birgewa da jan hankali.
Wani baƙin ƙaƙƙarfan namiji ne ya sha gabanta, fuskarshi murtuke babu ɗigon fara'a ya tambayeta ina ID card ɗinta, cikin harshen turanci.
"Oh god." ta faɗa tare da kai siririn farin hannunta ta shafa saman goshinta sannan ta zuge zif ɗin jikkarta ta ɗauki Id card ɗin ta sarƙafa tare da bashi haƙuri, janyewa yai daga gabanya tare da bata hanya ta wuce.
Tun da ta shi ta ke ta faman cin karo da mutane mabanbanta, wasu ta tsaya su gaisa wasu kuma ta wuce su ba tare da ta ko kallesu ba, da haka har ta sadu da ainahin inda ta ke aikinta.
Tulin wanke-wanke ne na kwanikan da aka yi amfani da su a ma'aikatar jinge, a yanda idanuwanta suka hango ma ta, na yau kamar sun doke na kullum yawa, haka ta shiga wani ɗan ƙaramin ɗaki ta ɗauro wa ta rigar unifor a saman kayanta sannan ta dawo, har abokan aikinta su biyu sun ƙaraso dama ita suke jira, nan suka hai aikinsu babu ɓata lokaci suna yi su na fira jifa-jifa, a madadin sauran lokuta da ita ce ƙarfin hirar, sau sam bata jin daɗin firar musamman da ya kasance yau zuciyarta a cunkushe ta ke.
"Kutumar uba, uban waye yai min asarar gari haka a ƙasa, wacce me bakin uwarce a cikinku?."
Ale Idi ya yi maganar yana hura ƙofofin hancinansa cike da bala'i.
"Yo wacece ta isa tai wannan ɗanyen aikin in banda matar so, ita ce ta zubar da shi dan baƙin ciki, saboda tasan ƴarta na can na rabawa mazan kan titi jikinta ana fakewa da sunan aiki tana kawo ma ta kuɗaɗe su na cin me kyau ai dole ta zubar mana da gari."
Inna Lantana ta faɗi tana hura hanci gami da harare-harare.
"Ke Lantana ki iya bakinki wallahi, ƴa ta aiko ta ke zuwa ba wani wajeba, kuma nine nan na samo ma ta aikin da kaina munafukar banza kawai wacce batasan hallaci ba."
A masife Inna Laraba ta harzuƙo tare da faɗin.
"Wallahi da gaskiyarta, idan ba karuwanci ba uban mi take fita ta yi, kullum yarinya na fita kwaskwas da ita tana yauƙi sannan ace aiki ta ke zuwa, idan aikinne miyasa baka samowa namu ƴaƴanba, sai ita na faɗa na ƙara yawon tazubar take zuwa ba aiki ba."
Wa ta ashariya me gunna Ale Idi ya lailayo ya watsawa Inna Laraba sannan ya ɗora da faɗin.
"Uban wa ya hana kuyiwa ƴaƴan naku tarbiya ta kwarai, ƴaƴa du sun lalace sun zama tambaɗaɗɗu, yawon ɗaukar magana kwararo-kwararo sun iya shi, na rantse da Allah, du shegiyar matar da ta sake yin mummunar magana akan Najma sai na bata mamaki, munafukan mata kawai."
Wa ni saurayine ya shigo gidan ya na tafe yana layi ya sha yayi tatul ya kalli saitin da Ale Idi ya ke ya ce.
"Ahucu hakanan Dagus, Allah wallahi sai da kai, wato Dagus ka gane ko eh yane waɗancan matan naka ƴan wahala ne, basu da aiki sai halin karnuka du sun cika manah kayi, a huce Dagus a huce, yane ɗan sinno min naira hamsin inɗan busa hayaƙi manah."
Yai maganar yana rangaji irinna ƴan ƙwaya.
"Mtswwwwww Allah ya sawaƙe biyar ɗina ta zo hannunka lalatacen yaro marar amfani kawai."
Cewar Ale Idi yana baza cukuikuyayyar babbar rigarshi ya wuce ƙofar ɗakin Mama Saudah.
