kasana, *ITACE ZATA YI MIN LADABIHHH!*, dan tsufa ya kama ni, sannan na kasance mai son bata damarta na dan Adam mai daraja, har take son wulakantani da yi min bazawar sirri a kan abinda yake *MALAKINS?*, inada iko da dukkan *BAIWAR* da Allah ya bamu, bata san na fi mai rike da bulalar iko ba!, Tashi ki je Uman biyu, bana son kuka ko damuwa, ki shige dakinki ki yi alwallah ki fadawa Allah, yau Lauratu a wajenki zata kwana, Allah ya maki albarka"
Idan ta iya budar baki tace ufan to fa takalmintama da ta saka a jirge ta nufi motar ya yi godiya ko ya yi magana, tunda suka shiga motar kuwa kanta a sade yake bata iya dagowa ba har suka karasa ta kuma ficewa ta nufi falon
Tana budewa ta ga wasu mata biyu zaune sunna zantawa
Ido hudu suka yi da junna, hakan ya sa ta duka har kasa ta gaishe su sannan ta mike ta nufi ciki
Tana nan zaune Baba ta iso itama dakin ta zauna ta fuskanceta ta shiga tambayarta yaya maganar gyaran jiki?
Da mamaki ta kalli babar, gyaran jiki? Wani irin gyaran jiki? Na me? Lallema baba ta iya hade hade a rayuwa
Bata ce mata komai ba, dan ta san ta gama sannin komai, abinda ta so ta ji wanene a cikin ma'aikatan gidan? Dan a yanzuma da ta fito ta ga baba direba sai kallonta yake yi yana murmushi, ko dai shine? Ama ba zata iya tambayar ko babar ba, kunyarta take ji walahi
Alwallar ta dauro ta dawo ta shiga gabatar da sallar magariba , a kan salayar bata tashi ba har aka yi isha'i, kai na takaice a nan harta abincinta nan ya iskota ta dan tsakura ta rufe shi ta ajiye gefe domin burinta ta dauki azumi goben! Ko menene ke shirin tarban rayuwarta Allah ya sa alkhairi ne, ta kasa gaskatawa, ashe itama zata yi aure? Aure fa? Gobe gobe? Shikenan shi babanta bashi da ta cewa kennan? Idanma waye a bata? Anya Baba dan iya zai iya bada y'arsa haka?
Cire komai ta yi a ranta ta ci gaba da adu'arta
Masu jiran Baba kuwa kowa sai kama wajen kwonciya ya yi ya kwonta, domin bai shigo gidan bama bale su hadu da shi
___________________________________
Washe gari
Jirgin karfe tara ya sauka da shi a kasarsa ta haihuwa
Yana samun ntwrk din kasarsa ya shiga kiran numbar baba da layinsa na gida
Abin mamaki tana yin ringin aka daga, kuma muryar baban ce
A tausashe baba ya ce" Ga dukkan alamu ka sauka Baban mutun?"
Abdul Ra'uf ya sauke ajiyar zuciya jin muryarsa ram ya ce" What happened with u? Shin me yake faruwa ne? Ina Hajia?"
Baba ya ce " Tana gida"
Abdul Ra'uf ya ce" Kai kuma kana ina?"
Baba ya ce" Yanzun dai na fito daga kasuwa ni da Malan Liman siyan goro, mu hadu a gidan dan nima cen na nufa ai"
Yana gama fada ya katse kiran yana ta adu'ar da Liman ya karra bashi har suka karaso gida
Gannin motocin Abdul Ra'uf din ya tabatar masa cewa ya karaso, lalle ya zaku ya ga kakarsa yar rigima
Murmushi ya yi yana gyara babar rigarsa dake baza kanshin misk hannunsa rike wayarsa da kuma carbinsa ya doshi falon kansa tsaye
Yana shiga mutanen da ya gani sai da bin ya so bashi dariya, haka kuma irin yadda ake nuna jimamin ba'a ganshi ba ya sake bashi dariya, kamar ya bace din nan?
Shi dai da mutunci ya gaishe su, sannan ya karasa wajen abokinsa da ya sake zuwa da sasafe dan jin idan ya dawo gidan
Hannunda ya kama yana fadin" Mu je saman mana Elhaji, na san Abdullahi ya karaso ko?"
