yaren, sannan tana tambayar taimako na yadda zatana saka su a hanya a wajen malamai da manyan datijan anguwar dan samun nagartacen fahimta tsakaninta da y'ayan y'ar uwar tata, sai kuma ta shiga tunanin takiya da dan waken da ya fada ya shige barci abinsa a lokacin da Hasan ke fadin" Kai acici ko? Ba za'a dafa din ba wannan furar da muka sha ta ishemu har gobe, kai kawai ka ci ka je bayi shine kwonciyar hankakinka? Mtsssssss!"
Ita dai bata tofa masu ba domin yanzu ne zasu rikice wannan yace ta bi bayan wannan wannan yace ai shine mai gaskiya, sai kawai ta shuge cikin itama dan ta cenza suturarta ta samu wankan idan Hassan ya fito daga bayin da ya nufa
Wannan kenan.
______________________________________
πββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈ
_*NI ZAN LADABI*_
πββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈ
*NA*
*SAJIDA NIGER*
Asalamu alaikum wa rahamatullah, makaranta novel dina gani na dawo da sabon takarda, sabuwar tafia, sabon salo mai dauke da darusan rayuwa, da karfin ikon sunnah, da gwagwarmaya da kula kula, rayuwa ce irin ta talaka bawan Allah dake gannin hawa da sauka dan ya rayu da mutuncinsa, rayuwa ce ta Mace mai dauke da hatsari, sadaukarwa, Biyaya da karfi.......zai zo maku da shafuka na gyara tun daga kan fatar jiki, ppart, sirika irin na cikin kurya a gangaro kan sabulai na sana'a da kuma turaran HUMURA wace kowace mace zata iya yiwa kanta tsumamen hadin tada hankalin mai gida
Wannan Novel na kudi ne ba free bane
Yan Nigeria jama'ata ga naku : 500 Naira
account number: 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank sai ka turo shedar biyanka ta numberta kamar haka +227 93811618 SAJIDA NIGER
Jama'ata yan NIGER ga naku : Dala dari , 500 francs cefa ta katin AIRTEL ko SAHELCOM ka turo ta numberna kamar haka 93811618 sai na saka ka
*NA gode sosai, Allah ya saka da alkhairi, sai kun zoπ₯°π₯°π₯°*
*Page 0οΈβ£2οΈβ£*
Barci suka samu wadatace har yama ta kusan yi domin har an fara kiraye kirayen sallar la'asar
A nutse ta mike ta dauro alwallah ta dawo dakin tana tashinsu ta umarcesu zuwa Masallaci da nasihar banda fada a hanya kuma kar daya ya saki ya bar daya a baya su dawo tare
Tana tsaye sai da ta ga fitarsu ta rataya sakata ta sake komawa saman nata dardumar ta kabarta sallah
Bayan ta gama adu'ar da ta saba ita ta ci gaba da yiwa naci, ba zata taba manta daren da aka shigo mata gidan nan ba, ba zata taba manta wannan rana ba, Allah ya tsaya mata ba'a cin mata ba, ama tunda daga lokacin take taka tsantsan da komai da addu'a, ta tabata wanda ya shigo mata ya nemi lalubarta ba yaro karami bane, abinda ya fi damunta yanzun gamawar da zata yi ta leka wajen mai kanti amsar kayan da zata hadawa kulin cen kar ya lalace
Buga kofar ta sakata mikewa ta zira hijabinta dogo sosai ta je ta bude masu tana murmushi hadi da fadin" Oyoyo biyuna"
Hassan ne ya fara shigewa yana cika yana batsewa, da sauri ta dan leka sai kuma ta ja baya kadan tana fadin" Au baba direba kaine ashe ke tafe"
Yar dariya ya yi yana fadin" Gaske Mai tsuntsaye ke hade min fuska daga cewa zasu dawo gidana da zama ina son na auri aminsu, yanzu Mai baban sunna nine Baba?"
Shiru Amina ta yi daga zauren bata leko ba haka kuma bata amsa ba, ita abindama ya fi damunta Husain dake tare da shi yake kuma jin abinda ya fada din
Dan murmushi ya kuma yi ya ce" Ba zaki ce komai ba maman biyu?"