Da Murmushi Mama Saudah ta taryi Ale Idi cike da kulawa gami da lankwashe murya kamar ba ita ta gama banbamin masifa ba yanzu ta bi bayanshi ta na faɗin.
"Sannu da dawowa Babansu, ka dawo lafiya ya gajiya da kuma rana, bara in ɗauko maka ruwa ka jiƙa maƙogaronka da shi, dan nasan ka gaji."
Cewar Mama Sauda bayan ta miƙe ta nufi wajen da ta aje kular da ta ke saka ruwa.
"Allah sarki Saudah nah, shiyasa nike tsananin ƙaunarki wallahi Allah, saboda kinfi kaf matan gidannan hankali."
Ya faɗi bayan ya amshi ruwan ya kafa a baki.
Sassanyan murmushi ta dinga jifanshi da shi harda wani shafa kafaɗunshi tana zayyano ma shi yanda ta ke bala'in ƙaunarshi a ranta.
Haka ya dinga washe bakinshi du miyan goro yana murmushi, amma ka rantse da Allah yaƙen kuka ya ke, Saboda Ale Idi yana daga cikin maza marasa kyawun fuska, sam murmushi baya kyau da fuskarshi ko dariya, idan yayi ko yanda kasan an tattaro duka muninshi ne.
Karkacewa gefe yayi tare da zaro damen kuɗaɗe ya ɗora bisa cinyar Mama Saudah sannan ya ce.
"Matar so yau fa kasuwa ta yi kyau, tas na saida kayan miyar yanzu ku ware min kuɗin siyen wasu kayan sai mu ƙirga ribar.
Sam Ale Idi bai iya lissafi ba, duda irin mugun son kuɗinda yake da shi, du cikin matanshi yafi yarda da Mama Saudah ita ce ta iya takunta bata nuna zalamarta ƙiri-ƙiri kamar sauran, hakan ya saka take yi mashi wayau wajen lissafi, kuma idan taga kuɗi bata kawo mashi wa ta buƙata a lokacin, saɓanin sauran matan dasun kyalla ido sunga kuɗi shikenan ba saura ba kingi sai su fara lissafo buƙatunsu kai tsaye, har da marasa amfani, shi kuma daya ji haka sai ya danƙe bakin aljihunshi yai gaba abinshi.
Yanzumma haka ce ta faru, Inna Lantana na ganin ya shiga ɗakin Mama Saudah ta salalaɓo ta laɓe wajen taga tana hangen du abin da suke yi, sai faman cizon yatsa ta ke tana karkaɗa kai, ta na ganin Ale idi ya warci wasu kuɗi ya bawa Mama Saudah da sunan nata ne ladar kwalliya da ruwan da ta nashi, aiko tai wuf ta faɗa ɗakin, bata dira ko ina ba sai gaban Mama Saudah ta miƙa hannu zata warci kuɗin, da hanzari Mama Saudah ta janye hannunta tare da hankaɗe Inna lantana har sai da ta faɗi ƙasa, a kausashe Ale Idi da ranshi ya gama ɓaci ya ce.
"Wallahi kin yi asara Lantana, kinji kunya sannan ki zubda girmanki, ki tattara kayanki ki lalubi hanyar ƙauyenku yau ba sai gobe ba kar in sake ganinki cikin gidannan har sai idan ni na dawo da ke."
Ya na gama faɗin hakan ya miƙe a fisace tare da kaɗa babbar rigarshi ya fice yana banbami.
"Wayyo Allah na higa uku, Allah ya tsine miki Sauda yau gashi ta sanadiyar ki kinja min bala'i, Allah ya isa baƙar munafuka me baƙar aniya."
A maimakon Mama Saudah ta ji haushi sai tashi ta yi tare da soma jujjuyawa Inna Lantana bazazzun mazaunanta tana waƙa cikin yaren buzanci, kamin ka ce mi tuni ƙofar ɗakin Mama Sauda ta cika da ƴan kallo, tun daga kan matan gidan har zuwa ƴaƴayensu da basu samu tarbiyya ta kwarai ba, ita ko, ko a jikinta bata ji komi ba haka Mama Sauda ta tiƙi rawa tana baza canjin hannunta ranta fes.
