balar miƙewa adda'a ɗauke a bakinsa, zare kayan dake jikinsa ya shiga yi wannan asalin lafiyayyar chocolote skin ɗin nashi na bayyana tana ɗaukan ido, saboda samun hutu da tsadaddiyar gyara da original skin products masu tsada da kyau da yake amfani dasu. Kai tsaye bathroom ya faɗa tare da sa karma kansa shower yana lumshe idanuwansa ruwan na sauƙa akan fuskansa suna ganganrawa jikinsa suna sanyaya jikinsa a hankali.
Ya jima sosai sosai a ruwan yana wankan, kafin ya fito ɗaure da babban towel me ɗan kauri white har wani miski miskin blue yake, jikinsa na fidda ƙamshin shower Soap ɗinsa na Ocean seaweed. Hannun sa ɗaya na riƙe da wani mini clean blue towel ɗin daban yana tsane jikinsa a natse. Pyjamas farare ya zira yana kallar agogon bangon dake ɗakin nasa. Ganin se yanzu ne ma sha biyu ke bugawa ya sanya sake ɗaukan system nashi, akan wata arniyar ɗunƙulalliyar kujera ya zauna yana fesar da hucin numfashi,
Ci gaba da ayyukansa yayi har zuwa wajen ɗaya, iska ya zuƙa ya kuma fesar yana jan idanunsa ya lumshe ganin ya kammala aikin nashi, Goran ruwan dake a Centre table ɗin dake gaban gadonsa ya ɗauka. Batare da yabi takan kofin dake kusa da ita ba ya ɓalle murfin kawai yakai bakinsa ya fara kwankwaɗa, Sai da ya shanyesa tas sannan yayi cilli da bottle ɗin, yana ambatar ALHAMDULILLA a bayyane.......
★
Zaune takai akan gefen gadonta tana haɗe kanta da gwiwwarta ababuwa na nemar fasa kanta ,idanunta sunyi wani irin jajir ɗin kaiwa maƙura a ɓacin rai da tashin hankali, daga inda take cakuyen take me roƙon ALLAH inama ya bata damar fashewa da gursheshen kuka. Se dai tayi duk yacce za ta yi amma ina kukan nan yaƙi iyuwa ya, tabbas se a yau take sake yarda wani kukan ma rahama ne, lallai kuma ta sake yarda da zancen nan na mutane da suke cewa idan baƙin ciki yay baƙin ciki kukan ma baya taɓa yiwuwa, Shin me rayuwa take nufi da ita ne wai har haka?, hannunta na dafe da kanta ta buɗe idonta, se kuma ta ware duka hannuwanta guda biyun tana me furta.....
"YA ALLAH!, kai ne ka ƙaddara min wannan daddaɗar jarabawar taka kuma na amsa da hannu bibbiyu, haka kuma kai ne ka ƙaddara min duk kan abinda zai faru dani a yau ɗina har dama gobena!. Haka kuma komai a cikin ikon ka da yardarka suke ci gaba da tafiya, Ya ALLAH kaci gaba da zama gatana!, YA ALLAH a koda yaushe cikin gode maka nake akan duk abinda ka jarabceni dashi a cikin duniyar, ka kuma bani juriya da hakurin ibadarka, domin kuwa UBANGIJINA ka fini sanin daidai, Komai na rayuwar ɗan Adam na tafiya ne bisa tsari da kuma ƙudurarka, komai kaga ya faru da bawa dama tun fil azal hakan na cikin rubutun kundin ƙaddarar sane, Wala ƘADDARA me ƙyau ko akasin hakan se dai masu iya magana sukan ce ita ƘADDARA abace mara tabbas nan dake takan iya sanjawa. Ya ALLAH ka fini sanin daidai na, ka mini maganin dukkan matsalolin da suke kewaye da wannan rayuwar tawa!, ka Zama gatan Mara gata... Ya ALLAH na amshi wannan rayuwar data zo min a wani irin hagunce, Hakan da ka tsara min na gode Ya Rabb, Tabbas wata rayuwar ba tamu ba, kamar yadda wata wata ƙaddarar ba sakacinmu ba ne, domin kuwa ƙaddara ba canki in canka bace bare kace zaka zaɓarma kanka kalar rayuwar da kake so ba, Ya ALLAH bana da iko ko halin da hukuncin ka, amma ka yanke min duk abinda yake ba alkhairi na bane..... Mafita ALLAH!, mafita ya ALLAH...." Tayi maganar jikinta na wani kalan tsuma, ji tayi kamar ana fuskarta zuwa baya don haka idanunta suka fara ganin xbibbiyu numfashinta kuma na gwamewa.... Se dai be kai ga rabuwa da gangar jikin nata ba wannan dai hayaniyar data gudonmawa na sake iskota har zuwa nan sashen nata, Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un take ambata tana jin inama a yanzun ba sai anjima ta mutu tabar duniyar, wannan wanne kalan ƙalubale da jarabawa ce haka, me ta tare ma Hajiya Ana surukuwarta kuma Uwar Mijinta?, me ta mata da zafi haka, don kawai ta auri ɗan ne?, ko kuwa kawai don akan wannan ƙaddarar ta taɓa faɗa mata ne? Ta na tsaka da wannan tunanin ne kuma burum taji an bugo mata ƙofar bedroom ɗin nata....
