masa a zuci na naiman zautar da shi. Shi da kansa kunyar kansa yake ji, baƙin ciki mai girma na da ɗa mamaye zuciyarsa.
Ɗayyib da ya juya ya kalli irin gyaran da Masautar Yankin ya samu da dukiyar da kai tsaye za'a kirasa da na Malik da irin manyan mutanen da ya ɓata dukiya ya gayyata saboda Kabeer kawai, sai ya ƙara juyowa. Da wani irin fushin mai girma yake yankar Sufyan ta ko ina yana maimaita
"Ko Marigayi Sarki Musa zai dawo duniya a raye ba zan yimasa irin wannan hidimar ba na rantse da Sarki Allah! Sufyan ka cuceni! Ka cuceni!!"
Daƙyar aka ƙwace Sufyan da ya yi kacha-kacha da jini a hannun Ɗayyib da ya zama kamar Mahaukaci.
Mutanen Jalal ne suka ja Ɗayyib cikin Gida, shi kuma Sufyan aka wuce da shi Asibiti yana ihun azaba kafin ya sume.
Sarki Hammam a take ya bayarda umarnin a rufe iyakar Yankin Tudu, kuma a turo masa Kabeer cikin Iyayensa da gaggawa.
Da ƙananun gulmammaki taron shagalin bikin Sufyan ya watse maimakon yabo da ya ci burin yasamu a wajen Mutane.
Kamar yadda Sarki Hammam ya bada umarni haka akayi sai dai babu Kabeer babu Iyayensa. Da gaggawa Sarki Hammam ya ƙara bayarda umarnin abi duk Yankin da yayyen Kabeer mata suke aure a kamo su. Sai dai suma duk basanan acewar Surukansu sun bar Gida da sunan zuwa shagalin bikin Ɗan shugaban kasuwar zinaren Yankinsu tare da rakiyar Mazajen su da Ƴaƴan su.
Babu inda ba su bincika ba amma babu Kabeer babu ahalinsa. Dagaske dai Kabeer ya gudu da dukka ahalinsa.
Ɗayyib da labarin ɓacewar Kabeer da ahalinsa ya riskesa Ihu ya kurma haɗe da ɗaura ɗamarar binciko Kabeer da ahalinsa a duk inda suke. Fadawan Sarki Hammam majiya ƙarfi Jalal ya bawa umarnin tare Ɗayyib daga barin Masarautar, ya na fizgewa suna tarosa, daƙyar suka danneshi aka nemo likita ya yi mai allurar barci.
WAIWAYE
Da Malik ya ɗauko Kabeer daga gidansu a sirrince ya fitar da shi iyakar Yankin Tudu sukabi Jirgin samansu zuwa ƙasar Abyad.
Daga wannan rana Malik baiyi ƙasa a gwiwa ba sai da Kabeer ya zama abinda zai sosai zuciyar Ɗayyib da shi. Ya na shirin ɗauko Iyayen Kabeer, bikin Sufyan ya Kunno Kai, don haka suka turasa bayan sun shirya yadda zai taho da Iyayensa da zarar taro ya hargitse.
A zahirin gaskiya Kabeer shugaban Sufyan ne a wajen aiki amma ba shi ne GM ba, Uzair da Naila ta taɓa ganin mai tsananin kama da Salman ne GM.
DAWOWAR LABARI
Lokacin da Ɗayyib ya fara yiwa Sufyan magana, Kabeer ya sulale da Mahaifansa har da ƴan uwansa suka bar Yankin, dama kuma tuni motocin ɗaukar su Kabeer yana Yankin amma saboda taron mutane yasa babu wanda ya ankara.
NAILA;
ɗaukemata waya da Bayin Gidan Sarki Hammam sukayi ya zama iyaka tsakaninta da Yasar, saboda tanan kawai yake iya sanin halin da take ciki. Lamarin ya sosa zuciyarta tare da ɗaga mata hankali sama da Sakin da Sufyan ya yi mata, domin ko bai saketa ba, dama tayi alƙawarin bazata ƙara iya rayuwar auren rashin ƴanci da shi ba.
Damuwar da ta shiga akan hanyar da zan ƙara samun Yasar ba ƙaramin tashin hankalin Kaka ya yi ba, cikin ƙarfin halin ɓoye ta ta damuwar take jaddamata ko da karo-karon ne zasu haɗamata kuɗin Mota ta koma Makaranta ita da ƴan uwan Mahaifinta dana Mahaifiyarta har ma da mutanen Yankin.
Wannan ƙarfin gwiwa da Kaka ta bawa Naila sai ya gusar da duk wani damuwa da fargaba da ke danƙare a cikin zuciyarta na fara walwala kamar kowa.
A haka suka kwashe kwanaki uku cikin gidajensu, ba tare da dogon zirga-zirga ba, abisa umarnin Sarki Hammam.
SUFYAN; yasha azaba irin azabar da bai san akwai irinsa ba, kullum cikin kuka yake tunda ya farfaɗo daga duniyar azabar da Mahaifinsa ya kaisa.
Sumaya ta na gefe itama tasha kuka idanuwanta duk sun koɗe, wahalar da bata taɓa tunanin zatasha ba har su gama rayuwar Aurensu da Sufyan shi take sha, idan zai yi fitsari da Toilet duk ita take taimaka mai gashi da raki kuma ita dama can ba saba aikin wahala ta yi ba.
Ga shi
Bayin ma da aka bari Maza ne masu gadinsu balle su taimaka mata.
Ƴan uwanta suma gaba ɗaya sun matsu su koma Birnin Abyad, danasanin rako Sumaya Yankin Tudu na damun zuciyarsu.
A ɓangaren Hindu bayan barinta Yankin Tudu zuwa Yankinsu, kai tsaye wajen Malaman dubanta ta wuce.
Tabbacin suka bata na; nasarar Sufyan da isarsa tsakiyar Babban Birnin Abyad da kuma samun ɗaukakarsa mai girman gaske ya na tare da Naila, babu abinda ya sauya.
Amma ita da Sufyan sun karya dokar da aka shimfiɗa musu tun farko. Na farko zaman Sufyan a Birnin Abyad saɓanin Babban Birnin Abyad da aka sharɗan ta musu, na biyu gaggawar Sufyan na yin Soyayya da Sumaya har da aurenta. Na uku sakin Naila da ya yi, shi ya ƙara wargaza komai.
Da rawar murya kuka Hindu take roƙon asama mata wata mafitar tun da wannan ya lalace.
Sihirin da za'a shayar da Naila ya bata na tsahon kwanaki uku ba tare da rarrabewar kwanaki ba. Zata dawwama a ciwon da babu magani, bayan tasha wahala Sufyan zai je da sunan taimakonta.
Idan har Iyayenta sun amincewa Sufyan ya samu damar ɗaukarta zuwa Masarautar su to ta dawo za'a bata maganin da zai karyar sihirin da sukayimata ta samu sauƙi, daga nan sabon shirin tunkurarsu Babban Birnin Abyad zai kankama da zafin da dole nasara ta tabbata. (Anya wannan nasarar zata tabbata🤔)
Da wannan ƙwarin gwiwar Hindu ta fara shirye-shiryen dawowa Yankin Tudu, bayan tayi kwanakin da ta ɗibarwa kanta.
ƊAYYIB
Har sati ɗaya ya shuɗe idanuwan Ɗayyib ba su washe ba, baya iya magana saboda baƙin cikin da suka yi mai karo. Ko Asibiti yakasa zuwa duba Sufyan, itama Hindu tattare lamarinta ya yi ya watsar, burinsa ya samo ina Kabeer da Malik su ke, su bashi labarin wanene Uban gidansu.
Babban Malamin duba da suka musanya bayan faɗarsu da Sarkin Tsafin Yankin Tudu Jalal ya gayyato tun daga wata ƙasar domin fayyace musu abinda Ubangiji ne Masani akai.
"Ina su Malik da Kabeer suke? A wacce duniya suke rayuwa? Shin dagaske Kabeer shine Uban gidan Sufyan. Wanene ko wacece asalin Uban gidansu? Waɗannan tambayoyin shi su Ɗayyib suke neman haske a kansu ido rufe.
Bayan sun gama korowa Malamin duba bayani.
A duban da ya yi
Abu ukun da suka tambaya bayyanannu ne amma na ukun saninsa sai Allah.
Na farko inda Malik da Kabeer suke da duniyar da suke rayuwa, na biyu kuma shin dagaske Kabeer shine Uban gidan Sufyan,
Na ukun da ya kasa gonowa shine sanin asalin Uban gidan su.
Amma ya kuɗurce a ransa bazai gayamusu ba sai abinda zai faranta ransu su biyasa kuɗi mai tsoka, don haka ya gyara zama ya yace;
"Kabeer da Malik suna wani gari ne Daf da shiga Babban Birnin Abyad, kuma suna rayuwa ne kusa da Company da Sufyan yake aiki ba a cikin asalin ƙwaryar Babban Birnin Abyad ba.
Kabeer kuma ba shine Uban gidan Sufyan ba, a yadda dubana ya nunamin Kabeer ba shi baya aiki ma da Ma'akatar su Sufyan kawai rufa ido ya yi muku. Asalin Ubangidan Malik kuma Macece wacce ta taɓa zama a nan Yankin Tudu amma nakasa gano asalin wacece"
Da sauri Ɗayyib ya miƙe yana dariya, cikin yaƙini ya ce idan ba Nanaah Faɗima ba ( kakar Sulaim matar Ubaidu) to Aysha ce( matar Abduh Dhahab Mahaifiyar Sulaim). Da sauri malamin duba ya gyaɗa kai alamar gaskiya ne.
Kuɗi masu nauyin dake bayyana jindaɗinsu suka sauke mai. Da murmushin samun nasarar duƙunƙune sun da ya yi, ya saɓa jakarsa ta zallar fata ya yi musu sallama. A zahirin gaskiya Kabeer da Malik tabbas a kusa da Company Dhahab suke rayuwa, amma da gaske Kabeer shine Uban gidan Sufyan yasan idan ya faɗi gaskiya a matsayinsa na babban malamin duban da suka ɗauko tun daga wata nahiyar ba zai samu kuɗi mai tsoka ba, batun Macece ko Namiji ne asalin Uban gidan su Malik ba shi da sanin komai akai, shima ya faɗa ne don ya faranta musu shima su faranta mai. Da mugun murmushi malamin duba ya hau motar da zai sadashi da iyakar Yankin Tudu da tumulin kuɗinsa a jaka.
Da gaggawa Ɗayyib da bai taɓa zuwa duba Sufyan ba ya ɗauki hanyar Asibiti, ɗauke da wayar Sufyan da ya jima a kashe.
Bai damu da halin da Sufyan yake ciki ba, ko yaya yanayin jikinsa yake ya naimi waje ya zauna.
Cikin sanyi murya Sufyan ya gaisheshi. Da sakin fuska ya amsa yana yi mai yaya jiki, ko kallon inda Sumaya take baiyi ba, balle ya yi mata godiyar hidimar da takeyi da ɗansu, sai ta basu guri zasuyi magana da ya faɗa a kausashe.
Jiki a sanyaye Sumaya ta bar Ɗakin nadamar auren Sufyan na mamaye ruhinta, tausayin Naila da ta fita shaƙar takaici da rashin samun rayuwar Ƴanci na tsarga mata, "ashe haka Naila take ji? Wallah na cuci kaina kaicona!" Ta faɗa ƙasa-ƙasa cikin kuka.
Bayan fitar Sumaya Ɗayyib ya mayar da kansa kan Sufyan. Wayar Sufyan ɗin ya miƙamai.
Babu wasa a fuskar Ɗayyib kamar ba Mahaifinsa daya sani a baya ba.
Jiki a sanyaye Sufyan ya kunna ya ajjiye yana jiran umarnin da zai biyo baya.
"A baya ina lallashinka domin ka yi min biyayya akan abinda kai ne zaka samu cigaba ba ni ba, amma ka bijiremin, to a wannan karon ba cigabanka bane kai kaɗai cigabanmu baki ɗaya, mun gayyato malami daga wani Birni, ya kuma shaida mana Kabeer ba shine Uban gidan ka ba, rufa ido ya yi mana, ba wai don ban yarda da shi ba, sai don na ƙara tabbatarwa nakeson ka kira wanda ya miƙa katin gayyatar bikinka wajen GM ɗinku ka ji dagaske ne ko a'a"
Sufyan yaso ya musa, amma tuna irin yankar da ya sha yasa ya fara lalubo number jikinsa yana rawa.
Bugun farko aka ɗaga da Muryar jimamin da ya nuna andaɗe ana naiman mutum ba'a samesa ba. Bayan sun gaisa da hanzari Baturen yake tambayar lafiya, bai dawo aiki ba ko fushi yake yi GM bai samu halartar taron shagalin bikinsa ba, ya yi haƙuri uzuri ne ya tareshi, ga ayyuka ta ko ina a office amma ba bu shi, don Allah ya dawo.
Daga Sufyan har Ɗayyib ajiyar zuciya suka sauke mai ƙarfi kafin Ɗayyib ya tashi ya rungume Sufyan cikin kukan farin ciki ya ce;
"ɗana Sufyan ina mai neman afuwarka, sai dai banason wannan damar ya zama abin sakankacewa garemu, inaso ya zama fitilar haska mana asalin wacece ta ƙara dawo da Dhahab a tsakanin Nanaah Faɗima da Aysha" Sufyan da yake son tambayar su wanene Faɗima da Aysha shiru ya yi tuna Mahaifinsa zai iya tuhumar mai yasa bai sansu ba.
A haka Ɗayyib ya share hours ya bar Sumaya zaune a waje ba tare da damuwar komai ba. A wannan yanayin Hindu ta iso Asibitin kallon inda Sumaya take batayi ba balle ta amsa gaisuwarta.
A wannan karon ma ɗari bisa ɗari Ɗayyib ya amince da batun da Hindu ta zo dashi, tare da bawa Sufyan umarnin sakin Sumaya da zarar sun koma Birnin Abyad ya ajjiye maganar Soyayya ya fuskanci gobensa. Sai dai dole sai sunyi taro na musamman a kan yadda za'a shayar da Naila sihirin da Hindu ta zo da shi.
Shi dai Sufyan kai kawai yake ɗaga musu saboda tsoron yin magana ma yake yi.
Tun a baya kowa yasan mutanen Yankin Tudu da son kansu da tsananin butulci, sai dai talauci da tsananin rayuwa ya sa suka sauya zuwa mutanen ƙwarai, amma duk da haka ba'a rasa nono a ruga kuma baza'a taɓa taruwa a zama ɗaya.
NAILA
Sartaj ya na ɗaya daga cikin matasan da suke yawan shigowa Gidan Kaka, kuma yana daga cikin waɗanda suka dinga bata kariya, yawan shigowarsa ya haifar da shaƙuwa a tsakaninsu har yakan ci abinci Gidansu.
Da ƙwaɗayin asalin jinin Yankin Tudu da butulcinsu da bai gama barin jinin Sartaj ba su Ɗayyib su ka samu dama sukayi amfani da shi. Sai dai shure-shure baya hana mutuwa....✍🏻
Na gode da Addu'o'inku Allah Ya bar mu tare Ya kuma bar zumunci.
[7/28, 9:46 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥
NAFISA ALIYU SASAAL
Page 22
Kuɗi masu nauyi a hannu da rashin albarka wajen sauke buƙatu Jalal da kansa ya biya Sartaj, bayan ya siyar da yardar da amince dake tsakaninsa da su Naila.
Da tattacen kayan marmari Sartaj ya fara amfani. Ya na zaune suna hira da Naila har ta shanye. A kwana na biyu da yankakkun kayan marmari ma su kyan gani a ido ya yi amfani. A kwana na ukun da ya kasance na ƙarshe da abincin Gidan Kaka ya yi amfani.
SUFYAN; Sufyan bai ƙarasa warkewa ba suka tattara suka koma Birnin Abyad da sunan idan sun isa ya miƙawa Sumaya takardar ta kafin ya wuce Babban Birnin Abyad bakin aikinsa.
NAILA;
Labarin tafiyar Sufyan bai zama abin damuwa a gareta ba, domin abinda kake so shi kakeyiwa kishi.
A hankali ta fara ramewa ƙasusuwan jikinta suka fara bayyana kansu kamar ba ta cin abinci, kasalar rashin son yin Sallah a kan lokaci da ƙinyi azkhar na neman zamemata jiki.
A cikin kwana biyar tayi wani irin ramar da ya tsoratar da kowa.
Kaka bata wahalar da kanta wajen kai Nsila Asibiti ba, tunda tasan su wanene Iyayen Sufyan. Malamin da ya taimaka mata a waccen lokacin da Hindu ta ciyar da ita Tufa mai ɗauke da sihiri ta nufa.
Bai buƙaci a kawo Naila ba da kansa ya zo. Ya na ganinta ya tabbatarwa da Kaka abinda take zargi, sai dai sihirin da aka yiwa Naila ba irin nata bane, samun maganinsa abune mai matuƙar wahala domin a wajen wani Malami da ke gabashin Yankin Tudu za'a iya samu maganin karya Sihirin.
Cikin kuka Kaka take faɗin; "wanene ya zaɓi Duniya akan lahira?, wanene ya zaɓi shayar da marainiyar Allah sihiri irin wannan, Allah bamu da kowa sai Kai!"
Babu wanda bai tausayawa su Naila ba.
Cikin fusata matasan Yankin suka nufi da suka samu labari suka nufi Gidan Sarkin tsafin Yankin Tudu ya duba musu wanene ya shayar da Naila Sihiri?..
A take kuwa yana dubawa ya gano Sartaj ne.
Gangamin Matasan Yankin Tudu ne sukayiwa Gidansu Sartaj zobe, Sartaj ba shi da Uba sai Uwa itama ta fara tsufa.
Cikin alhini da fargaba take sanar da su yanzunan Sartaj ya ce mata zaije Fadar Sarki Hammam gurin Mai girma Jalal wai yana naimansa.
Bayaninta ya ƙara fusatar da Matasan tare da ƙara tabbatar da maganar Sarkin Tsafi, don haka suka koma Gidajensu kowa ya ɗebo makamai sai fadar Sarki Hammam.
A fito musu da Sartaj su yankemai hukunci dai-dai da abinda da ya aikata. Suke ta nanatawa bayan isarsu Harabar gidan Sarki Hammam.
Ihun su da maganganunsu ma su khaushi ne yasa Sarki Hammam umartar fadawansa su lallashesu su kuma sanar da su Sarkin Tsafin Yankin Tudu ba gaskiya ya faɗa ba, so yakeyi ya hanasu zaman lafiya tunda ya ci amanar Masarautarsu ta koresa shiyasa su ma yake so ya tunzura su. Kuma lallai ya na bada umarnin kar wanda ya taɓa lafiyar Sartaj idan ba haka ba zai fuskanci hukunci mai tsanani.
Duk da an sanar da Matasan Yankin Tudu wannan jawabi na Sarki Hammam basu motsa ba, har sai da Sarki Hammam ya fito da kanshi ya taushesu da kalamai ma su taushi tare da tabbatar musu da ƙarya Sarkin Tsafin Yankin Tudu yake yi, Sartaj da ya ke na hannun damar Naila tayaya zai ciyar da ita sihiri?
Ba don sun gamsu ba sai don bin umarnin Sarki Hammam wajibi ne a garesu suka tattara suka dawo Gida.
Da labarin abinda ya faru ya isa wajen Kaka ba tace komai ba sai kuka da takeyi tsoron mutane da rashin yarda da su na ƙara kamata.
Bayan zuwa Matasa wajen Sarki Tsafi, da kansa yazo duba Naila har ya faɗi wasu maganganun da Kaka tayi watsi da su nan take.
★washe gari Matasan Yankin suka yanke shawarar fita naimo Malamin da zai yiwa Naila magani a Yankin gabashin da ake ce yake ko kuma ya basu maganin su kawomata.
Kaka da tana dama da ta hanasu domin ko sun karɓo bazata iya yiwa Naila amfani da shi ba, saboda bata yarda da kowa ba.
Matasan Yankin mu su Goma sha uku, sun kwashe kwanaki huɗu a gabashin Yankin Tudu amma ba su samu Malamin ba, sai maganin da suka ƙarbo daga takwarorinsa.
Da hannu bibbiyu Kaka ta karɓi maganin su, tare da tarin godiya mai yawa. Sai dai tana karɓa ta zubashi a shara.
Sartaj ya fito yana rayuwarsa kamar kowa amma bayayin nisa da Gida a wayonsa kar wani ya yi mai wani mugun abu. Hanyar Gidan Kaka tuni ya zama haramiya a garesa.
Cikin watanni biyu Naila ta ƙanƙance ta tsotse ta dawo kamar ba ita ba idan Kaka ta kalleta sai ta fashe da Kuka tana cewa;
"Ba sai mun nemo mai warware mana sihiri ba, mai warware mana yana tare da mu, kuma In Shaa Allahu da ƙarfin mulkinsa sai kinga har jikokinki Naila"
idan Kaka ta faɗi haka Naila fuskarta da ta dawo ƴar ƙarama ta yamushe take kawarwa gefe tayi kukan da batasam iyakarsa ba.
Kaka bata gajiyawa wajen kaiwa Allah kukansu, dare da rana, Safiya da yammaci. Jinkirin samun sauƙin Naila bai sa Kaka ta karaya ba.
Taimako da ake basu ne ya farayin ƙasa, abincin ci ya fara gagararsu, yunwar da ya yi sauƙi a Yankin Tudu ya dawo sabo fil, amma duk da haka da zarar sun ci kasuwar Tukwanen Zinare Matasan Yankin zasu haɗowa Kaka kuɗi, haka ƴan uwan Mahaifin Naila, a wasu lokutan har da Kakanninta na wajen uwa.
Shawarar dawo da sana'ar Mahaifiyar Naila na ƙera kayan wasan Yara na lakar ƙasa Kaka ta yanke. Drivern da yake fita iyakar Yankin Tudu ta roƙi alfarma ya dinga kaita bakin tasha tana siyarwa idan tayi ciniki ta biyashi, tunda kullum sai yaje.
Kai tsaye ya nuna mata kyauta zai dinga kaita ya dawo da ita amma tana ganin barin Naila a gida ba zai zama matsala ba, mai zai hana ta dinga lulluɓeta suna tafiya tare? Da sauri Kaka ta amince domin itama fargabarta kenan yadda zata bar Naila ita kaɗai a Gida.
Ba ta naimi shawarar kowa ba, kwana biyu bayannan suka fara bin Driver zuwa Iyakar Yankin Tudu.
A gefe Naila take rakuɓewa, Kaka kuma matafiya take bi tana tallata musu su zo su siya kayan lakar da ta ƙera Fisabilillah. Cikin hukuncin Ubangiji, sai tausayin Kaka da tausayin yadda Naila ta koma ya sa mutane suka yi ta siya har da masu ba su kyautar kuɗi.
kullum ba sa dawowa Gida da rogawa sai ya ƙare. kuma Driver bai taɓa karɓar ko sisinsu ba.
Duk wannan wahalar da Kaka take sha haka take ƙara raba dare a zaune tana kaiwa Allah kuka, domin bata iya tsayuwa saboda shekaru da wahalar da take sha.
Ƴan uwan Mahaifin Naila sun kawo ƙorafin ta dinga barin Naila a Gida, amma ta nuna sam bata yarda ba, tunda suma ba zama sukeyi ba kowa nema yake fita, matansu kuma ba lallai su kula da ita ba.
A lokacin da suka cika sati shida da fara fita Iyakar Yankin Tudu, jirginsu Sufyan ya sauka. Ya dawo Yankin Tudu, Motocin Mahaifinsa ne suka je tarbarsa amma da yake gulmar halin da su Naila suke ciki ya je mai tun kafin ya iso, sai ya gwada zuwa inda suke zama, don kawai yayimusu izgilanci kafin ya wuce.
Lokacin da ya iso ɗan rumfar da suke zama Kaka tana can tallatawa matafiya kayansu Naila kuma tana rakuɓe da ruwan shan da Kaka ta bata a gefenta. Dariyarsa kawai Naila ta ji a kanta.
Kafin ya fara magana Cikin izgilanci;
"Naila korarriyar Ɗalibar da talauci ya hana iyayenta naima mata magani ta warke ta koma Makaranta, ba kina ganin zaluntarki mukayi ba, lokacin da muka yi miki gata muka kaiki Birnin Abyad muka baki makwanci. Amma saboda butulci don kawai ina karɓar kuɗin kitson da kike yi kika zaɓi tozartani, yanzu gashi Ni da ke waye yake ji a jikinsa, kalleki dan Allah."
Naila bata ɗago ba sai yawun da take ta tofawa ruwan hannuna kamar zautacciya.
Farar fuskarsa da ya ke matuƙar ji dashi ya shafa dai-dai satin Yankar da Ɗayyib ya yi masa da bai gama bajewa ba ya ƙara ce wa;
"Banso haukarki tasa bakya gane maganganuna ba, amma wannan yawun da kike tofarwa da adanawa kikayi wataƙila kya rage wannan yamutsewar da kikay..." Saukar ruwan har cikin bakinsa yasa ya kurma ihu haɗe da tsalle kamar ƙaramin Yaro kafin ka ce kwabo tuni Matafiya sun cika wajen, suna kallon Sufyan da yake ihun "Saliva! Saliva!!" Haɗe da waftar ruwan hannun mutane yana wanke fuskarsa da bakinsa.
Gudun abun kunya ba tare da bin ba'asi ba Fadawan Sarki Hammam suka jashi Mota. Abinda Sufyan bai sani ba maganar Naila ta koma kamar ta ƴan yara ba kowane yake Fuskantar ta ba, ko azabar ciwon ya tashi sai dai ta yi ta kuka bata iya bayani yadda za'a fuskanceta. Shiyasa Kaka bata wahalar da kanta wajen tambayar abinda ya faru ba ta koma wajen tallata kayanta, suma mutanen da suka taru kowa ya kama gabansa.
A hanyar su ta dawowa Naila tke yiwa Kaka kwatancen abinda ya faru. Dariyar da rabonta da yin irinsa har ta manta Kaka ta ƙyalƙyale da shi, har suka isa gida lokaci zuwa lokaci sai ta saki dariya.
A wannan dare Naila tasha azaba irin azabar da batasan yadda zata misaltashi ba, da taimakon addu'o'in da Kaka take tofamata barcin ya ɗauketa. Kafin wayewar gari ta ƙara fita hayyacinta, babu wanda hankalinsa bai tashi ba.
SUFYAN; har ya suka isa gida bai sanar da Fadawa abinda ya faru ba suma kuma ba su tambayesa ba sai sannu da suke ta jeromai.
Ya yi wanka ya fi sau biyar haka bakinsa ya wanke yafi a ƙirga. Da daddare bayan Sallar isha suka ɗauki hanyar Yankinsu Hindu Mahaifiyarsa shi da da ita.
A daren Malaman Hindu Suka turo jinnun da zasu matsawa Naila da zarar Sufyan ya zo da buƙatar komawarta tare da albishir ɗin samo Malamin gabashin da suke nema Su Kaka za su amince a mayar da aurensu.
Sufyan aka bawa maganin da Naila zata sha sihirin ya karye ya zura a aljihun bayan wandonsa.
Gaba ɗaya sai ya matsu gari ya yi haske domin a daren suka ƙara dawowa Yankin Tudu.
Da Safe ko wanka bai yi ba balle ya karyawa ya nufo Gidan Kaka da sunan duba jikin Naila kamar yadda suka tsara a daren bayan dawowarsu kafin zuwan su Ɗayyib. Babu wanda ya rakosa, fuskarsa a tsamke alamun dai ba'a son ransa zai zo ba.
Sallama ya yi Kaka da batasan shi ba ne ta basa izinin shigowa.
A tsakar gida ya samu Kaka ƙannen Mahaifin Naila su na ɗaki tare da ita kowa ya na tofamata duk addu'ar da ta zo bakinsa.
Kaka tana ganinsa ta dakata daga hura wutar da takeyi. Cikin ladabi kamar gaske ya tsugunna yana gaisheta. Kafin ya ɗago Kaka ta rarumo ƙaton iccen da ya ke ci da wuta ta nufesa. Sufyan ya na hangota ya yunƙura ya miƙe a guje, garin wannan yunƙurawa Maganin bayan aljihunsa da aka basa tun daren jiya baiyi wanka ba kuma bai cire kayan ba, dama kuma aljihun bawani zurfi ne da shi ba ya faɗo ƙasa ba tare da ya ankara ba.
Ƙur Kaka take kallon magananin, kafin ta yi Bismillah ta na yunƙurin kai hannunta.
Muryar mutum taji a bayanta.....✍🏻
[7/29, 10:01 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥
NAFISA ALIYU SASAAL
Page 23
Da hanzari Kaka ta ɗauke ƙullin maganin ta wurgashi kwanon gefenta.
Yayyan Mahaifin Naila ne suke yunƙurin fitowa. Sallama su kayi mata, tare da alƙawarin kawo wani malamin ya ƙara duba jikin Naila. Su na fita Kaka ta sauke ajiyar zuciya, ba ta koma ɗakin ba tasa mayafi ta lalluɓe jikinta sai gidan Mallam.
Mallam
Juya maganin yake yi a hannunsa fuskarsa da yalwataccen murmushi ya ce "Tabbas! Allah ba Ya barci, sun biyota har gida sun shayar da ita sihiri, Allah kuma Ya ƙaddara su zasu ƙara biyota gida da makarin sihirin." Kaka da ke ta zare ido alamun bata fahimta ba domin ta ɗauka wani bala'in Sufyan ya ƙara kawo musu. Dalla-dalla Mallam ya yi mata bayani.
Ko
Cikin kuka Kaka takai
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 15