Su na ina!" A wannan karon Sulaim bai saki ƙara ba, sai zaburar dayayi ya soke shi da ƙarfen da ya soke a gefen ƙugunsa a dai-dai saman kafaɗarsa tunda ya na da tsahon ƙafa.
"yaushe Mahaifina ya gama girbar amfanin Irin da ya sha wahala da azabar shekarun shukawa, da har zakazo karɓan na ka kason!?" Sulaim ya tambayesa da sansanyar muryarsa da azaba ta sa ya ƙara yaushi.
Sulaim Bai gama sauke hannunsa da haɗiye yawun kalamansa ba ya ƙara yankarmai gefen kafaɗarsa na hagu haɗe da fesar da hucin haushin kalaman da Sulaim ɗin ya jefesa da shi. Shima Sulaim bai zube ƙasa gaba ɗaya ba sai ya da ya zaro ƙarfen da ya sokamai a kafaɗa ya ƙara kafamai a tsakiyar cinyarsa da dukka ƙarfin daya rage mai. Kusan lokaci ɗaya su ka zube ƙasa. Kowannen su ya na sauke numfarfashin azaba ga jinin da ya ke bin jikin kowanne su.
Kasa jurewa Matar Mahaifin Sulaim da ke laɓe ta yi ta fito ɗaga ɗakinta don tsaf ta haddace muryar wanda ya shigo musu gida.
Da kuka ta fito ta na ba shi haƙuri. Wanda ya yanki ya na ganin fitowarta ya miƙe da sauri kamar ba shi ba, saboda hasashen mallakar dukiyar Tukwanen Zinaren da Abduh Dhahab ya ɗauki tsahon shekaru ya na bautar tarawa ba tare da ya bari ko shi kansa ya mora ba.
Itama tambaya ya titsiyeta da shi ya na rintse idon azabar da ya ke ji, "a ina Abduh Dhahab ya ajjiye kuɗin Tukwanen Zinaren da ya siyarwa Turawan da suka zo? kuma a ina ya ke ɓoye dukka dukiyarsa ki faɗamin na ƙyaleki a raye?" Shiru ta yi ba ta ce masa komai ba, sai kallon bayansa da ya ga ta na yi. Bai kawo komai ba a ransa ya ɗauka halin da Sulaim yake ciki ta ke kallo.
Ganin bazata faɗa ba yasa ya kai mata hauri ta bugi bango da ɗaya ƙafarsa mai lafiya. Ya na juyowa inda ya bar Sulaim yaga ba bu shi a wajen. Kenan Abduh Dhahab yana gidan? maiyasa bai fara bincika ɗakunan Gidan ba tukunna?
"Abduh!!!!" ya faɗa da ɗan ƙarfi yana zare dukka girman idanuwansa da su ka yi jajir
Pito ya yi, abokannan rakiyarsa da suka maƙale suna jiran umarninsa suka shigo Gidan. Biyu zama su ka yi ɗauremasa ciwukan da Sulaim ya ji mai, bayan sun zare ƙarfen cinyarsa, ragowar kuma suka hau bincika gidan.
Sun samu Ɗakin Abduh Dhahab da duk amintakarsa da Mutum ba ya bari ya shiga, sun bincika amma babu ko sisi a ciki.
Hanyar da jinin Sulaim ya ɗiɗisa su ka dinga bi su na haskawa, har suka samu ta inda Abduh Dhahab da Sulaim suka bi suka bar gidan, ta ƙofar da ba su san da shi ba.
Zabura ya yi ya na haska ƙofar bayan da Abduh Dhahab ya bi har zuwa inda jinin ya tsaya. Dariya yaƙen azabar da ke nuƙurƙusarsa ya saki ya na kutsa kai cikin gidan bayan sun ɓalla ƙofar Moƙocinsa kuma Amininsa da suke kyautata zaton nan Abduh ya shiga.
Da matar gidan su ka ci karo tana salla a tsakar gida. Bai amsa tambayoyin da ta ke jero mu su na dalilin shigo mata gida kai tsaye ba ya ce:
"Sarah! Ina Mijinki ya ɓoye Abduh Dhahab da Ɗan shi? Asibiti ya kai shi, ko su na cikin Gidannan? kifaɗamin gaskiya ko na wulaƙantaki" ya ƙarasa faɗa ya na ƙare mata kallo ta hasken farin watan daya haske gidan.