"Kina ina shegiya baƙar munafuka!, to wllh na gaji da zama dake a haka, gaba ɗaya tun da kika auri Yahaya na dena gane mishi, gashi zama yayi zama ace zama har shekara na ƙoƙarin wucewa amma ace ko ɓatan wata baki taɓa yi ba, to wllh da sake, A yau ba sai yanzun ba indai ni uwace ga Alƙali Yahaya Shehu Usmanu seya sake ki Aminan...."
Jikintane ya tsananta rawa sosai fiye da farko, amma babu ɗigon hawaye ko ɗaya a ƙwayar Idonta, shigowar Alƙalin kamar wanda aka kifo ne ya saka Meenerl ɗin saurin miƙewa tana nufarsa, don gani take a cikin wannan yanayin shi kaɗai ne Garkuwa da madogararta, hannunsa ta koma cikin kamar ta fice a hayyacinta tana jan shi gaban Hajiyar tasa suka zube, "Don ALLAH Hajiya kiji tausayina, ki tausayama maraicina kiyi hakuri ki janye kalamanki akan mu, wllh ba laifi na bane, Daddy'nsu kace wa Hajiyarmu nima zan haihu, kai nake ta jira wllh a shirye nake indai zaka bani cikin!!!, Nima ina son yaran Hajiya...." Cafe zancen yayi shima ta hanyar sake furta.
"Hajiya dan girman ALLAH, don Annabin Rahama Annabi Sallallahu alaihi Wasallam kiyi hakuri Hajiya, don wanda akai duniya dominsa lahira dominsa, aka yi wuta don maƙiyansa, aljannah kuma don masoyansa ki gafartamana ki mana sassauci wllh ina son Jaririyata, ina jin tsananin tausayinta, wllh ban san wanda ya haɗani dake ba cikinsu, amma kamar yanda kika shariɗanta min wllh tin daga wannan ranar ban sake kusantar ƴar shila ba gata nan ki tambayeta koba haka ma Meenal?..."
Wanda ita kuwa Meenal ɗin jin kalamansa na ƙarshe ne suka sake nemar gigita ƙwanyarta, me hakan ke nufi?, Hajiyar ce ta hana masa dena kusa tarta kenan da yayi tsayin watanni kusan har ukku kenan?, wanne laifin tama ALLAH ita kam da yake jarrabarta da ƙaddarori masu kwamanceceniya da juna?, ita kuwa Hajiyar se wani sake huhhura hanci sama take tana wani karkada ƙafafunta. "Ta yaya kake son inci gaba da yarda dakai Yahaya?, A gabana fa yanzun gashi nan kake ƙiranta da sunaye na fitsara da rashin mutumci har da wata ƴar shilarka, dan ubanka yau she ka fara farauta ban sani ba da har kake da wata ƴar shila?, kuma ni dai iyaka sani na baka taɓa sunkuyawa da kanka ka haihu ba bare na sake tabbar da cewar kana da jaririyar, ka sani idan har kaji bakina ya sake buɗuwa da nufin kowacce kalan magana to ka sani ta tsinuwace gare ka Yahaya....."
"Hajiya don alfarmarki da Sayyiduna Muhammadun Sallallahu alaihi Wasallama kuyi.....h......."