A hankali ta ajiye numfashi ta ce" Uhum"
Daga wannan bata dake cewa komai ba, dama ya san ba nisa maganarsu ke yi ba, ko gidan ta je jefi jefi dan gudun kar Mai Shanu ya tako da kansa yace shi ya zo a yi zumuncin bata kula mutane irin a yi ta hira da dariyar nan, sama sama ake dan gaisawa ta yi gagawar shigewa, a gidan Mai Shanu da matarsa samarin ma'aikatan gidan na mararin mu'amalantar wannan cakwaikwai din budurwa mai yan samari, masu auren wasu na son aurenta wasu kuwa abinda ke cikin hijab dinta suke son yayewa su ga wacece ita a fili, sai dai kamun kanta da mutunta mutanenta ya sa ake shayin kawo mata maganar banza bale har a nemi haye mata fuska, a lokacin da aka diro mata Mai Shanu ne da kansa ya zuba polisawa aka kusan sati ana bincike ama ba'a gano wanda ya diro mata ba, kuma ta ki ta kaura gidan Mai Shanun kamar yadda ya so, ta gwamace mu'amalantar gidan da mai gidan da matarsa mai shekaru madaidaita da manyan mata masu aji yan siyasa na kafawa a jarida suka malaka watau shekara hamsin da hudu a duniya
Kudin dake hannunsa ya ba Husain yana fadin" Dama Mai Shanu ne yace a kawo wannan"
Kudin Husain ya shigo ya miko mata ta yi raf da hannunsa rike da kudin tana hararsa kadan dan irin yadda yake da wani hali daban da dan uwansa na shigewa mutane , shi kowa abokinsa ne ta ce" To ama baba ai kudin watan da ta bada na Waina ba karewa suka yi ba"
Ya ce" Eh sai da yace ta yiwu kice hala, yace ace maki a nan dubu goma kudin makarantar biyu ne, dubu biyar ki yi kudin adaidaita ki yi kokarin ki yi anfani da sauran yana so ki yiwa wainar hatsin nan miya ta gargajiya inaga dai ga dukkan alamu za'a samu ziyarar jikansa ne "
Kai ta gyada kamar yana kallonta sai kuma ta amsa shi ta juya tana sakawa gidan sakata ba tare da ta bashi damar shiga gidanta ba
Da dan gagawa take kimtsawa bayan ta gama yin wanka da rubuta dukkan abubuwan da tsle da bukata, sai kuma ta zauna tana tunanin inda ya dace ta je ta samo kwanuka masu sauki da kuma sauran kayan miyar da a yanzu ba zata iya samu ba gashi wainar tuyar asusuba take yi ta mika masu da sasafe
Hannayen yarenta ta riko suka fito sunna tafia bayan ta rufe gidan da ky dinta
Mijin Inar saude ne ya tsaya a gabansu da adaidaitarsa sabuwa dal sai walwali take yi ya leko kansa yana fadin" Uman biyu ce da kanta da yamacin nan? Sai ina ku shige mu je"
Dan murmushi ta yi ta ce" Aban Saudat mune, ni da kaina ban san ina zan samu siyayata ba na dai fito na san ba zamu rasa ba idan mun shiga ciki sosai wajen bariki"
"Me kike son siya ne?"
Ya fada bayan sun shiga yana kunna adaidaitar hadi da wanata kadan
Amina ta ce" Ina so na yi siyayar abubuwan da zan yi miyar gargajiya harma da kwano idan da hali"
Dan jim ya yi sai kuma ya ce" Ni kuwa na san inda zan kaiki, mu je Rahusa gaba daya abinda kike so zaki samu da rahusa a shagon"
Ita dai bata ce komai ba, hasalima bata dan inane Rahusa ba sai kawai ta yi shiru a bayan motar adaidaitar ya ja su ya tafi
Sun yi tafia mai dan tsayi gaskiya , sunna karasowa ta kalli sunnan wajen ta kalle shi ta ce" Kayan miya fa nace Aban Saudat?"