Da sunan Ubangijin da take ambata ta yi jarumtar furta "Mallam ba ya gari, ya tafi Fansar Litattafai, Asibitin kuma sati ɗaya kenan ba a yi aiki a cikinsa ba"
dariya su ka bushe da shi don ko a ranar sun ga mijinta. Ƙasan Gidan ya haska ya na kai dubansa dai-dai wajen da Jinin da ya ɗiɗisa har zuwa inda ya tsaya.
Dai-dai inda Mallam ya ke ajjiye kekunan hawarsa har guda biyu jinin ya tsaya. Dariyar ƙeta ya sa kafin ya ce. "ashe Mallam mai Asibiti da zai fita da dukka kekunansa ya fita Fansar Litattafai kenan? Ki faɗa min wanene ya tuƙa ɗaya keken?" Kai ta girgiza haɗe da yin duk addu'ar dayazo bakinta.
"Wallahi kinji na rantse idan baki faɗamin gaskiya ba zan ƙona gidanan da ke da ƴaƴanki gaba ɗaya." kuka tasa ta na roƙonsa da magiya kala-kala.
Ganin ta na ɓata mu su lokaci ya sa ya ce a ƙona Gidan tunda taurin kai ne da ita. Ta na jin haka ta ce Abduh Dhahab ya zo da Ɗan shi amma sun tafi Asibiti. Dasauri ya ce: "ya zo da kuɗi?"
"Bansaniba amma dai yazo da buhu mai girma da abu a cik.." bai bari taƙarasa ba, su ka bar Gidan.
Ko da sukaje Asibitin Mallam, ba bu Abduh Dhahab da Sulaim kuma ba bu ko sisi sai Mallam da su ka samu yana ƙoƙarin dawowa Gida.
"A wani ɗakin ya ɓoye Abduh Dhahab da Ɗanshi da kuma dukiyar da ya ƙullo a buhu?" Suka tambayi Mallam.
Shiru Mallam ya yi kamar kurma. Sunfi minti 15 su na ta tambayarsa kafin ya basu amsar Abduh Dhahab yana cikin Asibitin da dukiyarshi.
"A wani sashe na Asibitin? kuma a wani ɗaki?" Su ka ƙara tambayarsa Tunda Asibitin ba laifi ya na da girma. Shiru ya yi yaƙi ba su amsa kuma ba bu inda ba su duba ba babu Abduh Dhahab kuma sun kasa gano shaidar ɗakin da zasu sameshi ga dai keken Mallam daya tuƙo a gefe jini duk ya ɓatashi. Kuma Mallam ya kafe Abduh Dhahab na cikin Asibitin da ɗanshi da dukiyarshi. Ganin kamar raina mu su hankali haɗe da son tona mu su asiri ya ke yi. Sai suka turashi cikin Asibitin su ka kulle.
A can gidan Mallam
Suna fita Matarsa ta tattara ƴaƴanta su ka nausa hanyar Yankinsu a cikin daren kamar yanda Mallam ya umarceta kafin ya zo ya samesu.
Bayan sun tura Mallam cikin Asibitin sun kulle, wuta suka saka, sannan suka ƙara dawowa gidan Abduh Dhahab suka yiwa Matarsa kashedi mai zafin da ya kai ga guntule mata ƴan yatsu biyu, tare da yashe duk wasu dukiya da suka samu a ɗakinta na tarin kuɗin la'adar da Abduh yake biyanta idan ta tayasu aiki.
★washe gari labarin gobarar Asibitin Mallam ya karaɗe Yankin, Da farko ba'a fahimci gawar su waye a ciki ba, sai da Surikin Mallam ya biyo jin ba'asi bayan isar Matar Mallam Yankinsu anan ya tarar da mummunar labari, ya kuma tabbatarwa da Mutanen Yankin su Mallam ne suka ƙone, da iyakacin hujjar da ƴarsa ta bashi.
Duk da a kwai waɗanda suka ɗan ji abinda ya faru a cikin daren, amma sukayi shiru su ka ƙi magana, kowa ya ja bakinsa ya tsuke, tunda matar Abduh Dhahab bata farfaɗo ba, tun cikin daren zuwa wayewar gari balle ta faɗi sunan waɗanna su ka aikata a ɗauki mataki a kansu, kamar yanda Sarki Hammam ya bayar da shela.