Inna Lantana na kuka harda fyace hanci ta fito tsakar gida tare da zazzago manyan ashariya ta dinga makawa tana kiran babu inda zata je wallahi, yayinda ƴaƴanta da saura matan gidan suka shiga turata akan karta yarda ta tafi ta, suna kuma jifar Mama Sauda da habaice-habaice.
Najma ba ita ta tashi daga wajen aiki ba sai marice liƙis, lokacin waɗanda zasu yi night sun iso.
Wajen da aka tanada domin bayar da abinci suka nufa ita da sauran abokan aikinsu, su na zuwa suka iske an gama harhaɗa musu abincin da kullum ranar ta duniya ake basu idan sun gama aiki, karɓa suka yi kamar kullum sannan suka fice suna ɗan taɓa hira.
Yauma kamar kullum a daidai lokacin da suka isa bakin makeken get ɗin shiga ko fita daga company, anan ta iske motarshi a fake, ya buɗe murfin gaba, yana ganin sun kusanto waje yai saurin fitowa tare da soma ƙawata kyakkyawar fusarshi da kyakkyawan murmushi.
Tun kafin ya idasa ƙarasowa wajensu Najma ta ɗauke kanta bayan ta tsayar da murmushin da take yi, a daidai saitin ta ya ci burki, ta yanda ta ke iya jin kusancin su da yayi yawa, ba tare da ta ɗago kai ta kalleshi ba ta yi ƙoƙarin kaucewa, amma mi sai ya dinga ɗaga takunsa yana binta du inda ta yi, a gajiye ta ɗaga kyakkyawar fuskarta tare da watsa ma shi wanni kallo irinna ka ƙureni fa, amma mi sai ya sakar ma ta lallausan murmushi kamar kullum.
Wani abu ne ya tokare girjinta, ida akwai abinda ta tsani gani bai wuce fuskar mayenta Abdul ba, sake ɗaure fuska ta yi tamau sannan a tsiwace ta buɗe bakinta tare da faɗin.
"Miye hakan?."
Bata aje ƙarshen kalmar ba ya amsa ta.
"So da ƙaunar ki ne hakan kyakkyawar flower."
"Na rasa acikin mayu wane suna zan kira ka da shi, nace bana yinka ka barni mana."
"Ai ni ina yinki, nawa ma ya ishe mu."
"Bana da lokacinka Abdul please ka rabu da ni."
"Nayi alƙawri akan bazan taɓa rabuwa da ke ba har gaban abada, ke ɗin tawace ni kaɗai, babu wanda ya isa ya raɓe ki da kalmar so, zuciyarki tawa ce."
"Ƙarya kake Abdul baka isa kaja da ikon Allah ba, zuciyata tawa ce, sam baka da gurbi a cikinta, kuma ba zaka taɓa samu ba har gaban abada."
"Ƙarya kike Najma ke tawa ce, sannan zuciyarki ma tawa ce koki so ni koma karki so ni babu ruwana abu ɗaya zan sake jadadda maki shine, babu wani matsuguni a zuciyarki da soyayyar wani mahaluƙi bayan Abdul zata tsaya, zuciyarki tawa ce."
Wani irin ɗumi ne ya lulluɓe cikin tafukan hannayenta, yayinta tsananin ɓacin rai ya turniƙe kafaffiyar zuciyarta, bata san mi ta aikata ba sai da takai dubanta kan hannunta da ya soma rawa.
A razane ƙawar aikinta Khadija ta ja da baya gami da dafe baki ganin yanda Najma ta ɗaga hannu ta wanke fuskar Abdul da lafiyayyen mari wanda ƙararsa ya karaɗe wajen.
Cikin kausashiyar murya ta soma faɗin.
"Akwai banbanci tsakanin zuciyarka da tawa, sam bamu dace da juna ba, bana sonka kuma bazan soka ba har gaban abada."
Caraf Abdul ya damƙi hannayenta duka biyu wani abu da bata san ko mineneba na narkewa a fuskarshi, idanuwanshi ya saka a cikin nata da yake iya hangen ƙiyayyarshi kwance a ciki, sannan ya furta.