Du yadfa suka so dan fara dannarsa kowa sai ya yi shiru suka haura saman
Tun daga kofar dakin nata yake jiyo muryoyi na mata da kuma nata, ita tana magana da kuka ne, matan kuwa sunna irin abin nan na zigi zigi da nuna sam idan aka yi haka ai wulakanci ne da tozarci,
Hajia ta sake dubansa hannunta cikin nasa ta ce" Kar ka yarda Abdallah, ka tuna kana soyaya da yarinyar nan, yarinya yar gata gaba da baya, ga ilimin boko rututu a kanta, ga kyau ga kwalisa, aljannar duniya ce ita din, idan har ka yarda ya dauki y'ar fa ta gama yawace yawacenta kwararo kwararo ya aura maka ya cuceka, zai aura maka itane dan yana tausayinta, wai ita uman biyu, kulun tana tafe da yara sunna rike da hijabinta, bari ka ji ifan har ka aminta da haka ya wulakantar da girmanka da darajarka, da wahala Honorable ya yarda a makawa yarsa kishiya jahila!, Me take da shi na classssss? Me take iya yi na nuna halin girma? Zata bata sunnanka da nawa, kai ka ga duhun fatarta? Kar ka yarda da wannan hadin ka ji yarona?"
Shi kam abin gaba daya wani iri ya zo masa, kallon kakar tasa yake yi a tsanake yana nazartar abinda take son fadi, shi fa idan za'a yi masa bayani da hargagin nan ba ganewa yake yi ba, ga kawayenta sun ki su yi shiru kowace sai fada take yi,
A tausashe ya ce" Uma ku yi shiru mana daya ta yi magana, nu na kasa fahimta, aure ne za'a yi min?"
A kusan tare suka amsa shi da eh
Da mamaki yana jin murmushi zai subuce masa ya ce" To fah, sai kace yar budurwa? Shi mijin naki bai san ba an daina yayin auren dole ne ko ga yan mata?"
Hajia ta ce" magana nake maka ta gaskiya fa son, ba maganar wasa bace, nufinsa aure zai daura maka nan da kwana uku kennan yau!"
Ido ya dan zarro sai kuma ya dafe habarsa yana dan tunnani, a hankali ya ce" To yanzu kukan da kike yi a waya kika ce zaki mutu baki da lafiya ne? Jikin ne ya motsa?"
Wace yake kira da Uma ce ta karbe maganar da fadin" Aa abin ne ya daga mata hankali mana Gwamna, ni da kaina sai da na ji kamar hawan jinina zai tashi , ka kuwa san me hakan yake nufi? Tun jiya take kuka baiwar Allan nan, duba ka ga yau ko dan kwalin kirki ban daura ba na fito daga gida , soma na yi na kwana sai kuma dai na koma gidan"
Dan kwalin da tace ya bi da kallo, da magangannunta yana aunawa ya ce" Uma, kardai daga ke sai wannan abin na kanki kika fito?"
Uma ta ce" Eh kana gani dai son, ai a mota ne da kyar na iya yin barci jiya, kar ka yarda da auren nan kai kadai ka isa ka bijire masa!"
Mai Shanu da abikinsa, amininsa , datijon arziki da a jiya matar Mai Shanun ta rikita suka sake kallin junna
Mai shanu ya saki murmushi ya dan ja shi gefe ya ce" Yarinyar nan ta wajen mai gadina ce ake magana a kanta, ka san bata samu aure ba.........."
Gaba daya ya kwashe ya fada masa komai, ya dora da fadim" Shine Ni hauwau take neman tozartawa da tara kawaye ana yamadidi da korawa yarona bayani kan kar ya mik biyaya? Ashe basu da hankali? Ashe basu da kunya? Basu san sun girma ba? Kawunna cike da furfura basu gane a kusa suke da rami ba? Inace ba'a yi sati uku ba da daya daga cikinsu ta rasu , basu gane ana masu dauki daidaya ba suke neman izgili da lamarin ubangiji? Matan nan sunna da hankali kuwa?"
Shima da madaukakin mamaki da takaici ya ce" Dama abinda ya sa Hauwau tara jama'a tun jiya har yau kennan? Hasbunnalahu waniimal wakil, hauwaun haka ta zama? Kai kace karfe nawa daurin auren?"