_ALHAMDULILLAH!,ALHAMDULILLAH!!, ALHAMDULILLAH ala kulli halin🙏 🙏!!!, Anan na kawo ƙarshen book One na KARSHEN ƘADDARA, sai kuma ALLAH ya haɗa mu da masu rabo a BOOK TWO nashi_
_Tofa masu karatu yaya take ne?, mike shirin faruwa?..._
_Shin ya kuke ganin za a kare tsakanin Alƙali Yahaya Shehu Ɗan Batta da kuma mata da mahaifiyarsa?...._
_Ku a naku gani da tunanin wannan sakin ze iyu kuwa?, Me kuma kalaman Hajiyar suke nufi da gasken kenan itace da kanta ta dakatar dashi ci gaba da mu'amulantar matarsa?, kai wannan cajin kai dai da yawa yake...._
~A tunaninku shike nan wasan zezo ƙarshe ne?, La la la..... Yanzu ne ma zamu ɗauki wani salon shima me zafi, kuma shima kakan nashi ƙalubalen daban shima~
_Domin kuwa a gobe ma da wani labarin, Kwarai kuwa haka Nie AMMEY LAYLERH'NKU ɗin ku naceeee...._
_Wai hausawa suka ce ɓukatar maji hajji Sallah, karfa ku manta da hasashen Ahmad kar dai ya zame mana gaskiya jama'a, domin fa ance sunan littafin ƘARSHEN ƘADDARA karku manta, me bi kuwa akwai yiyuwar wasu aure auren bayan na Alƙalin dake kanta, wanda yake daf da rugujewa shima....🤸🤸🤸🤸_
_Amma fa kar FAN'S su ce na fiye zaƙewa nima a zaƙen nake da jin yadda zata kaya ɗin ne ai🤩_
_Tofa wata daban kuma wata sabuwa, wai ma waye wannan MAJEED DAWOUD ISHAQ ɗin ne?, Baban AYLA kuma lawyer ɗin daya tsaye ma AMEENERH SHEHU USMAN, har se da Shari'a ta bata gaskiya....?_
_Wai kuwa 👍 🙂 duk kun shirya bin AMMEY LAYLERH'NKU, don warwarar wannan ƙaddarar da daku?, kun shirya ayi tafiyar daku cikin labarin littafinta me SUNA KARSHEN ƘADDARA???_
_Hhhhh Hajiya ke dai nace bara nai shiru kar na cika masu karatu da tarin jawabai, domin kuwa tafe labarin yake da tarin gurmi. Gurmi gagarumi ma kuwa na musamman. Dan littafin nan ɗauke yake da nasa salon da ban taɓa yin irin saba na sani_
_HUMMM Kai kar dai na cikaku da surutu ku shirya kawai tsaff domin warware muku zare da abawar dake cakuɗe cikin wannan littafin_
_Duk zamu samu amsoshin waɗannan tarin tambayoyi namu ne idan mun shiga book 2 da yardar Allah. Nan muka kawo ƙarshen BOOK 1 NA ƘARSHEN ƘADDARA Wanda basu biya ba su hanzarta don kar ayi tafiyar babu su littafin ƘARSHEN ƘADDARA 500 Hundred ne kacal babu yawa..._
_Ga duk mai son biya kai tsaye zai tuntuɓeni a wannan number_
👇
08104493215
Wanda suke sun biya zasu turo kuɗin su cikin wannan asusun bankin
👇
8104493215
Maryam Nasiru
Opay
Or
3206656358
Maryam Nasiru
First Bank
A turo shedar biya ta wannan number
08104493215
_Masoya na amana a nuna min kauna sai najiku masoya karku sake ayi tafiyar PART 2 na KARSHEN ƘADDARA, daga AMMEY LAYLERH'NKU me ƘAUNARKU FAKA FAKA_🤸🤸🤸_
_Byee my FAN'S sai mun sake HAƊUWA a cikin PART 2 gamai Rabo. Dan koda kuɗin ka saida rabonka littafin ƘARSHEN ƘADDARA ba hhhhhhhhhhh To ai shikenan sai a gimtse koooo?...... To ai shikenan kawai A gimtse ɗinnn🤸🔏 🫰✊_
_MASU TAMBAYANA JERIN SUNAYEN LITTATTAFAINA TO GASU KAMAR YACCE NA MUKU ALƘAWARI ZAN LISSAFO MUKU...._
*KAREN BANA FREE*
*JALAAL AREEF FREE*
*ƘAUNA BIYU FREE*
*MIKIYA PAID ONLY 500 HUNDRED*
*TA DABAN ONLY 500 HUNDRED*
*DUNIYARMU ME CIKE DA TARIN ƘALUBALE ONLY 1K*
*SO DAN RAYUWA ONLY 500 HUNDRED*
*RAMIN KURA ONLY 1K*
*DUHU na DUKAN duhu ONLY 1K*
*SE KUMA SHI WANNAN ƘARSHEN ƘADDARAR shima 500 HUNDRED yazo muku*
Ku sani waɗan nan litattafan suna jerin sunayen littattafan nawa ngd👏👏👏....
*BY AMMEY LAYLERH ✍️*
ᴬᴹᴹᴱʸ ᴸᴬʸᴸᴱᴿᴴ🤫😶🤐😥😢😩👌✍️🙏👩👁️🤦🙅♂️🙋♂️🙆♀️.......
08104493215
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 14