"Kin yi kuskure, kin yi kuskure da har kika yarda akaro na farko hannunki ya sauka akan tsadaddiyar fuskata sa sunan mari, wannan marin da kika yi min shine matakin farko da zai ɗorar da ƙaƙƙarfar alaƙa a tsakanina da ke dole ki so ni, dole ki zama mallakina dole inzama linzami da akalar sarrafa zuciyarki."
Sai kuma ya saki hannayenta ya kama fuskarta cikin tafukan hannayensa sannan ya ce.
"Ki shirya tarbata a matsayin masoyinki, domin a koda yaushe zan iya mamayar rayuwarki da zazzafar soyayata."
Yana gama faɗin hakan ya cire idanunsa daga cikin nata da ke faɗar ma shi da gaba, domin ƙiri-ƙiri yake kallon tsanarshi a cikinsu.
Ƙwace fuskanta ta yi tare da zubar da yawu a ƙas sannan da kakkausar murya ta furta.
"Baka isa kayi komi ba Abdul, baka isa ba wallahi, kuma mu zuba ni da kai mu gani, ɗan halak ka fasa, a yau a kuma wannan wajen na yi maka alƙawarin baka kunya, saina saka ka ka ƙaryata kanka da kanka."
Tana gama faɗin hakan ta bangaji gefen jikinshi ta wuce a zafafe tana jin yanda taurarriyar zuciyarta ke tunzurata, amma sai ta yi galaba akan zuciyarta ta hanyar ambaton Allah akan harshenta.
"Ka....ka...kayi haƙuri dan Allah." Ƙawarta Khadija ta faɗa jikinta na rawa, sannan ta giftashi itama ta wuce da sassarfa tana kiran Najma.
VICTORIA ISLAND.
A hankali ya soma buɗe raunanin idanuwansa, amma mi, a maimakon yaga haske sai ya ga duhu me gauraye da hasken dum light da suke kunna kansu da kansu idan dare yayi, a hankali ya soma motsa yatsun hannuwansa yana fatan Allah yasa ba abin da ya ke zargi ba ne ya faru, sai de jin yatsun hannuwan nashi cikin tausasan hannuwa a rumtse ya tabbatar masa da zarginsa, wani ɗan guntun murmushi ya saki tare da juya kanshi a hankali ya kalli saitin Papie da ke barci rungume da hannuwansa a ƙirji, sai ya dawo da kanshi a saitin Mommcy da ita abin nata ya girmi na Papie domin duka hannayenta ta saka ta matse nashi a cikin, ahaka barci ya ɗauke ta, wani sashe ne na raunanniyar zuciyarshi ya motsa da tsananin tausayawa iyayenshi da suka sadaukar da farin cikin rayuwarsu akan shi, shiɗin dai daya kasance gawa ta ƙi rami, shiɗin da yake jiran zuwan mutuwarshi a kullum, yana ji inama ace Allah zai ɗauki ranshi kowa ma ya huta, su su huta da zullumi shi kuma ya huta da wahalar ciwo, kamar ya manta da Allah ne keyin yanda ya so a kuma lokacin da ya so, ya manta da Allah na rayar da matacce cikin rayaye, haka kuma ya rayar da matacce cikin rayayye.
A hankali cikin rashin kuzari ya soma ƙoƙarin zare hannayensa daga nasu hannuwan, a can ƙasan ranshi yana sa rai da abin da baya da tabbacin faruwarsa, hasalima yana gudun du wani abu da zai kawo ayi maganar bare a danganta shi da shi, zuciyarshi na hango ma shi yin aure ne kaɗai zai hutar da iyayensa akan gaganiyar da suka shafe shekaru suna yi da shi, sai de kuma idan ya tuna wani abu, yana hanzarin kawar da tunani nan take.
"Son ka farka ne ya jikin naka fatan babu wani abu, a kira doctor ko mu tafi hospital."