Baba mai shanu ya ce" Shi dai uban yarinyar yace daga azahar har isha'i sunna sauraronmu
Baba Rabi'u zai yi magana sai ga Abdul Ra'uf ya fito daga dakin yana dan tare gaban goshinsa, fuskarsa dauke da murmushin rikicin kakarsa da kawayenta, to rikici mana, wannan maganar ta wuce a zauna a tatauna tsakaninsu su uku a kashe wutar a wuce wajen? Shine take kukan nan? Uhum shi yanzu baima san inda zai lalubo Docter Mansur ya zo ya dubata ba, ya ga du ta kode abinka da farin mutun ido ya jeme mata ba kwaliya wai ita ta shiga tashin hankali za'a yiwa gwamna aure, shi idan sunna kiransa da gwamnan kamar ya fashe da dariya walahi
Hannu ya fara mikawa Baba Rabi'u yana rage tsayinsa , sannan ya kalli Babab yana nazartar irin daure fuskar da ya yi ya ce" Ashe kana nan angin uley"
Sukan yi haka da junna , yace da shi na bar maka shima yace aa aa tasa ce, ama yau sai ba'a bashi amsa ba, hasalima Baba Rabi'u ne ya shiga yi masa nasihar da ta saka shi zubar da dukkan wani yannayi na farin ciki da daukan maganar a shirme yana kallonsu baki daya, har suka gama suka dire Aya
A hankalce ya ce" Ama, baba ka san ai inada wace na tsayar a matsayin wace zan dauka ko?"
Baba ya fuskance shi da kyau ya ce" Ban hanna ka ba, ama a yanzu na cenza shawara sai na ga yannayin zamanka da yarinyar nan sai ka karra aurenka, ABDUL RA'UF na riga na sayi goro na kuma tsayar da magana, idan mun dawo daga daurin auren ma shigo mu zauna da iyayenku da ita yarinyar da kowa da kowa"
Idannuwansa ya wara da mugun mamaki, a san kagauce ya dubi kansa, farar shada ce a jikinsa dinkin tazarce, simple bata da adon komai a jikinta sai hular dake kansa , kayan tunda asuba ya saka su, kai bama wannan ba sai kace mutuwa wannan abu a kagauce?
"Ba zaka yi min ladabin ba?, Ba zaka bi umarnina ba? Nace ba zaka amsa maganata ba? Kana da damar bijirewa kamar yadda suka ce, kana da damar kiyawa tunda ai dama kaine mai kudin, hausawa kuwa suka ce mai kudi uban iyayensa!, Zamu yi gaba da jama'ar da na gayata, idan mun je cen din zamu daura auren, kafin nan kafin azahar ka yi kirana idan ka ga ba zaka iya ba kace da ni kar na saki na daura, domin ba zan so na yi maka auren dole ba, ai kai ba yar budurwa bace!, Rabi'u mu je" Baba ya fada a hasale ya fara yin gaba da tafiyarsa ta tsanake dan baya oya mugun sauri jikin tsufa
Sosai baba Rabi'u ya dan kara tausarsa da nuna masa ya yi Ladabi wa kakansa, ya isa da shi kar ya bashi kunya, sannan ya bi bayan tsohon ba tare da ya yi masa tambayar waima wacece ne? Shi gaba daya gani yake yi ai mafarki ne wannan din, wani irin almara ce wannan? Aure? Aure fa? To da bai zo Bama za'a daura masa auren ne? Wannan wani irin abu ne? Wacece wai yarinyar nan da kakarsa ke ta fadin ta gama yawace yawacenta? Kuma shine shi za'a daura masa? Ya salam
Jikinsa ya ji na damunsa da gajiya da kuma kasala dan haka sai ya koma ya dauki darduma a dakin hajia da ta daina kuka hankalinta kwonce ta san am gama tunda ta yaron ya kuma yarda da maganarta
A hankali ya fice baya ya shinfida dardumar ya karasa wajen pampo ya daura alwallah ya koma ya zauna ya dauki carbinsa ya shiga ja, ko yinwar baya ji, ya fi irga lokaci da duban hanya, y kula samarin gidan sai ficewa suke yi a motocin gidan, har gidan ya dauki shiru , aka fara kiraye lurayen sallar azahar
Kasa fita waje ya yi ya kabarta ya shiga bin sallar daga nan,, har aka salame ya sake Ubbawa wayarsa ido da tunanin in dai da gaske ne yanzun ana cen ko an daura masa aure da bakuwar da bai san ko wacece ba ko za'a daura masa
Kai yau shi ya ga masifa lukuta walahi
Sannu sannu har karfe biyu ta gota, dan haka ya mike ya dauki dardumar da nufin yin tsakar gidan
Sai dai hango mnai gadi ya wangale kofa ya saka shi cenza akalar tafiyar ya dauki doguwar hanyar wajen mangoro dan burinsa ya dan labewa hayaniyar da ya tabata za'a yi a gidan nan a yanzu ,,. Dan baya so tta summe idan ta ji an daura masa auren nan, shi su bashi dama ya fahimci abinma sun kasa bashi, uhum wani abu sai hausa!