Gawar Mutum huɗun da aka zaro sun ƙone ƙurumus bakyan gani don babu fuskar wanda aka gane balle a banbance. Ɗayyib ya na kwance lulluɓe cikin abin rufa sai kuka da ihu ya ke yi jikinsa ya na rawa, haɗe da sabbatun su fito masa da Abokinsa Abduh Dhahab, wallahi bai yarda Abduh Dhahab ya mutu ba, wanene ya kashemasa Abduh Dhahab Aminin ƙwarai?
0
09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥
SASAAL
03
A fadar Sarkin Hammam aka sallaci gawarwakin da Sarki Hammam da kansa ya jagoranta. Kafatanin Mazan Yankin ne sukayiwa gawarwakin rakiya izuwa makwancin su. Kafin dawowar su Dangin Mahaifin Mairam (matar Abduh Dhahab) sun zo sun ɗauketa saboda gudun abinda zai biyo baya, haka Malik maiyiwa Abduh Dhahab hidimar shara duk safiya shima ana dawowa da ga kai su Abduh makwanci aka nemesu aka rasa shi da Iyayensa.
A wannan ranar kasuwar da Abduh Dhahab ya sha gwagwarmaya shekaru kafin kafuwarsa na siyar da Tukwane ma su Taken Tukwanen ZINARE don cigaban Yankinsa ya yi faɗuwar tasa da ba'a taɓa tunani ba.
Domin duk wanda ya zo ya ji mutuwar Abduh Dhahab ba ya iya tsayawa ya ke juyawa inda ya fito. Dubban mutanen Yankin sun tafka asarar abincin siyarwa da su ka dafa da sauraran kayan amfanin da suka sarrafa don siyarwa baƙin da suke shigowa.
Anya mutuwar Abduh Dhahab bazai kawowa yankin su Talauci mai ƙarfi da koma baya ba kuwa? tunda ta nan suke samun kuɗin shiga ta hanyar abubuwan da suke sarrafawa su siyarwa Baƙin da su ke shigowa, ga kuɗin hayar masauƙin da suke samu da ga wajen baƙin da suke zuwa daga nesa. Dukka wannan ya rushe kenan? Tambayar da Mutanen Yankin suke ta yiwa kansu kenan..
NAILA
Ta fi minti Talatin a tsaye a harabar Gidan su Sulaim ta na jiran fitowarsa, bayan tasha kukan daya ɓata Kyakkyawar Fuskarta da hawaye da majina. Don ita bata yarda Sulaim ya mutu ba.
Daƙyar Babanta ya janyeta shima na shi ran na suya.
Da Surukin Mallam zai koma Yankinsu Sarki Hammam ya umarcesa ida anyi Ukun su Mallam ya kawo masa Sarah ya na son yi mata tambayoyi, tunda Matar Abduh bata hayyacinta. Da "to" Surukin Mallam ya amsa amma har cikin zuciyarsa bayajin Sarah ɗiyarsa zata ƙara taka Yankin..
Da yammacin ranar aka binne su Abduh Dhahab, sai gaba ɗaya mutanen Yankin suka koma zancen asarar da suka tafka, ba tare da sun ƙarabi takan abinda ya yi makasudin ajalin Abduh Dhahab da Ɗansa har ma da Mallam ba. Wannan lamari ya yi matuƙar sosa ran Dajjito Junaid.
Junaid ɗaya daga cikin Dattawan Yankin ne, kuma na hannun daman Sarki Hammam, ba shi alaƙar Jini ko na dangantaka da su Abduh Dhahab.
★washe gari Dattijo Junaid tattaki ya yi har Yankin su Sarah Matar Mallam. Ya sameta a mawuyacin hali mai ban tausayi, iyayenta sun karramashi tare da bashi abin sha don jiƙa maƙoshi. Tambayar duniya Sarah taƙi faɗar waɗanda suka zo gidanta neman Mallam, ƙarshe da Dajjito Junaid ya matsa mata kuka ta fashe da shi raɗaɗin kisan gillar da akayiwa Mijinta na cigaba da sukarta. Ta yaya zata faɗa bayan tasan za su bibiyeta.
Har Rana ta yi Dattijo Junaid bai bar Gidan su Sarah ba. A kan idonshi Iyayen Sarah da ita kanta da ƴaƴanta suka fito da kayayyakin su don yi balaguro tunda sun san dole a bibiyi ƴarsu gudun kar ta faɗi gaskiyar abinda ta sani.
Hawaye Dajjito Junaid ya share ya na bin bayan su. Cikin taushin harshe da amon dake bayyana irin raɗaɗin dayake ji a ƙasar zuciyarsa ya ce;
"Sarah tunda bazaki bani ƙarin haske akan abinda ya faru ba, ki taimaka ki faɗamin inda Mallam yake samun taimakon inganta babban Asibitin mu, da kuma Makarantun ƴaƴamu na roƙeƙi" ya ƙarasa faɗa yana haɗa fararen hannayensa waje ɗaya alamar roƙo. Tsayawa Sarah ta yi zuciyarta na karyewa tsananin tausayin Abduh Dhahab da Sulaim na bijiromata. Sai da ta tattaro dukka jarumtar daya bata damar shanye kukan dake neman cin ƙarfin maganganun da takeson faɗa sannan ta ce;
"Abduh Dhahab shi ne wanda ya gina makarantu da Asibitin daya bawa Mallam amana bayan ya roƙi Mallam ya yi mishi alfarmar kar ya bari kowa ya sani har sai idan shi ya buƙaci hakan da kanshi. Ya ƙare rayuwarsa da Ɗansa wajen bauta muku da son ganin cigaban Yankinku, amma duk da haka sai da kukayi sanadiyar ajalinshi. Tir! da wannan Yanki na ku" ta ƙarasa faɗa tana fashewa da kuka haɗe da barin Dajjito Junaid tsaye da sakekken baki.
Dattijo Junaid Tafiya yakeyi da iya ƙarfinsa amma sai yake ganin kamar baya sauri, burinsa ya isa Yankinsa ya ba su labarin da zai dawo da su hayyacinsu su binkico shaiɗanin dayayi sanadiyar rushewar Yankin su.
Da Yammaci Dattijo Junaid ya iso Yankinsu da labarin alkhairin Abduh Dhahab,
Ba bu wanda ya yarda da shi, sai ma cewa da suke yi;
"Abduh Dhahab ɗin da yake mayen kuɗi ne, zai yarda ya bautawa Yankinsu da dukiya mai yawa irin wannan? Kawai ƙage da rashin son zaman lafiya Dajjito Junaid yake son kawowa Yankin su" ire-iren maganganun da sukai tayi kenan har da masu kwashewa Dattijo Junaid albarka.
★Duk da haka Dajjito Junaid bai gajiya ba washe gari ya ƙara ɗaukar harama ya na shela layi-layi.
"Ya ku mutanen Yankin Tudu! Ina jiyemuku ranar nadamar da zakuyi nan gaba da kuma talauci mai raɗaɗi da azabar da zai iya riskarku matsawar kukayi butulci baku tsaya tsayin daka wajen ganin an binciko waɗanda suka kashe Abduh Dhahab da Iyalinsa ba, lallai sakayya mai raɗaɗi yana nan zuwa garemu, matsawar kuka yofintar da zance na. Haƙiƙa nan gaba kowa a cikinmu zai ɗanɗana kuɗarsa, Wannan wahalar nake jiyemana mutanen Yankina"
Leƙosa sukeyi wa sun su na dariya tare da yin Allah wadai da kalamansa, su na cewa;
"ai mu Abduh Dhahab ya cuta, tunda dama sihiri ya yi wa Kasuwar Zinaren da idan ya mutu Kasuwar da ya gina shima zai mutu baza mu moraba, tsabar mugunta da ya shiryamana har Tukwanensa ya kwashe kaf ya siyarwa da Turawa mu kuma ya barmu da tafka asara" har ya gama Shelarsa ya wuce Fadar Sarki Hammam babu wanda ya ƙullasa.
Da Dajjito Junaid ya yi magana a fada Sarki Hammam, ansamu waɗanda hankalin su ya karkata kan anya labarin da Dattijo Junaid ya zo dashi ba gaskiya ba ne ba kuwa? Haka a ɓangaren Sarki Hammam ɗari bisa ɗari ya yarda da zancen Dajjito Junaid har ya bada tabbacin ƙara zurfafa binciken waɗanda suka aikata wannan mummunan aikin. Dama ya daɗe yana kokwanton waɗanda Mallam ya ce suke ɗaukar nauyin dukka ayyukan tun farkon buɗe Makarantun da Asibiti, da yanda ake biyan ma'aikatan jinya da malaman Makaranta albashi akan lokaci, da yanayin kulawar da ma'aikatan suke samu duk ba iri ɗaya bane da wanda suka samu gwamnati take ɗaukar nauyi.
Ragamar binciken komai Sarki Hammam ya miƙa a hannun Dattijo Junaid.
A wannan ranar da tsananin farin ciki Dajjito Junaid ya nufi Gida.
bai runtsa ba har sai da ya fara kamo bakin zaren abinda yake zargi.
A Yammacin wata Laraba ya shirya kaiwa Sarkin Hammam ziyara, don gabatar da shaidun da zai ƙara buɗe idon mutanen Yankin har su bashi goyon baya wanda ya yi dai-dai da cikar su Abduh Dhahab sati biyu a kaburburan su. Kafin ya buɗe gidanshi anrigasa buɗewa.
★washe gari, har rana ta fito Ba bu wanda yaji ɗuriyar Dajjito Junaid da Matarsa dama kuma Allah bai ba su haihuwa. Wannan dalilin ya sa aka ɓalla Gidan tunda ana da tabbacin su na ciki. Cikin jinin daya bushe aka samu Dattijo Junaid da wuƙa soke a gefen cikinsa, bakinsa ma jini duk a bushe ko da suka duba bakin anyanke mai harshe. Tsohuwar Matarshi kuwa tana Ɗaki a kulle tsoro da tashin hankali ya daɗe da sumar da ita. Mamaki da tsoron ne ya dirarwa mutanen Yankin Tudu, amma dayake yawancin su ma su ƙaranci tunani da kuma hangen nesa ne, sai suka fara surutun;
"ai shi ya jawowa kanshi, tunda ya ce shi bazai kama bakinsa ba"
Ba bu wani cikakken damuwa ko alhinin abinda ya faru da Dattijo Junaid a zuƙatan mafi akasarin mutanen Yankin, wannan ya sa suka cigaba da harkokin gabansu, tare da alƙawartawa kansu jan bakunansu su yi shiru tunda ba su shiryawa mutuwa ba, don babu wanda yaji ko da ihun naiman taimakon su Dattijo Junaid da Matarsa balle su sa ran idan sunyi ihu za su iya samun taimako.
Cikin hikimar Ubangiji numfashin Dattijo Junaid ya dawo cikin tsananin azabar rayuwa ko mutuwa tunda Allah bai ƙaddara ajalinsa a hannun waɗanda suka zo kashesa ba, Itama iyalinshi ta farfaɗo banda kuka babu abinda take yi. Keɓantaccen wajen da babu mai shiga sai Sarki Hammam da mai Maganin da zai dinga duba lafiyarsa Sarki Hamman ya tanada a cikin Marasautar tare da kashe maganar bincike akan kisan su Abduh Dhahab.
Ba bu wanda ya gamsu da maganar Sarki Hammam saboda sun san dole yayi bincike ta ƙarƙashin ƙasa. Don haka waɗanda suke da alhakin kisan suka shiga tararrabi tare da fara tunanin ƙirƙiro abinda zai kawar da hankalin mutanen Yankin da shi kanshi Sarki Hammam.
NAILA;
tun tana sa ran wata rana Sulaim zai dawo har ta gaji da cire rai, sai dai Gidan su ya koma dandali taruwa Yara abokannan wasanta tana ba su tahirin rayuwarta da Sulaim, har da tatsuniyoyi ta ƙirƙira na labarinta da Sulaim. Ba ta fita wasa kullum tana Gida kamar ba Naila mai son wasa da neman tsokana ba.
A cikin watanni biyu da mutuwarsu Abduh Dhahab wani gagarumin Talauci yafara kunnowa Yankin kai. Rana ɗaya suka wayi gari babu Malaman Makaruntun su, Asibitin Mallam da Sarki Hammam yasa aka gyara dukka ma'aikatan jinyar sun gudu. A cikin yini biyu Mutane biyar suka rasa ransu saboda rashin ma'aikatan jinya. Ba bu wani Ɗan Yankin Tudu da hankalinsa bai tashi ba, ciki har da Ɗayyib da bai jima da samun sauƙi ba.
A rana ta uku Mahaifin Naila da ya tashi da tsananin ciwon ciki shima ya rasa ransa zuwa yammaci duk da maganin gargajiyan da akayita ɗirkamai don sun je Asibitin Gwamnati ba ma'aikata. Asibitin Mallam dama tuni aka rufeshi tunda dukka ma'aikatan sun gudu.
Rasuwar Mahmoud Maihaifin Naila wani babban gibi ne mai girman gasken da su Naila ba su da abin maye gurbinsa har abada.
A cikin watannin da suka biyo baya wani irin Talauci ya yi wa Yankin mamaya mai ƙarfin gaske, ga shi babu wadataccen ilimi ba bu Ma'aikatan lafiya masu sanin makamar aiki. Zuwa Lokacin Dattijo Junaid ya samu lafiya amma babu damar yin magana.
Suna cikin wannan yanayin Abdullah ya bayyana a matsayin ƙwararren Likitan da Gmannati ta turo.
Sarki Hammam ya yi Farin cikin bayyanar Abdallah a matsayin Likitan da gwamnati na musamman, Saboda sabon abune a garesu, domin shi da al'ummar Yankinsa rayuwa suke yi tamkar ba ƴan ƙasa ba, babu gwamnati da hukuma sam a lamuransu, sai ɗan abinda ba'a rasa ba, shiyasa kowa yake yin abinda ya ga dama
Bayan kwana biyu
Cikin iko Allah marasa lafiya suka fara samun kulawa ta musamman. Mutanen Yankin sun saki jiki da Abdullah tare da wani irin so da sukeyimai saboda sauƙin kansa da iya mu'amalarsa. Wannan dalilin yasa ya buɗe aji koyawa Matasan da suka kai shekaru 18 mata da Maza dabarun kula da mara lafiya da karɓar haihuwa cikin Hikima.
Da kayan aikin dayazo yake koyawa mu su. Kafin rufuwar wata biyu wasun su har sun ƙware.
A hankali labarin alkhairin Abdullah ya fita ko ina na Yankin sai ya zamana har a maƙotan Yankin su ana zuwa ɗaukar Matasa wala Namiji ko Mace don duba majinyaci ko karɓar haihuwa. Cikin lokaci ƙanƙani talauci Yankin ya fara raguwa walwalarsu ta fara dawowa.
A cikin watanni shida Abdullah ya yaye Ɗalibansa haɗe da ƙara ɗiban wa su. Sarki Hammam da Dattijo Junaid baƙaramin alfahari sukeyi da Abdullah ba, girmamashin da suke yi ma na daban ne.
A na cikin haka aka tsinci ƙaramar Yarinya anyi mata fyaɗe mara kyan gani a bayan Ofishin Abdullah.
Duka na rashin imani da manta halacci Mutanen Yankin sukayiwa Abdullah. kafin sanarwar ya isa ga fadar Sarki Hamman har sun sumar da shi.
"Wani irin ƙwaƙwalwa ne a cikin kan Mutanen Yankin Tudu, kuma wacce irin zuciya gare su mai tsanin butulci da manta alkhairi? Ta ya ya Abdullah zai iya yiwa Yarinya ƙarama fyaɗe na rashin imani irin wannan? shin ina hankalin su yake? Maiyasa ake amfani da toshewar basirar su wajen sa su su dakushe cigaban Yankin su da kansu batare da sun sani ba?" Dattajo Junaid ya tambayi kanshi zuciyarsa na Suya.
Daƙyar Fadawan Sarki Hammam suka fatattaki Mutanen Yankin da bulalai.
Babu wani ƙwararren Likita a ƙasa da zai iya kula da Abdullah, sai masu maganin gargajiya aka nemo.
★washe gari duk da haka Mutanen Yankin basu haƙura ba gangami sukayi har Asibitin suna faɗin abi mu su haƙƙinsu, a cikin su har da waɗanda Abdullah ya koyar kuma suke samun alheri. A cewar su "dama sun san dole akwai wanda ya turoshi don cin mutuncin Yankin su" Daƙyar fadawan Sarki Hammam suka ƙara fatattakarsu da bulalai.
★washe gari da sassafe aka tashi da labarin guduwar Abdullah daga Asibiti bayan ya farfaɗo, fadawan Sarki Hammam ne suka bada labarin wani ne yazo da sunan dubanshi shikuma Abdullah ya yi mishi rakiya a daddafe zuwa motar daya zo dashi gabannin Asubahi daganan kuma basu ƙarajin ɗuriyarsa ba.
Labarin sam bai yiwa Wa su marasa goyon bayan lamarin daɗi ba musamman Sarki Hammam da mutanensa. Dattijo Junaid kuwa har da kukansa.
Labarin abinda mutanen Yankin sukayiwa Abdullah da labarin guduwarsa har wajen Yankin wannan sai ya sa musu baƙin jini tare da kafa tsoron su da ƙyaƙyamin kulla alaƙa da su a zuƙantan maƙotan Yankunan su.
A wannan yanayin Mahaifan Maman Naila suka zo ɗaukarta tunda ta gama Takaba tuntuni. ko da aka buƙaci su tafi da Naila tunda Yarinyarce, ƙin amincewa sukayi bayan baƙaƙen maganganun da suka gasawa Mahaifiyar Mahmud kakar Naila tare da yin Allah wadai su tafi Yankinsu da jinin mutanen Yankin Tudu.
Dole Naila ta koma wajen Kakarta ta wajen Uba da zama bayan kukan da ta sha har da zazzaɓi.
Cikin watannin da suka biyo baya, Mutanen Yankin suka ƙara komawa Talaucin da yafi na baya muni da raɗaɗi. Ga ƙyama da suke fuskanta daga dukka ƙabilun dake kewaye da su, ko Aure ɗan Yankin Tudu yaje nema ba'a ba shi.
Rana ɗaya dukka matasan Yankin suka yi zuciya suka koma Gona har da Ƴaƴa mata saboda raɗaɗin Talauci da rashin abin yi. Don ko aure Mazan Yankin suka fita nema a mokatan Yankin su ba'a ba su, balle su yarda Ɗan su ya auro mu su Ƴar Yankin Tudu. Wannan dalilin yasa suka fara auren Junansu cikin tsananin Taulauci.
Bayan amfanin Gona ya yi, suka fara fita dashi kasuwanni Yanki-Yanki. Abin mamaki duk Yankin da suka kai ba'a siya sai su ce "Allah Ya raba su da cin kayan amfanin gonar mutanen Yankin Tudu" kamar waɗanda sukayi bar ruwa da guba haka Kayansu ya koma a idon Mutane. Ko wani bare daga wani ɓangaren da bai sansu ba ya yi niyyar siya sai aja kunnensa da kar ya kuskura idan ba haka ba kuwa, tamkar ya kirawa kansa mutuwa ne.
Mutanen Yankin Tudu suna ji suna gani suka ƙara komawa Talaucin dayafi na da raɗaɗi da azaba
Suna cikin wannan yanayin Salman ya shigo Yankin a matsayin mai koyar da sana'o'in da gwamnati ta turo...✍🏻
09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥
SASAAL
04
Bayyanar Salman a Fadar Sarki Hammam a matsayin mai koyar da Sana'o'i ya yi matuƙar faranta ran Mutanen Yankin kamar dai lokacin Abdallah, saboda ya zo akan gaɓar da suke tsananin buƙatar ire-irensa.
Ɗayyib ne ya kawo shawarar mai zai hana a kai Salman Gidan marigayi Abduh Dhahab da tun bayan Mutuwarsa yake a garƙame a matsayin Masauki?. Ba bu jaa kowa ya yi na'am da shawarar Ɗayyib tunda Salman ya ce shi ma Maƙeri ne.
Bayi Sarki Hammam ya bawa mukulli suka gyara gidan.
Ɗayyib da kansa yayiwa Salman rakiya har gidan Abduh.
Bayan sati ɗaya.
Da tsananin Farin ciki da wani ƙauna mara iyaka Ɗayyib ya nufi Salman bayan ya gama kallon irin Tukwanen da Salman ƙera. Rungumesa ya yi ya sumbaci gefe da gefen kunchinsa, sannan ya ce;
"A ina ka koyi ƙera irin Tukwanen da Aminina Abduh Dhahab yake ƙerawa? Tun bayan mutuwar Abduh muka shiga wani yanayin na ƙangin rayuwa, saboda mutuwar Kasuwar Tukwanen Zinaren da yasha wahala kafin kafuwarsa, ba bu wanda ya yi hikimar koya a cikin mu lokacin da ya ke raye, daga shi sai Ɗansa Sulaim ne kawai suka iya ƙerawa. Sai ga shi bayan munfidda rai da ƙarasamun rayuwa mai daɗi Allah Ya Kawo mana kai. Alhamdulillah!" Ɗayyib yaƙara faɗa ƙwalla kwance a ƙasan fararen manyan Idanuwansa.
Salman bai ce masa komai ba sai murmushinsa daya faɗaɗa yana komawa wajen Tukwanen daya ƙera. Har Ɗayyib ya gama santin Tukwanen
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 15