Mommcy da cikin barci ya ji yanda ake son rabata da hannun Mahwish ta yi hanzarin miƙewa, ganin idanuwanshi a buɗe ya sakata soma jero ma shi tambayoyi fuskarta da alamun damuwa gami da tsananin tausayinsa, tausayin da ke zaune akan fuskarta tsawon shekarunshi, tausayi da dam u wa sune suka za ma ado akan kyakkyawar, ko yaya zata caɓa ado yana hango hakan....✍🏻
KUYI FOLLOWING SABON CHANNEL ƊINA DAN SAMUN ZAFAFFAN LITATTAN HAUSA 👇👇👇👇👇👇👇👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb8OWPtBKfi1C9DGBa13
NI CE TAKU MARYAM STAR ⭐⭐
https://chat.whatsapp.com/DczAiFp992p78VNoV6tcMo?mode=gi_t
𝙈𝘼𝘽𝘼𝙉𝘽𝘼𝙉𝙏𝘼𝙉 𝙕𝙐𝙆𝘼𝙏𝘼❤️🩹❤️🔥
𝙎𝙏𝙊𝙍𝙔 & 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙏𝙀𝙉
𝙈.𝙎𝙏𝘼𝙍⭐⭐⭐
💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉 💪
𝗧𝗛𝗘 𝗦𝗛𝗜𝗗𝗢𝗥𝗜𝗔 𝗪𝗥𝗜𝗧𝗘𝗥'𝘀 𝗧𝗘𝗔𝗠💪✍🏻
Chapter 3
Yana hango rauni baibaye da ita, kamar dai shi ɗin, shi daya kasance rauni gaba ɗaya rasuwarsa da komi nasa a raunane ya ke, haka ƙaddararsa ta zo.
Maganada Momcy ta yi ce ta farkar da Papie, haka shima ya miƙe tare da jero nashi tambayoyi yana yi yana dudduba jikin Mahwish ɗin, ƴar siririyar dariya Mahwish ya yi, ganin yanda Papie ke dudduba jikinshi kamar yana neman wani abu.
Jin saurin dariyarsa sai ya nutsar da zukatansu, suka ji farin ciki ya baibayesu, dan hakan na tabbatar musu da ya samu sauƙi.
Mommcy ce cikin muryar rarrashi ta ce da shi.
"Son zaka iya saka wani abu a cikinka in samar ma ka, du yaufa baka ci komi ba tun break fast."
Da disasshiyar muryarsa ya amsa ta da. "Hot chocolate tea."
Godiya ta yi masa sannan ta janyo landline da ke bisa bed side ta dannan wasu lambobi ta kira, ana ɗagawa ta sanar da abin da ta ke so ta ajiye wayar ta sake matsawa gabanshi.
Shi a yanda yake ganin sun saka shi tsakiya kamar wani baby abin dariya ya ke bashi, su kuma babu ruwansu sun dage sai fira me daɗi suke yi mishi du dan ya mance da du wata damuwa.
Ko da aka kawo Chocolate tea ɗin, da kansu suka soma bashi, bayan Papie ya wanke ma shi baki da wani irin brush na ƴan gayu.
Yaɗan sha sosai babu laifi, sannan ya kalli iyayen na shi tare da faɗin.
"Ina so zan yi wanka."
Dayake sun san abin da yake shirin yi har haɗa baki suke yi wajen furta.
"Ga bathroom anan ka shiga manah."
Ɗan kwaɓe fuska yayi cike da gajiyace ya ce.
"Please my lovely."
Amma sai suka kauda kawunansu gefe kamar dai yanda suka saba yi a kullum idan yana so su barshi ya tafi.
Badan ya so ba hakanan ya lallaɓa yayi a nan ɗin, amma bai koma kan bed ɗin ba, sai koma kan lallausar katifa ya kwanta, kyaleshi kawai suka yi amma su yanda zai motsa sai sun taso sun duba lafiyarshi, a haka har nannauyan barci yaci ƙarfinsu su duka.
Kiran Sallar da suka jiyo da lallausar sassanyar muryarsa ce ta farkar da su biyu, kallon juna kawai suka yi tare da murmushi, sannan suka tashi danngabatar da tasu sallar.