Tunda ya taho tunani ya cika kwakwaluwarsa, haka itama dake tahoha dan ta koma dakinta ta kicin kamar yadda ta biyo ta zo ta wuni a karkashin mangwaron nan dan ta gujewa abinda Baba Lauratu a sakota a gaba da shi wai wani gyaran jiki har ta kama ta murza mata man ja da kurkum a jiki sai karnin man jan tale, shi yasama ta ki saka hijabinta ko daya dan bata shirya lalata hijabi ba a kan shirmen gyaran jikin auren da bata san da waye ba, kawai ta fito da doguwar rigarta sai dan kwalin rigar ta yane kanta da shi, kanta a kasa tana ta tunanin a wace ake ciki ne? Ina baba yake ne bata ganshi ba tun jiya? Shin yaya maganar da ya mata ne? Allah ya sa an fasa
A zuciyarta ta ayana' Allah ya sa baban yace aa an fasa ba yanzu ba , ba zai bayar da................." Kim, kum duskarta mai dauke da man ja da kurkum tana kyalin mai ta kumun masa a gaban kirjinsa da farar shadarsa
A rikice ta saka hannunta da ya dauki yellow din kurkum din ta damuki rigar tana furta" Aushhhhhhhh subahanalah wa........."
Dif maganarta ta dauke a lokacin da ta yi arba da sajjen fuskarsa da kuma hasken fatarsa da kamaninsa
Shima da hanzari ya rike damtsen hannunta ya janyeta baya yana yatsina fuska da binta da kallo da son tuno wacece wannan a ina ya san fuskar wanann, bale dan kwalin da ya yaye sak sai ya so tuna masa wata fuska daban
Dan tsakin da bata dan da shi bane ya bale mata ta shiga jan hannunta, sai kuma da dan karfi ta ce" Malan cikani mana meye haka!"
Idannuwansa ya wara a kanta, nan take a ransa ya ayana 'Fitsarariyar nan ce!' ,
A hankali hankali ya shiga dan nitsa mata hannunsa a damtsen da take gannin na mai karfi ce ita yana kallonta sai kuma ya dan matse hannun yana tsaye kikam yana kallon yadda ta kawo dayan hannunta tana zarro ido hadi da kokowar son kwace kanta a haukace ta ce" Kai baka da kunya ko? Ka cikani ni sa'arkace wai da zaka matsen hannu ? Kai ka...........
Wai wai wai wai wai wai wai gwarama in ji kawata
Nace ba, kin kuwa turo naki katin? Nan na tsayar da free, kuma in sha Allah shi din babu na aunty sajida a taimaka min da NI ZAN LADABIHHHH, domin a cikinsa zan baje basira na bada maganar gyara na sana'a ba cuta ba cutarwa .........garzayo yar uwa mu je da ke rikicin mai karfi ne.......wai yaya tafiar zata tafi ne? AMINA fa baba ce bata son raini, ga kuma wanda ya fita gannin shine baba , a samanta yake, uwa uba su din mata da miji suke a yanzu....wai yayane , *WAYE ZAI YI LADABIN?*,
GA kuma hajia a gefe, kun tanadi ruwan watsa mata dan ta farka idan ta summa?, Wai yayane maganar yar gidan honorable? Iyayen gida mune da kambun wannan karo, tafiyar tamu ce! Ku buga mana tamburan aunty, hajia sannunki yah mama, kece uwar gidan gidan oga, kece za'a yiwa ladabin fa!
Maman jariri nace ba? YayaneπΆπ»ββοΈπΆπ»ββοΈπΆπ»ββοΈπΆπ»ββοΈπΆπ»ββοΈ
S
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels