ya bar gidan Salman bai ce komai
Da Ɗayyib ya kaiwa Sarki Hammam labarin Tukwanen da Salman ya ƙera, Umarni Sarki Hammam ya bawa Fadawansa su bi layi-layi suyi shelar Bayyanar Salman a matsayin mai koyar da Tukwanen Zinare sak irinna Marigayi Abduh Dhahab.
A yammacin ranar suka cika umarninsa,
Nan da nan farin ciki ya mamaye zuƙatan Mutanen Yankin, maimakon su godewa Allah su ƙara sanin amfanin Marigayi Abduh Dhahab a Yankinsu sai suka hau Sukarsa da ce wa;
"Allah Ya sa shima wannan ba irin Abduh Dhahab ba ne mai mugun zuciyar da zai yi sihirin da Kasuwar Tukwanen Zinaren zai ƙara rushewa idan bayanan" da ire-iren kalaman sukai ta sukar Marigayi Abduh Dhahab kenan.
Ba su tsagaitaba har sai da labari ya jewa Sarki Hammam. Da kakkausar Murya ya yi gargaɗin duk wanda yaƙara sukar Abduh Dhahab abisa son zuciyarsa to zai fuskanci hukunci mai tsanani.
Ba bu kunya mutanen Yankin suka cika gidan Abduh Dhahab, Yara da Manya, Maza da Mata Don koyan ƙera Tukwane.
ƊAYYIB
Da wani irin takaici yake kallon ɗansa Sufyan, ba don kalamansa suna yimasa daɗi ba ya cigaba da saurararsa.
"Baaba tayaya zan koyi ƙera Tukwane da wannan kyan nawa? Baabah ba ƙera Tukwane ne ya dace da Matashi kyakkyawa irina ba. Ni burina shine naje Babban Birni nayi Karatu mai zurfin da zan kawowa Yankina cigaba, amma ba koyan ƙera Tukwane ba gaskiya" Yaƙarasa faɗa yana yin ƙasa da kansa da suma baƙi mai laushi ke kwance luf a kai.
Tabbas! Ɗanshi Sufyan kyakkyawane amma idan aka haɗa kyansa da na Sulaim daya ƙare rayuwarsa wajen bautar ƙera Tukwane to tabbas Sufyan ɗin ba komai bane.
Da taushin Muryar da yake burin Sufyan ɗin ya fuskancesa har yagane abinda yake yimasa kwaɗayi ya ce;
"Sufyan Idan har Sulaim da Allah Ya yiwa baiwar kyau ninkin baninkin naka zai ƙare rayuwarsa wajen ƙera Tukwane bisa umarnin Mahaifinsa, to banga dalilin da zai hanaka bin nawa umarnin ba. Sana'a baya hana karatu sai dai ma ya taimaka wajen ragewa Iyayenka ɗawainiya kuma kai kanka sai ka fi jindaɗin kayiwa kanka abu batare da ka jira an ɓata maka lokaci ba. Kaje kayi shawara da Mahaifiyarka amma kasani idan har ka saɓawa umarnina to babu ko sisina a harkar neman Iliminka." Ɗayyib ya na gama faɗa ya miƙe ya bar wajen.
Sufyan ba a iya Cikin zuciyarsa yake jin raɗaɗi kalaman Mahaifinsa ba har a kan fuskarsa.
Yaushe labarin kyan Sulaim zai gushe a zuƙantan mutanen Yankin. Ya na son ace yana da kyau duk da yayi imanin shi ɗin kyakkyawane, don matan Yankinsu da na maƙotan Yankinsu har so suke yi yayi musu magana. Amma duk wannan yabon kyan nasa da sukeyi da zarar hirar Sulaim ya ratso sai su hau ƙodashi da faɗin da Sulaim ya girma a raye to da babu wani Matashin da zai kamosa a kyau kaf faɗin Yanki, a wasu lokutan ma sai su ce har da maƙotan Yankunansu, duk ranar da irin haka ta ratso a gabansa ko labari yazo kunnensa yini yakeyi yana kallon ƙaton madubin Gidansu.
Hindu Mahaifiyarsa mai taya ɓera ɓari kullum ƙara zugasa take yi da cewa; "ba wai su na zuzuta kyan Sulaim ba ne don dagaske ya na kyan ba, sai don Tukwanen Zinaren da Mahaifinsa ya ƙirƙirowa Yankin, idan shima yaje Babban Birni Ya yi karatu mai zurfin da kaf faɗin Yankin ba bu mai kwatankwacinsa to ba shakka shima zai zama abin kambabawa, kar ya kuskura ya yarda da batun Sana'ar da Mahaifinsa ya jima yana burin ya yi, idan ba haka ba Sulaim shi zai cigaba da zama Saurayi mafi kyau a Yankin duk da baya raye, idan ma ya lura sun mayar da labarin kyan Sulaim kamar wani Tarihin da suke kambawawa. musamman ga waɗanda ba su sanshi ba" har alƙawarin auren gata tayimai da wacce zata bauta mai kamar Sarki idan har ya cikamata burinta na zuwa Babban Birni karatu.
Waɗanan huɗubobin da su Sufyan yake kwana kuma yake tashi.
A ɓangaren Mutanen Yankin ma su koyan ƙera Tukwane a wajen Salman sosai suka nuna jajircewarsu da farko, amma da tafiya tai tafiya sai suka fara nuna gajiyawarsu har sai da Salman ya zaburar da su da kalaman asalin wanda ya ƙirƙiri Tukwanen;
"Ba a lokacin da muka shuka iri, zamu girbi amfaninsa ba dole sai munjira kuma munyi haƙuri tare da yin aiki tuƙuru" waɗannan kalamai na Salman baƙaramin tsoratar da Mutanen Yankin ya yi ba, musamman ga waɗanda sukayiwa Abduh Dhahab farin sani. Tsoron kar su wayi gari wata rana su ga babu Salman don sun fi alaƙanta shi da aljali saboda kalamansa masu kamaceceniya da Abduh Dhahab, sai suka ƙara zage damtse.
Labarin kamaceceniyar kalaman Salman da Abduh Dhahab dayake yawo a gari har kunnen Naila da Kakarta. Naila data kasa samun sukuni a sace ta tafi Gidan ba tare da sanin Kakarta ba.
Sai da ta yi zuwa har biyu amma ta kasa shiga sai dai ta laɓe tana Kallonsa.
A ranar zuwanta na uku Salman ya kamata. Har cikin gidan ya riƙo hannunta ya shigo da ita.
"Maiyasa kullum kike zuwa ki maƙale kina kallona, mai kike nema?"
Salman ya tambayeta yana kallon cikin idonta.
Murya na rawa Naila ta ce "inaso nasan labarinka, inaji a jikina kamar Kanada alaƙa da su Sulaim, shin dagaske Sulaim yaƙone bazai ƙara dawowa ba?"
Kamar wanda ya ke son haddace halittun fuskarta haka Salman yake kallonta kafin ya ce;
" Ki je nan da Sati biyu ki dawo zan baki labari" ya ƙarasa faɗa ya na turata waje haɗe da kullo ƙofar Gidan.
Daga wannan rana Naila ta fara lissafin kwanakin da Salman ya ɗebarmata ba tare da sanin Kakarta ba.
A ɓangaren Mahaifiyar Naila tun bayan komawarta Yankinsu, zumuncin da dama can akwai shi tsakaninta da Mairam Matar Abduh Dhahab ya ƙara ƙarfi kullum ita take kula da Mairam a gidan take wuni sai dare take dawowa gida. Mairam tana samun sauƙi amma kullum a cikin kuka take ba magana.
Ranar da ta buɗi baki ta tambayi Ruwa, gidan ruɗewa sukayi da farin ciki ba iya su kaɗai ba har mutanen Yankin da labari ya je wa. Murnar fara maganar Mairam kaɗan-kaɗan yasa Mahaifiyar Naila yanke shawarar kwana a gidan, acewarta " yau kwana zamu yi muna hira" ta ƙarasa faɗa tana dariya.
Babu zato babu tsammani
A daren ranar aka kawo mummunar harin da ya faɗa kan Mahaifiyar Naila.
★washe gari da Sassafe Jama'ar Yankin suka kewaye gidan.
kuka mai raɗaɗi da ciwon gaske Kakannin Naila suka ƙanƙanme juna su na yi, lokacin da sukayi ido biyu da gawar ƴarsu. Ga shi Mairam da Mahaifanta sun gudu, tun Asuba..
Bayan an kimtsa gawar Mahaifiyar Naila kafin a kaita, Mahaifinta shi da Mutanen Yankinsa sukai gangami har Fadar Sarki Hammam, don suna kyautata zaton fara maganar Mairam ne yasa suka zo kasheta don karta faɗi abinda ta sani tsautsayi ya faɗa kan ta su ƴar.
Bayan sun samu shiga Daular Sarki Hammam maganganun ma su nauyi a harshe da raɗaɗi a zuciya Kakan Naila da mutanen Yankinsa suka fara zazzagewa Sarki Hammam da Muƙarrabansa. Zafin kalamansu dayake nuna cin fuska ƙarara ga Sarki Hammam yasa Fadawansa nufarsu da manyan bulalai.
Sarki Hammam dakatar da su ya yi, sannan ya yi wa Kakan Naila alƙawarin yin adalci matsawar ya bincika ya gano dagaske da hannun Mutanen Yankinsa akan kisan gillar da akayiwa Ƴarsu to zai hukuntasu dai-dai da abinda suka aikata.
Da wannan yarjejeniyar Kakan Naila da mutanensa suka bar Yankin, ko kallon Naila dake kuka kamar ranta zai fita basu yi ba.
Su na tafiya Naila da Kakarta suka shirya suka nufi Yankin.
Abun takaici bayan isarsu ko wajen zama ba'a basu ba, a cikin bainar jama'a, Kakanninta suka ce sun yafe ta, babu su babu ita, kuma karsu ƙara ganin ƙafarta a Yankinsu.
Naila tana kuka suka dawo Yankin Tudu.
A yammacin ranar sai da Sarkin Yankinsu Kakannin Naila na wajen Uwa, yaje har Yankin Tudu duk dai akan kisan gillar Mahaifiyar Naila, alƙawarin da Sarki Hammam ya yiwa Kakan Naila shi yaƙara yiwa Sarkin su.
Bayan Sarkin su ya dawo ya tattauna da Kakan Naila. A take Kakan Naila ya yafewa Iyayen Mairam tunda tafiyar tasu shine nutsuwar su da na Mutanen Yankin gaba ɗaya.
Naila bayan sun koma Gida kafin dare ya yi zazzaɓi mai zafin gaske ya rufe ta har bata gani da kyau.
A haka tasha jinyar da tayi sati Uku a kwance. Bayan ta wartsake ta tuna alƙawarinta da Salman sai dai babu damar zuwa saboda shirye-shirye bikin sake buɗe Kasuwar Tukwanen ZINARE, da za'ayi washe gari.
A ɓangaren Salman tuni ya manta da batunsa da Naila ya cigaba da abinda ya kawosa.
A daren washe garin da za'a buɗe Kasuwar Tukwanen Zinare, Sarki Hammam ya gayyacesa cin abinci..
Salman ya samu Tarba mai kyau daga Sarki Hammam, bayan sun kammala cin abinci, Sarki Hammam ya buƙaci tattaunawar sirri da shi game da shugabancin kasuwar Tukwanen Zinare.
Sarki Hammam da kansa ya faɗi sunan wanda yakeso ya zama Shugaban Kasuwar da kuma Mataimakinsa. Salman bai musa ba, shi dama aikinsa koyar da Tukwane kuma ya yi ya gama.