Tun da ya fice masallaci da asuba bai dawo ba, acan yai kwanciyarsa dan yana so ya dinga bawa mahaifan space, sosai ya sha barci bai farka ba sai ta ya ji hannu na tattaɓa shi, buɗe idon da zaiyi sai ya yi tozali da kamulalliyar fuskar Papie da ke shirin ɗaukarshi, kafin ya ce wani abu tuni Papie yayi sama da shi kamar wani yaro ya ɗaurashi a kafaɗa ya soma tafiya da shi cikin tafiyarshi ta izza.
Bai dire shi ako ina ba sai gaban wani sink, shima duƙar da fuskarshi papie yayi ya soma wanke ma shi da kanshi, sannan ya janyo brosh me caji ya wanke ma shi baki tas, ya kuma sake saɓarshi yai kan ƙayataccen dinning da shi, a kujerar tsakiya ya zaunar da shi sannan shima ya zauna kusa da shi, sai ya zama yana tsakiyar Mommcy da Papie.
Sauran mutanen gidan da sungama hallara tun ɗazu suka soma gaisar da shi one by one tare da tambayarshi ƙarfin jiki, cike da kulawa yake amsa musu, murmushi baiyane akan kyakkyawar fuskarshi.
Murmushin da ya dasa wani tsiro na tsananin tsana a zuciyar Muhasin da ke zaune wa je, gaba ɗaya ji ya ke kamar ya sanya bindiga ya harbe Mahwish kowama ya huta.
Zuciyarta tafarfasa haka ta tsaida ɗan sahu, murya a cunkushe ta sanar da shi inda zai kaita, Khadija ce ta tsayar da shi ganin yana ƙoƙarin wucewa da Najma, jaka da ledar abincinta ta ɗora ma ta akan ciyarta, sannan taja baya tana ɗaga musu hannu.
Adaidai ƙofar gida ya ajiyeta, naira dubu ta miƙa ma shi sannan ta shiga cikin gidan nasu da sallama can ƙasan maƙoshi.
Gidan Ale Idi kenan, yanzu ka taras ana tafka uban dambe kamar zasu kar juna, anjima kuma ka shigo ka taras anata nishaɗi.
Zazzaune suke akan shimfiɗa kwansu da kwarkwata harda mazan gidan kowa ya dawo gida, yayinda suka zagaye Mama Saudah da ke ta faman basu labari su na dariya, babu wanda Najma ta kallah ta tsallakesu ta shige ɗaki, aje jakarta ta yi sannan ta faɗa akan gado tana jin yanda zuciyarta ke tafarfasa kamar wuyan zafi akan wuta, ji take ina ma zataga Abdul yanzu da sai ta yi mashi abin da bai yi zato ba, wani sabon ƙunci ne ya kuma lullume zuciyartaw lokacin da ta kwanyarta ta hasko ma ta yanda ya Abdul ya riƙe hannunta, bayanan kuma ya riƙe fuskarta a harziƙe ta miƙe tsaye tare da kwalla wa ta iriyar ƙara me razanarwa, sannan ta sulale a wajen kamar gawa.
Su Mama Saudah ana zaune fira ta kai musu karo, sai ji ƙara me razanarwa suka yi ta cike kunnuwansu, da hanzari suka mimmiƙe tsaye su na salati suka nufi ɗakin Mama Saudah inda nan suka ji sautin, da mugun mamaki suke kallon Sauda yashe a ƙasa, kanta suka nufa da sauri Inna Laraba ta tallafota tana girgizata amma shiru, da sauri ta suri kofin ruwa ta shiga yayyafa ma ta a fuska amma shiru, zubewa Mama Saudah ta yi ƙasa tare da rushewa da matsanancin kuka tana kiran sunan Najma, kanta su Inna Lantana suka yi tare da soma rarrashinta cike da kulawa.
An kwashe mintuna talatin ba tare da Najma ta dawo hayyacinta ba, bayan sunyi sallar magrib suka yanke shawarar zuwa asibiti da ita, ana tsaka da shawarar sai ga Ale Idi ya shigo yana baza babbar riga, ganin Inna Lantana tsaye ya saka shi soma faɗin.