Daria ya yi ya ce" Kwarai kuwa, ai idan kika shiga nan babu ce kawai babu, komai kuma da layinsa da masu kula da layin, ki je ki gani da idannuwanki "
Kai ta gyada a ranta tana ayana'" Masha Allah mutane sunna da hikimar nema, ama a wannan waje da tun daga nan zaka iya hango bayan ACn dake jejefe ace wai kayan miya ke ciki sunna shan sanyin? Su kayan miya an ci gaba"
A hankali suke tafia, tunda ta shigo wajen ta karanta layin abinda take nema ta dauki hanyar ta nemi shagalta da kalle kalle da mamakin kayayakin dake cike a wajen
Lalle babu ce kawai babu, harta da albasa sai da ta ga kala uku , dadawa ta kasa kasa, kai harta da atarugu gashi a kilace a wajensa, gaba daya sai ta shagalta tgana tura abin tana karanta kudin abubuwan tana dauka a hankali har ta gama siyayar ta koma zagayen kwanonin ta shiga bi tana karanta kudadensu tana zarro ido da mamakin yanzu wani fa sai ya siyi wannan kwanon mai kudin gadon budurwa na aure ya zuba abinci ko? Har ta gangaro wajen kannanun masu kannanun kudi tana karantawa tana waiga manyan ta jinjina kai tace gaskiyane, da bambanci ko a kallo, tana yi ne ba tare da ta kula da kowa ba, koda yake babu wanda ya damu da wani, daidaikun matan nema wata kan alli skin dinta a fuzge ta sake kallonta a fuzge ba tare da ta kureta da kallo ba a ranta ta ayana masha Allah, bata taba gannin black beauty mai lalausan kyau irin wannan ba, bakinta mai birgewa ne da shiga ido sosai, du kuwa irin yadda ya ciza haka yske da shiga ido da birgewa
Sai da ta dauki kwano daya da miya tana duba kudinsu gabanta ya fadi ta juyo da sauri bayanta dan son gannin yarenta
Wayam din da ta gani ya sakata sake wara idannuwanta tana dubawa cikin mutanen dake bangaren kwanonin ko sunna cikin su? Ama wayam babu su babu alamunsu
Da sauri ta juyo kurar ta shiga bin bayanta hanyar da ta biyoa hankali tana furta" Fadeel? Farid? Hasan? Husain?"
Rashin gannin alamunsu ko mai kama da su jikinta ya fara rawa, lokaci daya ta nemi rikicewa tamkar ba ita ba, bata taba jin tashin hankali irin na wannan ba bayan rasuwar iyayenta, kai ko halin da kanwarta ke ciki bai taba daga mata hankali irin wannan ba
A hanzarce ta shiga tura kurar da dan gudu gudu sannan ta kara ware muryarta tana kiran sunnayensu
Da karfi ta bangaji kurar wani mutumen da ya fito yana tura tasa kurar shima , mutumen ba yaro bane gaskiya baban mutun ne kuma kasancewar tasa kurar abinda ke ciki ba wani bane sai batirin da ya zo siya da abin gyaran gashin maza kurarsa ta kifa a wajen lokaci daya ta dafe bakinta da hannayenta ta fashe da kuka tana juyawa ta saki dayan hannun nata ta dora saman kanta da da dan karfi ta shiga fadin" Wayo na shiga uku kardai an sace min y'ayana? Wayo Allahna na shigo nan da y'ayana basa yin nisa da ni yanzu kuma basa tare da ni! Hasan? Husain!?"
Ma'aikatan da suka kwashe kayan suka riko mata kurarta ne macen ta karaso tana kamota tana fadin" Calm down Madame, y'ayanki ba zasu bace ba akoy CCTV ta ko'ina a nan mu je cen baban dakin kusa da office din oga a hasko su na tabata sunna cikin nan sunna yawonsu ki daina kuka ba'a satar yara a nan"
Ita dai bata daina kukan ba, haka kuma bata gamsu da kowa a wajen ba, da sauri take bin matar tana riko fari kal din hijab dinta da ya karra haska hasken duhun fatarta suka zo shiga wajenma abin kallo ne , watau wajen sai ka tsaya nanma an cajeka da abin nan na caje mutun sannan sai an maka daukan zafin zazabin wannan cuta ta zamani mai taken covid 19
Du ta kagauta, bata taba jin tana iya zma terrorist ba irin na yau, a cen kasan zuciyarta babu irin abinda shedan la'anane baya kitsa mata, ciki harda idan har dauke mata ya'ya aka yi ta tabata mai wajen nan ne ita kuwa da hannunta zata bankawa wajen nan wuta kowa ya kone, domin ta san wannan din ba abokin gabar gwamnati bane!