Sai dare sosai ya dawo Gida.
★washe gari kowa na Yankin bakinsa a washe, saboda dawowar Kasuwar Tukwanen Zinare babban nasara ne gare su baki ɗaya.
Bayan anci ansha Salman ya fara jawabi;
Bayan ya yi godiya ga Allah ya ɗora da jawabin godiya da kuma muhimmancin sana'ar da suka koya.
Can murnar kowa ya tsaya lokacin da Salman yake ƙoƙarin sanar da Shugaban Kasuwar Tukwanen ZINARE. Kowa burinsa ace shine ko wani nasa ne.
A bisa tattaunawar da Salman ya yi da Sarki Hammam bayan sun gama cin liyafar daya gayyacesa a daren jiya, ya sanar da ƊAYYIB a matsayin shugaba DATTIJO JUNAID kuma mataimakinsa.
Hayaniya ne ya ɓarke wasu suna ganin Dittijo Junaid da baya iya magana bai cancanci ya zama Mataimakin Ɗayyib ba, wa su kuma daga Ɗayyib har Dattijo Junaid ɗin duk basa so. A haka taro ya watse wasun su rai a ƙuntace da alwashi kala-kala.
Salman tare da Dattijo Junaid da Ɗayyib, gidan Abduh Dhahab dayake a matsayin Masauƙin suka wuce don yin bankwana saboda washe gari zai koma ƙasar su.
Sun shafe awanni suna tattaunawa kafin dukkan su su miƙe suna ƙarayin musabaha. Dai-dai lokacin da suke yunƙurin fitowa sukaji ana kwaɗa sallama haɗe da ɗan bubbuga Gidan.
Tare suka fito Salman ya buɗe ƙofa, kafin ya ankara aka fara sararsa ta ko ina...
Kamar dai Shekarun baya lokacin su Abduh babu wanda ya leƙo, duk da anajin kururuwarsu✍🏻
09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥 ZINARE 🔥
SASAAL
05
★washe gari da dukuku Maƙotan da suka ji kururuwarsu suka kai koken sun ji ihu a gidan Marigayi Abduh Dhahab jiya da daddare.
Sarki Hammam a kiɗime ya miƙe shi da Muƙarrabansa suka nufi gidan Abduh.
Kafin gari ya ƙarasa haske labari ya karaɗe ko ina.
Kafatanin Mutanen Yankin Tudu ne suka yiwa Gidan Marigayi Abduh Dhahab zobe, kowannen su zuciyarsa cike da tsoro da wani fargaba mai girma gaske. Yunƙurin faɗar gaskiya a Yankinsu ko kawo wani cigaba ya zama babban musibar da Mutum zai iya rasa ransa a kai.
A cikin Gidan Marigayi Abduh Dhahab Gawar Salman ne a yashe, ya yi kacha-kacha cikin jini, sai Dattijo Junaid da shima idonsa ɗaya yake a tsiyaye bayan raunuka marasa kyan ganin dayake jikinsa. Haka Ɗayyib shima wuƙa ne soke a gefen cikinsa sai raunukan da ba'a rasa ba.
Sarki Hammam kansa ya ɗaga sama, sai da ya tabbatar ya shanye ƙwallar da ya yiwa ganinsa yana sannan ya ɗurkusa a gaban Gawar Salman.
Baƙin cikin da yake ji bai tsaya a iya cikin zuciyarsa ba har saman fuskarsa, yana son Salman sama da son da ya yi wa Abduh, saboda ya taimaki Mutanensa a lokacin da suke da tsananin bukata, amma wannan baisa sun rangwantamai ba har sai da suka kaishi ƙasa kamar yanda su ka kai Abduh. Fari ƙal ɗin hannunsa da ya ɗan fara yamushewar tsufa yasa ya shafi fuskar Salman, kafin ya miƙe don a samu damar fitar da su daga Gidan.