"Ke Lantana uban mi kike yi min cikin gida bana ce ki tafi gidank..."
"Yauwa dama kai muke jira ka zo akai Najma asibiti, bamusan shigowarta ba sai jin ƙararta kawai muka yi, muna shiga muka taras ta faɗi, gatacan har yanzu bata farko ba."
Bai gama jin bayanin Inna Laraba ba ya kwasa a guje yana salati ya nufi ɗakin Mama Saudah, kan Najma yayi yana salati ganinta kwance kamar gawa, kama hannunta yayi cikin na shi sannan ya ce.
"Faɗimatu ta shi kinji, babu abin da ya same ki."
Wani abin mamaki a hankali ta soma motsa hannuwanta, daga bisani ta shiga ƙoƙarin buɗe idonta, dishi-dishi ta ke ganin Ale Idi a gabanta, cikin disasshiyar murya ta ce.
"Baba zuciyata, zuciyata zata buga idan banganshi na sake jadadda ma shi cewar na tsane shi ba, ina jin zafi gami da zugi a zuciyata."
Ta yi maganar cikin sanyin murya.
"Ni da kaina zan raka ki ki faɗa ma shi hakan, yanzu dai ta so kiji ƴar babanta."
Ya yi maganar yana taso da ita zaune.
Ruwa Inna Tabawa ta miƙo ta ce.
"Ba ta ruwa ta sha, da alama itama ta yo gado, Allah dai ya kyauta." amsar ruwan Ale Idi ya yi tare da kafa ma ta a baki, sai de ruwan ya taru sosai a bakinta amma ta kasa haɗewa, du rarrashi da ban bakin da suka yi mata amma ruwan ya ƙi haɗuwa agareta, zubar da shi kawai ta yi sanna ta kwantar da kanta a kan kafaɗar Ale Idi gami da lumshe idonuwanta.
Inna Tabawa ce ta shigo ɗakin tare da zama a gaban Ale Idi, ta ƙurawa Najma ido tana ƙare ma ta kallo sannan ta nisa tare da faɗin.
"Iko sai Allah, wallahi itama ta gada, ta yo gado a wajen kakaninta, taurin zuciya ba."
Zuba ma ta ido Ale Idi yayi sannan a sanyaye ya ce.
"Taurin zuciya kuma Inna, tayaya hakan zata faru bayan su sun jima da barin duniyar."
Jujjuya kai Inna ta yi sanna ta ce.
"Kayya Idi, wa yace maka dan sun bar duniya shikenan an shafe babinsu, ka manta sun yaɗa zuriya, gakunan ku har yanzu, tabbas Faɗima ta gado kakanin kakaninta wajen taurin zuciya, ba zata sake samun salama ba a yanzu haka har sai ta aiwatar da abin da ta ƙudurta, abu ɗaya zan sanar da kai shine ka gaggauta samo wanda zai zama mahaɗin rayuwarta, ita nada da taurin zuciya, kuma tun da abin ya soma bayyana yanzu ya zama dole a nemo mutum me raunanniyar zuciya domin shine mahaɗin rayuwarta, masu irin zuciyarta rayuwarsu kan inganta ne idan aka haɗa MABANBANTAN ZUKATA a waje ɗaya, ita zafi da taurin zuciya, sai a samu sai rauni da sanyin zuciya, ahaɗata zama waje ɗaya ko kuma a ɗaura ma ta aure da shi domin inganta rayuwarta, naji matuƙar daɗi da hakan bata faru ba sai yanzu da takai munzalin aure, da ace abin ya bayyana tun a yarinta da ba ita kaɗai ba hatta mu iyayenta sai mun ji jiki, Allah ya jiƙan magaba masu wannan lalura ya haskaka makwancinsu, ita kuma Allah ya sassauta ma ta."
Tun daga kan ƴaƴa da matan gidan du jikunnansu sunyi sanyi ƙalau, su na da yawan rigima da hayaniya amma kawunansu a haɗe suke, kuma su na zama a tare su jajanta idan wani abu ya samu ɗaya daga cikinsu ko da kuwa ƙaramin yaro ne bare babbar budurwa irin Najma,