Sunna shiha wani launin kanshi da sanyin daban da na baban filin sana'ar ya buso su, ama ita Amina sam bata ji shi ba, matatakala suka kama hawa sai da suka yi hawa biyu sannan suka shiga Lift ya hauda su hawa na nawa bata sani ba ita dai ta ga an bude nan da nan sun fito
Yan tafia kadan ce suka yi yanzun suka ido mamakeken ofice din dake dauke da na'urorin da ma'aikata manya manyan masu ilimin dake kula da aiki da na'urorin wajen
Sunna shiha kunnayenta suka ringa jiyo mata muryarsa da gura gura watau Husain yana fadin" To kai Hasan tsakani da Allah kaima baka ji ya birgeka ba biscuit din cen? Kuma fa ka ga yinwar yama nake ji, ni walahi dama sauran suka bani na cinye dan na san mama zata biya idan ta zo!"
Hasan da haushi ya gama cika shi na maganar da matar dake tsayen cen ta fada a kansu cewa barayi ne su ko? Sun shigo ne da wa? Wa ya bari yara kananu suka shigo su yiwa mutane sata? Yau sai ta ga iyayensu sun biya kudin biscuit din nan gobema sa saki yara sunna masu barna a waje ya ce" Ka yiwa mutane shiru! Ba zaka ci biscuit din ba! Kai baka tunanin inda Mama take ne? "
" Fadeel" ta fada a raunane tana fashewa da wani kukan da ya fito daga zuciyarta hade da dariya tamkkar wata tabarariyar yarinya lokaci daya fuskar yaren da take boyewa ta bayana a tatare da ita ta duka kasa sosai suka zo suka fada jikinta karfin soyaya da shaukin ganninsu ya debeta yana ta rungumarsu tana kukan hadi da fadim" Ashe ba'a sace ku ba? Ashe kunna nan? Me yasa kuka fita a bayana? Ina kuka je? Wa ya kawo ku nan?"
Muryar matar ne fuskarta a hade tana tsaye cikin shiga ta sweet bakake irin uniform din du wani baban mahaukacin wajen mai dogon wando ne da farar riga daga ciki cikin yaren turanci ta waiga tana kiran wanda take gannin zai fasarawa wannan mai shige da village girl din ta ce" Wannan yaron aka kama yana satar kayan kwalam da makulashe yana budewa yana ci, irinsu ne ke zuwa su yiwa mutane barna a masana'anta, muna bukatar ki sadamu da iyayensu dan su biya barnar da ya yi sannan mu yanka masu kashedin kar su kuma zuwa da yara mararsa ji masu dauke dauke wajen nan, idan sun zo da su su tsaya iya park da su ba sai sun shigo nan ba!"
Tunda ta fara maganar take kallonta, a hankali ta juya wajen yaron da aka nuna, watau Husain yana tsaye sai turo baki yake yi, Hasan kuwa yana hararar matar kamar zai fashe dan takaici da jin haushi
A hankali kunanyenta ke jiyo mata fasarar da saurayin ke bata ama yana kiyaye mugwayan kalaman da matar ta fada kamar irin su kiran Husain da barawo da ta yi, da sauransu ya dai bata maganar a dunkule ne cewa yaron laifi ya yi ba'a bude abu a ci gashi yau oga na nan basa son abinda zai kawo hankalinsa kansu na rashin kula da wani abin
Idannuwanta ta sake zubawa mutumen a hankali ta ce" Ka tabata haka tace ka ce min?"
Sake kallonta ya yi,bama kamar lebenta dake dauke da kalar kasa kuma a kallonsuma sai kyalin laushi suke yi da fari tasss din idannuwanta masu dauke da siririn kwali zuwa hijabinta da ba zai iya fadin sunnansa ba gaskiy har zuwa takalmin dake kafarta dan soso da kuma irin na kafafuwan yaren wanda ya tabata wannan shiga ce ta saka Madame yanke mata hukuncin bata fa ilimin boko harma ta mata kallon talaka futuk da sauransu dai irin na wasu masu kudin da suka raina talaka daga kallon idannuwa suke ganne kai din su ya su ne ko kuma mu ya mu ne, ta haka zasu yanke hukuncin abinda ya dace da kai su yi maka ya sake gyada kansa zai maimaita mata matar da haushi haushi ta daki table din tana rankwafawa ta janye hannun Husain da ya juya zai dauko biscuit din ya nunawa mamansa cewa ba fa sata ya yi ba wannan ne kawai ya bude ya dauki daya shine aka kama su aka ce ina iyayensu aka yi ta nemanta wajen kayan miya ba'a ganta ba shine aka ce karya suke yi su kadai suka shigo, masu tsaron kofa suka ce aa ba su kadai suka shigo ba da mamansu ama aka ki yarda aka kawo su nan, tunda aka kawo su matar nan tale fada tana zaginsu da barayi, sai dai bata bari ya fadan ba ta ture shi da tsawa ta ce" Ka fadawa wannan bagidajiyar ta kira min uwar yaren ko ubansu na dalamesu su bani waje tun kafin sir ya leko ya ji karnin da Yaren nan suke yi da ganninsu a wajen nan ransa ya bace! Yaron nan da gani barawon anguwa ne!"
πββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈ
_*NI ZAN LADABI*_
πββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈπββοΈ
*NA*
*SAJIDA NIGER*
Asalamu alaikum wa rahamatullah, makaranta novel dina gani na dawo da sabon takarda, sabuwar tafia, sabon salo mai dauke da darusan rayuwa, da karfin ikon sunnah, da gwagwarmaya da kula kula, rayuwa ce irin ta talaka bawan Allah dake gannin hawa da sauka dan ya rayu da mutuncinsa, rayuwa ce ta Mace mai dauke da hatsari, sadaukarwa, Biyaya da karfi.......zai zo maku da shafuka na gyara tun daga kan fatar jiki, ppart, sirika irin na cikin kurya a gangaro kan sabulai na sana'a da kuma turaran HUMURA wace kowace mace zata iya yiwa kanta tsumamen hadin tada hankalin mai gida
Wannan Novel na kudi ne ba free bane
Yan Nigeria jama'ata ga naku : 500 Naira
account number: 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank sai ka turo shedar biyanka ta numberta kamar haka +227 93811618 SAJIDA NIGER
Jama'ata yan NIGER ga naku : Dala dari , 500 francs cefa ta katin AIRTEL ko SAHELCOM ka turo ta numberna kamar haka 93811618 sai na saka ka
*NA gode sosai, Allah ya saka da alkhairi, sai kun zoπ₯°π₯°π₯°*
*Page 0οΈβ£3οΈβ£*
"please pull yourself together" Amina ta fada a sanyaye tana kallonta tana ta dane guguwar bacin ran da take tsoron fashewarta a irin wannan lokacin
Dagowa ta yi ta karra daukota da kallo ta watsar, yin turancinta ba shine abinda zai sa ta sasauta mata ba , ta tabata turancin an koye shi ne a boyi boyi ko a titi , watau turancin tsakiyar titi ba na makaranta ba, dan haka ta dubeta ido cikin ido ta ce" Oh kennan kina gane abinda nake fada, ohk ki yi gagawar aiwatar da abinda na fada tun kafin lokacin zuwa sallar oga ya yi ya sameku a wajen nan!"
Amina ta saki hannun Hasan ta matso daf da matar ido cikin ido ta dubeta sosai ta ce" Idan ban aiwatar ba fa?"
Matar ta kalleta da mamaki, ta kalli mutanen da suka dan fara kawo hankalinsu kansu ta dan matsa dan bata so jikinsu ya hadu ta ce" Ke, ki matsa min kadan mana baki san ana fama da cutar covid bane? Idan kika ki kuma sai ki tafi ki barsu a nan na mika su hannun masu horar da barayi!"
Da karfi Amina ta janyo atishawar karya ta maka mata sannan ta ce " Bismillah ki mika mu gaba dayanmu wajen masu horon tunda azalumai ne ku!"
Hankalinta tashe take goge fuskarta da tissu tana fadin maza a kira mata security service!
Jin haka ya kara tunzura Amina ita kuma ta shiga ihun wanda ake gudun ta gannin take son gani, da karfi ta ce" ba kina tsoron kar hankalinsa ya karkato wajenki ba? Shine zaki wulakantamu ki kirayi y'ayana barayi? Na san ke da gani baki san menene yaro ba baki san ciwonsu ba tunda ga dukkan alamu ko mage bakya ciyarwa! Na tabata shi din idan har datijon arziki ne zai maki fadan kira min yayana da sunnan barayi da kika yi!"
A haukace Amina da nake yiwa kallon ko dan yatsana na saka mata a bakinta ba zata taba cizawa ba ta shiga watsar da dukkan abinda hannunta ya kai ta nemi haukacewa a wannan waje har daidai lokacin da secirity biyu suka shigo mata da sauri suka nufota daya ta samu ta damketa sai dai juyin da ta yi da ita ta kubce mata har ta nemi yin taga taga , hakan da suka gani ya daka dayar janyo bindigar teaser dinta ta nemi kashe gaban jikin Amina a lokacin da ta danna zata dora mata shi a lokacin Husain ya gantsa mata cizo a kafarta yana kukan kokowar da ake yi da mamansa , Hasan kuwa yana tsaye wajen mutumen nan da yaren turancin dake harshensa wanda su dukansu sun yi mamakin yaron dama haka yake da turanci a bakinsa yana fadin ya hannasu taba mamansa shima yana daf da fashewa da kukan da idan ya fara ta yiwu yin shirunsa da hakurinsa sai ko zuwa gobe aka danna baban office din da ogan wajen ke ciki da bakonsa da kuma likitansa da ya zo bashi magani domin a yau ranar da ya bi sosai ta bale masa habo har sai da ya yi kiran likitan dole
Docter Mansur , likitansa kuma daya daga cikin abokinsa ne ya ga za'a jonawa yarinyar nan abin nan dake saka mutun yin bori a kasa kamar dan jaki kafin gaba daya jikinsa ya mace har fitsari ake saki fa da sauri yana fadin" stop that immediately!"
Da sauri ta dakata tana kallonsa hadi da dan ja baya domin babu wanda bai san waye shi a wajen ba, da sauri ya dan karaso yana fadin" Subahanalah, me yake faruwa haka a wajen nan , hey boys me yasa kuke kuka? Hey saketa mana, ki saketa menene haka?" Sai kuma ya juya wajen babar mai kula da harkar cctv din ya shiga tambayarta abinda yake faruwa
Kafin ta bashi amsar da zata gamsar da shi Amina dake share idannuwanta da suka cika da kwalla tana tare hijab dinta da aka yaga mata ta dube shi muryarta a shake ta ce" Dan girman Allah ina son gannin mai wajen nan, na yi rantsuwar ganninsa a yau kar kafars ta kamani, idan har ka san inda yake ko kana iya min iso ka taimaka min na ganshi"
Kallonsa Mansur yake yi sannan ya dake kallon yaren dake kuka sunna rike hijabinta , sunnan da suke kiranta da shi Mama ya saka shi sake kallonta kafan sai kuma ya juya wajen da aka yi cirko cirko, a dan hade kadan ya badu umarnin kowa ya koma bakin aikinsa, sai kuma ya dake dubanta a hankali ya ce" Ina fata lafiya? Domin bashi da lafiya ne"
Amina ta hadiyi yawu dake makogwaronta a hankali ta furta" Lafiya lau"
Kofar office din ya nuna mata sannan ya juya wajen ma'aikatan da wace ke son nuna masa bai dace ta shiga haka kanta tsaye ba, bata da damar ganninsa kai tsaye haka bale ba abin kirki ne zai kaita ba , zuwa ne zata yi ta masa rashin kunya may be fiye da haka, sa sauri ya juyo dan idan har maganar cewa rashin kunya ne zata shiga ta yi a office din cen gwara ta zo ta yi wasan kurar da suke yi da kowa a wajen nan ciki kuwa harda shi, domin idan har wata magana marar dadi ta faru a cikin cen daga bakinta bai san me zai faru ba, du inda kake neman dan zafin kai mai tsutsotsin kai idan ka zo kansa ka ja ka tsaya ka dasa aya
Sai dai ya makaro, bayanta kawai ya gani d Ζ΄aΖ΄anta dake biye da ita sun kutsa cikin office din
Juyowa ya yi dafe da gaban goshinsa ya rasa abinda zai ce, sai dai ba zai bar wajen ba sai ya ga abinda zai faru dan baya so a samu matsala ya barsu da rigimarsa su kadai
Da karfi ta bude wajen sannan ta kutsa kanta da salamar da ta zamto tarbiyar bakinta ta shiga baza ido dan ta ga abinda ta shigo nema watau mai wajen
A hankali ya dago lumsasun idannuwansa ya sauke saman kanta da Ζ΄aΖ΄anta dake ta faman rike gefe da gefen hijabinta, tunda ya mike dan takawa bakin da ya yi da sauri ya dawo sanadiyar ihun kukanta, kansa tunda ya