa kwata_kwata dak'yal da kuka da kuma na nuna mashi Ya daukeni ba uwa ba hakan yasa Kabir ke barin d'anshi zuwa wajena sosai nakeson Mujahid kamar yanda Tunda aka Haifi Hajara nake sonta Dukda dai bana son uwarta data hadamun y'ay'a fad'a.
Koda yaushe Hajara na bangarena inba kuka tayiba akaita wajen uwar sosai Mujahed ke sonta tun tana jaririya Danshi ya sanya mata Sunan Aira daga nan sunan ya bita a lokacin Mahaifin Aira baya hana Mujahid mu'amula da Aira Dan har lokacin yana jin nauyin K'anan nashi yasan shi yayi mashi laifi hakan yasa bai d'auki abun da zafi ba Dan koda Aira ta girma Har fita Mujahid yake da Ita Yayo mata sayayya a saboda Aira Mujahid Koda yaushe da ya dawo daga Makaranta ya na gida na yana like da ita harta girma.
itama kuma sosai ta shaku dashi koda yaushe tana lik'e dashi Dan idan baizoba Haka zatayi ta kuka Ta rikice sai in yazo ake samun Lafiyarta Bayan Haihuwar Hajara da shekaru Hud'u Rahama ta sake haihuwar d'anta Namiji Aliyu Haidar tun daga kanshi kuma haihuwar ta tsaya mata Chak sai yanzu kusan Bayan shekara goma ta sake haihuwar wannan yaron
Koda Mujahid Yaje Karatu k'asar Misra duk hutun da suka samu saiya taho Dan Ganin Aira Haka har ya kammala karatunshi Inda yana gamawa ya samu aiki a CBN Abuja Dan abunda ya karanta kenan har lokacin Mahaifin Aira bai damu da Taren Aira da Arman ba Dan ko da ya samu aiki Abuja tofa duk karshen mako saiya taho yaganta.
Ana Hakane shekaru Biyu da suka wuce Abubakar ya fito takarar gwamnan wannan jahar ganin haka ya sanya Kabir cewa Shima ya samu damar da zai rama Abunda Yayan nashi yayi mashi Shima ya fito takarar gwamna a wata jam'iyar Wanda Duka su biyun aka tsaida y'an takarar gwamna.
Sosai Abun ya bak'antawa Abubakar Nan aka shiga siyasa ba kama hannun yaro dukansu kamar ba y'an uwaba Dan yanda mabiyar kowannensu ke sukar d'ayansu musamman mabiyar Kabir wakoki da maganganu na habaice habaice na y'an siyasa aka shiga yiwa Abubakar ba yanda banyi dasu ba akan cikinsu wani ya janye amma sukak'iya Hatta kanwarsu Halima da tayi Aure ta auri wani soja a Kaduna Inda ta haifi hafsat kusan sa annin Aira ce kwana ashirin Aira ta bata Dan kusan tattare akayi Auren Halima da Rahama Halima yaranta biyu Hafsa itace babba sai kaninta Sadiq ita kanta ba irin tashin hankalin da bata shiga ba akan siyasar da y'an uwan nata suka fito Dan tuni zance ya baza duniya .
zancen Cin Amanar da Abubakar yayiwa Kabir Y'an siyasa sukayi Amfani dashi dukda ba kowa yasan maganar ba amma suka yayata maganar ko ina Wanda da wannan ne suka samu damar kayar da Abubakar siyasa Dan Sun sokeshi da cewa tunda yaci Amanar d'an uwanshi suma talakkawa zai iyacin Amanarsu Inda suka zab'i Kabir a matsayin gwamnan wannan Jahar yanzu.
Abubakar ya shiga tashin hankali ba Kad'an ba akan wannan Abun da d'an uwanshi yayi mashi wannan ya k'ara rura wutar k'iyayyar junansu Wanda Abubakar yakejin tsabar kiyayyar Kabir fiye da wacce kabir yake mashi Tun daga lokacin Abubakar ya raba Mujahid da y'arshi amma sukaki rabuwa kullum yaganta tare dashi saiya daketa Amma washegari sai ka gansu tare .
daman Hajara wajena take tun tana yarinya to anan suke haduwa da mujahid dan baya shiga gidan su Abubakar ya daina yiwa Mujahid magana ya daina Amsa gaisuwarshi Dan k'iyayyar Mahaifinshi Ta shafeshi Mujahid ganin Idan ya gaishe dashi baya amsawa ya sanya ya daina gaisheshi kwata_kwata Duk yanda Abubakar yaso Raba Mujahid da Hajara gagara abun yayi shakuwarsu sai abunda yayi gaba har zuwa yanzu dai ya kasa rabasu.
To Yau dai kinji Dalilin wannan Gabar da k'iyayyar Duka akan mace macen ma Rahama shiyasa kikaga bana son Rahama inbanda ma ina son d'iyarta da me zanyi da Rahama Mayaudariyar da ta raba mana Kan iyalai Duka fa itace munafukar da ta had'a abun nan da batace tana son Abubakar d'inba da duk haka ta faru ba"
" amma Munafukar Mayaudariyar ta tashi daga kan k'ani ta koma Yayanshi ku yanzu duk a tarihi da kuka taba ji ina kuka tab'a ganin Anyi haka "Inna ta k'arasa fad'a tana hawaye Tare da murje ido ta ce " Ai Tsakani na da Rahama sai Allah ya isa Nasan da Adda Hajara na raye da bazata yarda A auro mata wannan annobar Rahamar ba "Inna takarasa fad'a ta na shaftar Majina".
Hafsat ce da aka gama bata labari saida tayi hawaye jin wannan sark'ak'k'kiyar ta ce Daman ashe wannan dalilin ne ya had'a Daddy da Abba Jin Inna na shiruftu Daga karshe tana zagin Mamy ya sanyata B'ata rai ta ce " haba Inna Daga cewa ki bani labari kuma sai kihau kuka da Zage_Zagen Mamy nidai shikenan labarin ya isa Haka "
"Yoke y'ar nan ba dole na zagi Rahama ba Dole kiga nayi kuka idan na tuna da Abun nan " Aira da tunda Inna ta fara labarin tana jinta tayi shiru sosai surutun ya dameta saida taga ta fara zagar mata uwa ya sanyata tashi cike da Masifa tana hawaye ta kalli inna ta ce.
"Karki sake zagarmun uwa me tayi maki da zaki hau zaginta tun d'azu fa ina jinki na kyaleki" Cikin masifa Inna ta ce "to Mai ido a tsakar ka ai bansan kin damu da uwar taki ba Sai kin rama mata An Zage ta d'in"To wlh karki sake zagarmun uwa tunda uwa ba fin uwa tayi ba kowa son uwarshi Yake ke da dadi a zagar