Fito da Salman a luluɓe har kaa, saɓanin ragowar yasa zuciyar kowa ƙara karyewa. Banda koke-koken muryoyi daban-daban ba bu abin yake tashi a ƙofar Gidan.
To ko dai Tukwanen Zinaren ne ba'a so a Yankinsu tunda shine sana'ar da yafi kowawa Yankinsu kuɗin shiga? Wanene yake musu wannan Ta'addacin a Yanki? Daga Abduh Dhahab har Salman dukkan su maƙera ne, ma su kamaceceniya a ɗabi'u har ma da wasu maganganunsu. kenan anfiso su cigaba da rayuwa cikin azaba da ƙangin Talauci? Tambayar da Mutanen Yankin Tudu suke ta yiwa junansu kenan.
Kamar shekarun baya da suka shuɗe, Daular Sarki Hammam aka wuce da Gawar Salman anan aka Sallacesa, bayan an miƙa su Dattijo Junaid da Ɗayyib Asibitin da babu likitocin azo a gani.
Fargaba mai gusar da nutsuwa ne ya dabaibaye zuciya Sarki Hammam, dalilin haka yasa Jininsa ya hau dole aka buƙaci Likita daga Babbar Birnin Abyad don kula da shi da su Ɗayyib.
Kafatanin Mazan Yankin Yaransu da Manyansu ne suka tafi kai Salman makwancinsa cikin su har da Manya masu faɗa aji a fadar Sarki Hammam.
Daf da zasu shiga Maƙabarta aka sani harbin bindigar da yasa mutane dayawa darewa . Ma su ɗauke da Gawar Salman ma ajjiyesa su ka yi sai dai su ba su gudu ba, su na dai tsaitsaye. Ƙarar Harbin da'asaki sau biyu a jere ne yasa suma suka tarwatse aka bar Iya Gawar Salman.
Mota mai tudu baƙi mai tsananin sheƙin dake bayyana girman dukiyar da'a zuba kafin mallakarsane ya yi parking a gefen Gawar Salman.
Maza majiya ƙarfine suka fara fitowa ɗaya bayan ɗaya har su uku a jere kafin fitowar na huɗunsu.
Fitowar na huɗunsu ne yasa Bashar kawun Ɗayyib kuma mai faɗa aji a Masauratar Yankin Tudu da ke laɓe a ɓoyarsa shi kaɗai kuma ya sawa zuciyarsa dole sai ya ga duk abinda zai faru zare dukka girman fararen manyan idanuwansa na Usul ɗin Mutanen Yankin Tudu. Fitsari mai ɗumin gaske na biyo jikinsa, a take ya ji idanunsa na ƙyaƙyayin azaba. Amma duk da haka taurin zuciya, da kafawa duk abinda yasa a gaba ƙahon zuƙa sai yaga bayansa yasa ya ƙi kulle idanuwansa kamar yadda ragowar su ka yi a maɓoyarsu.
Ba bu rahama a fuskar na huɗunsu da yafi su girma da tsaho, hannu ya sa ya ɗauke Salman a makara, yanayin yanda ya ɗagashi na bayyana rauninsa. dasauri ragowar ukun suka buɗemasa bayan mota ya shimfiɗesa.
Harbi suka ƙara saki amma duk da haka fararen idanuwan Bashar da suka koma jajaye na tsaye ƙyam a kansu. Yunƙurin shigar su Mota yasa ya ɗan lumshe idanuwansa na seconni ko zai samu sassaucin zugin azabar da idon yake mai.
Ɓude idanuwan da Bashar zai yi ya tsinci Mutum biyu a gabansa, dama ba bu wani tazara a tsakaninsu. Ya kasa ihu saboda duniyar fargabar daya tsinci kansa a ciki. Kamar Kayan wanki haka suka ɗebesa har Gaban mutumin da Kallonsa daga nesa kaɗai ya sa shi sakin fitsari. Ƙasa Bashar ya yi da kanshi jikin da dama can lallaɓawa yake yi saboda yawan shekaru ya fara karkarwa. Ɗago shi ya yi suna kallon tsakiyar idanuwan juna, idon Bashar kamar an tsiyaya jini tsabar jan da sukayi. Ƙasa Bashar yaƙarayi da kanshi saboda gudawan daya tahowa mai, ba ya kuma burin ya ƙara kallon ko da fuskarshi ne balle cikin idanuwansa saboda tsoro. Bashar bai gama saƙe-saƙen da yake yi ba yaji ya ƙara ɗago Kanshi. Da ƙarfi ragowar suka buɗemai baki. Gurnanin azabar gaske Bashar ya saki lokacin da na huɗunsu ya ciremai harshe kwatankwacin yadda aka yanke na Dattijo Junaid. Watsar da shi su kayi suka faɗa Mota kamar iska haka suka bar wajen da Yankin Tudu gaba ɗaya.
Gurnanin azabar da Bashar yake yi babu wanda bai jiyosa ba a maɓoyarsa ba, amma tsoro ya hana kowa fitowa duk da Matsayin da Bashar ya ke da shi a Daular Masarautarsu.
A ɓangaren Sarki Hammam duk bai san wainar da'ake toyawa ba saboda barcin daya ɗaukeshi, suma waɗanda suka rage a Masarautar laƙwas su kayi kamar basusan abinda yake faruwa ba, tunda wanda zai tilasta mu su fita kai agajin bai san ma anayi ba.
Sai da kowa ya yi hour biyu da ɗoriya a maɓoyarsa sannan duk su ka firfito, zuwa lokacin tuni Bashar ya yi suman azaba. Ko takan inda harshen da suka yanke yake basu bi ba suka saɓashi a guje sai Asibiti. Daga Asibiti kowa ya silale ya yi Gida haɗe da kulle ko ina.
Har aka kwana aka wuni Yankin Tudu tsit kamar babu kowa.
A ɓangaren Naila tayi kukan mutuwar Salman, har sai da ya saukar mata da ciwon kai mai nauyin gaske, gashi babu damar fita kaita Asibiti saboda tsoro. Haka Kakarta tayi ta yimata jiƙe-jiƙe har zuwa washe garin da ta ji ɗan dama-dama.
Da wani kallo ta kalli Kakarta murya na rawa ta ce;
"Maiyasa ake kashe kowa haka, shin su Abduh da aka kashe basu da dangine? su waye danginsa maiyasa ba su ɗauki mataki ba? da sun ɗauki mataki da yanzu ba akashe Salman ba, Kaka su waye dangin Abduh Dhahab? maiyasa suka wofintar da al'amuransa a haka?"
Kaka murmushi ta yi tana shafa kan Naila ta ce;
"Ki bari ki ƙarasa warwarewa In Sha Allahu zan baki labari"
SARKI HAMMAM
★washe gari da Sarki Hammam ya farfaɗo ya samu labarin abin ya faru. A gaggauce ya yace a shirya mishi zuwa ganin Bashar.
Lokacin da ya isa Asibiti da ake yiwa su Ɗayyib, Dattijo Junaid da Bashar maganin gargajiya kafin ya shiga Ɗakin da Bashar yake saƙon Dattijo Junaid ya riskeshi na;
" idan ya shigo yane raye, a faɗamasa yazo gareshi yana da saƙo."
Sarki Hammam ya na jin saƙon Dattijo Junaid ya fasa shiga Ɗakin Bashar ya wuce na Dattijo Junaid bayan ya dakatar da kowa daga bin bayansa.
Kallon yadda Dattijo Junaid ya koma kaɗai wani abin fargaba ne. Bayan ya yi mai ya ya jiki ya naimi waje ya zauna.
Alama da salon maganar kuramen da Dattijo Junaid ya saba yakeyiwa Sarki Hammam bayani, cikin ikon Allah, Ubangiji ya bawa Dattijo Junaid ikon yin bayani kamar da bakinsa yake magana tsabar yanda Sarki Hammam ya ke fahimtarsa.
Bayan ya gama bayani Hannunsa Sarki Hammam ya kamo. Junaid Amininsa ne tun suna Yara amma banbancin Gidan da suka fito ne ya nisanta Amintakarsu dole, Bayan ya zama Sarki Junaid ya dawo ƙarƙashinshi Bashar ya maye gurbinsa na Amini.
Sarki Hammam Ya na cikin wannan tunanin Allah Ya amshi ran Dattijo Junaid. Kuka ya zauna yi kamar ƙaramin Yaro. Ya yarda Bawa baya mutuwa har sai idan lokacin da Ubangiji ya ɗebarmasa sun cika, banda haka tayaya Dattijo Junaid zai yi ƙarfin zuciyar rayuwa bayan yana kallon ajalinsa a kusa dashi ko da yaushe kuma ya ja bakinsa ya yi shiru?.
Mutuwar Dattijo Junaid da hasken da Sarki Hammam ya samu dangane da badaƙalar dake addabar Yankinsa a ɓoye bai tsaya a iya hawan jininsa ba har jinya ya kwanta, don dole aka fitar dashi Babban Birni Abyad.
Mutuwar Dattijo Junaid da abinda ya samu Bashar ya kasa hankalin mutanen Yankin kashi-kashi. Wa su sun yarda waɗanda suka zo a Baƙin Mota sune suke yiwa Yankinsu aika-aika, wa su kuma suna ganin sam ba haka bane idan hakane aiba Bashar zasuyiwa haka ba kawai dai Ƴan uwan Salman ne suka zo ɗaukar fansa, to amma ta ya ya akayi suka san mutuwarsa? tunda babu komai na Salman da ba'a bincika ba amma an kasa gano daga inda yake.
Daga wannan lokacin baƙin jininsu sai ya ragu a zuƙatan Maƙotan Yankinsu saboda da yawa sunfi yarda masu Baƙin Mota ne suke yiwa Yankin ta'asa tuntuni, ba wai Mutanen cikin Yankinba
Bayan wani lokaci, Sarki Hammam ya dawo daga Babban Birni Abyad, Bashar shima ya samu sauƙi.
A Fadar Sarki Hammam aka gayyato ƙwararrun ma su zane don su zana wanda Bashar ya haukace yana ta kwatance har da kaisu gidan Abduh Dhahab, duk wannan kwatancen na shi ba bu wanda ya ɗauki hasken komai Sai Sarki Hammam dashi ƙadai yasan wanda Bashar yake nufi daga bayanin da Marigayi Dattijo Junaid ya yi masa. Shara da tsaho yake ta kwatantawa, banda wannan ya kasa siffanta komai. Sai da ƙyar ya fara zayyano siffar wanda sam babu ko mai kamanninsa a Yankin. Dole yana ji yana gani masu zane sukayi tafiyarsu.
Kwanaki bayannan Sarki Hammam yasa atara mishi mutanen Yankin don zaɓar sabon Shugaban Kasuwar Tukwanen ZINARE da Mataimakinsa tun da har lokacin Ɗayyib bai samu sauƙi ba..
41 3080: 🔥ZINARE🔥
SASAAL
Arewabooks@sasaal
06
Kamar ko da yaushe Layi-layi aka bi ana shelar Sarki Hammam ya na buƙatar ganin Mazan Yankin a Masarautarsa..
Kafin ka ce me, kafatanin Magidanta Yankin sun cika harabar Masarautar.
Bayan an ansanar da su saƙon Sarki Hammam, na shin akwai Mai son zama Shugaban Kasuwar Tukwanen Zinare a cikinsu? Ba bu wanda ya ɗaga hannu, ɗaya bayan ɗaya suka dinga sulalewa kafin Minti Talatin filin ya dawo fayau babu kowa, dalili; kowa tsoro yake ji, kar ya karɓi Shugabancin shima a biyosa har gida akashe shi.
SARKI HAMMAM;
Da labarin guduwar Mutanen Yankin ya riskesa ajiyar zuciya ya sauke. Shikenan! Maƙiya Yankin sunyi nasara akan Mutanensa, dama tsoro da gudun mutuwa akeson dasa musu, su dawwama yin rayuwa cikin Talauci, da ƙin faɗar gaskiya ko da za'a kashe na su a gabansu saboda su tsira da rayukansu, duk da mutuwar dai da aka dasa musu tsoronta suke gudunta zai riskesu idan kwanansu ya ƙare.
Kansa ya dafe, ya na jin raɗaɗi a cikin zuciyarsa kenan Mutanen Yankinsa sun gwammace ko shekara nawa Ɗayyib zai yi a kwance zasu jirashi ya jagorance su, idan ya ga zai iya idan kuma ba zai iya ba su haƙura da kasuwar gaba ɗaya. "Kaico" Sarki Hammam ya faɗa a sarari.
★Kasa jurewa ya yi, washe gari ya ƙarasawa ayi shelan;
"shin da wanda ya ke so ya zama Mataimakin Ɗayyib idan ya warke?" Nan ma babu wanda ya amsa tsit sukayi a cikin Gidajensu kamar ruwa ya cinyesu.
Da aka ƙara sanar masa babu wanda ya daki ƙirji ya fito, Gaba ɗaya sai ya rasa abinda yakemasa daɗi, ba shi da wanda ya yarda da shi a kusa da shi balle ya tattauna damuwarsa da shi, saboda masu aikata ɓarnar a kusa da shi suke ta yanda ba shi da yadda zaiyi ya yakicesu, kuma ko da ya faɗi ma su aikata ɓarnar kai tsaye babu wanda zai yarda da shi.
Ya zama dole ya canza salon dabarar mulkinsa shima, don tsirar da Mutanen Yankinsa.
Bayan wani lokaci...
A ɓangaren Ɗayyib ba laifi yanata samun sauƙi saboda ƙwararrun likitocin da suke shigowa dubashi akai-akai, don da farko a Yankin Tudu ya yi ta jinya, sai dai rashin likitoci ya sa aka fitar da shi wani gari da yake kusa da Babban Birnin Abyad.
A cikin watanni ya warke tsaf kamar bai taɓa jinyaba. Da tsananin farin ciki shi da Iyalinsa suka ɗauki hanyar Yankin Tudu.
A ranar da ya dawo Gida bayan ya huta Sashen Bashar da yake a matsayin ƙanin Mahaifinsa Jalal uwa ɗaya uba ɗaya ya nufa.
BASHAR
Lokacin ya yi ido biyu da Ɗayyib da sauri ya rungumesa ya na yi mai kwataccen ya ya jiki?
Amsawa Ɗayyib ya yi haɗe da jajantamai abinda ya sameshi.
Bayan sun ƙara gaisawa, Ɗayyib ya tambayi Bashar garin ya ya haka tafaru? Da kwatancen Gidan Abduh Dhahab ya fara.
Ɗayyib mutum ne mai kaifin Basira da saurin Fahimta, wannan dalilin ya sa kai tsaye ya fahimci dole wanda ya gutsewar Bashar harshe yana da alaƙa da Gidan Abduh Dhahab.
"Sulaim ka gani, ko Abduh ko Mairam?" Ɗayyib ya tambayeshi a nutse. Shiru Bashar ya yi takaicin Ɗayyib na kamasa tayaya zai iya faɗamai bayan ya ambaci sunayen su dukka a lokaci ɗaya? Ganin ya yi shiru kamar mai tunanin yasa Ɗayyib umartar a nemo mai zane....
Bayan mai Zane ya iso..
Fuskar Abduh ya fara zanawa da kwatancen da Ɗayyib ya ke yi mai, Bashar ya ce ba shi bane an zana Sulaim da Mairam suma ya ce dukka ba su bane.
Bashar miƙewa ya yi yana kwatanta tsaho da shara, har ya gama kwatanta iyakacin abinda zai kwatanta babu
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 15