Sannan ta yi wa mutanen Kura tsaraba musamman Malam Bala da dangin mahaifan Abdulwahab na uwa da uba. Kwanan ta uku ta kafe sai ta tafi Kura,kuma da Salma za ta tafi,domin amana ce Atine ta bata,ba za ta rabu da ita ba sai aure ko mutuwa. Salma na jin maganar aure kunya ta kama ta,sai ta dena rikicin ba za ta bi Gwaggo Kande ba ta wuce ta fara haɗa kayanta. Washegari da sassafe Abdulwahab ya saka su a mota suka koma Kura.
Gwaggo Kande na tafiya Mahaifiyar Ammabuwa ta matsa akan sai Ammabuwa ta koma gida wanka,domin ta gano babu wani babba da ke yi mata wanka shirmen su kawai suke yi ita da Layuzah a gidan. A daidai wannan gaɓar Layuzah ta shiga damuwa saboda tafiyar Ammabuwa,sai take jin gidan shiru babu Salma,babu Maheer,ga Ammabuwa ƙawa kuma aminiyarta ta koma gidan iyayenta. Wannan damuwar da ta shiga ne ya sanya Abdulwahab bata lokacinsa sosai,har ya zamana watarana ma baya fita aiki ko kasuwa, Mudassir ne kawai yake tafiya ya ji da komai. Ana haka Layuzah ta fara yawan cin abinci da kwaɗayin tsiya,bata yin wani ciwon kuma bata amai ballantana zazzaɓi. Gaba ɗaya basu gane abinda ke faruwa da ita ba har sai da Ammabuwa ta gama wankan gida,danginta suka dawo da ita cikin kwalliya irin ta Buzaye da kayan gara irin na al'ada da ake yi a duk haihuwar fari. A lokacin da za su tafi ne wata Innar Ammabuwa ta ke cewa.
"To Gwaggon Maheer kema Allah Ya sauke ki lafiya. Ku ci gaba da haƙuri da junanku domin zaman ku lafiya na faranta mana rai mu iyayenku. Allah Ya yi muku albarka."
Da haka suka tattara suka tafi suka bar Ammabuwa cikin murnar dawowa kusa da aminiyarta. Bayan sun raka su sun dawo ne Ammabuwa ta ce.
"Ƴar'uwa wai meye sirrin ne na ga kin yi wani irin kyau sai kace yanzu ne kuke cin amarci ke da Yayana?"
Murmushi Layuzah ta yi ta ce.
"Ni kai na ban san me yake damu na ba,kin ganni nan babu abinda na saka a gaba da ya wuce kwaɗayi da yawan cin abinci, sai kuma yawan bacci kamar wata kasa."
"To ko dai maganar Innahta ce za ta zamo gaskiya Maheer zai samu ƙani ko ƙanwa?"
Kunya ce ta kama Layuzah ta ce.
"Habaa babu wani ciki da nake ɗauke da shi ni dai. Da duk ban samu ba sai yanzu?"
"Iyi mana,ai Baban Mudassir ya bani labari irin soyayyar da kuke zubawa a gidan nan kamar wasu tattabaru."
Dariya kawai Layuzah ta yi, ta wuce ciki ta ɗakkowa Ammabuwa abicin da ta dafa mata na musamman. Nan suka zauna su na ta hira Layuzah na riƙe da Maheer a cinyarta ta na jin son yaron na ƙaruwa a cikin ranta saboda kyau da girman da ya sake yi.
Su Layuzah basu tashi sanin tana dauke da ciki ba har sai da cikinta ya kai watanni huɗu a duniya. Ranar da ta fara jin motsi ta gigice ta gigita kowa a gidan. A wannan ranar kuwa Abdulwahab baya gari tafiya ta kama su daga wajen aikinsa. Mudassir ne ya ɗauke ta a kan babur ya kai ta asibiti aka duba ta. Bayan gwaje-gwaje likita ya tabbatar musu da cewar ta na ɗauke da juna biyu har na tsawon watanni huɗu. Murna sosai Mudassir ya dinga yi,ita kuwa Layuzah sai ta ji kunyar Yayan nata ta kama ta har ta ƙi hawa babur ɗinsa sai da ya samo mata bus ta hau aka mayar da ita Ƴankaba. Ta na zuwa gida ta tarar da Mudassir ya riga ta zuwa har ya sanar da Ammabuwa. A ƙofar gida ta tarar da Ammabuwa goye da Maheer ta na ta washe baki. Hijabi ta sa ta rufe fuskarta saboda kunyar da ta ke ji. A haka suka shige gida Ammabuwa na nan nan da ita. Har so take ta ji Layuzah na buƙatar wani abu ta gabatar mata da shi. Bayan kwana biyu Abdulwahab ya dawo daga tafiya aka sanar da shi wannan labarin mai daɗi,farinciki ya dinga yi ya na kumawa tare da godiya ga Allah da ya yi masa wannan kyautar.
Sosai mutanen nan uku suke nuna wa Layuzah kulawa har watarana ta kan rasa bakin yi musu godiya. Idan Mudassir na tsokanar Abdulwahab sai ya ce.
"Ni dai na shiga uku da surukin zamani,wai kai ba ka jin kunya ta ne don Allah?"
"Ina fa zan ji kunyar ka tinda dai ni ba a suruki na ɗauke ka ba. Kai ɗin abokina ne,aminina ne kuma ɗan'uwana. Dan haka babu wata kunya a tsakaninmu."
Abdulwahab na jin daɗi a ransa idan ya ji Mudassir na bashi babban matsayi a ransa.
Ana haka cikin Layuzah ya shiga watan haihuwa,gashi Abdulwahab ya na so ya yi tafiya ƙasar Ghana saboda shigar da wasu kaya da suke son su yi. Da jin haka sai Layuzah ta hau kuka ta na faɗin.
"Gaskiya babu inda za ka tafi ka barmu ni da abinda ke ciki na,ko kana son ka tafi ka barni wajen haihuwa na mutu baka nan?"
Da sauri Abdulwahab ya kalle ta ya na jin zuciyarsa na tsananta bugawa. A duniya baya son ya ji Layuzah na kiran mutuwa ko rabuwa a tsakaninsu. Dan haka cike da rarrashi ya ce.
"Ki kwantar da hankalinki,babu inda zan je, bana Yayanki zan tura Ghana duk da baya son tafiye-tafiye,na rasa me yake jin tsoro,amma dai a wannan karon dole shi zai je,idan ba haka ba kuma sai dai mu haƙura da kai kayan gaba ɗaya,tinda ke kin ƙi amincewa na tafi."
Haka suka dinga hira Layuzah na sake jaddada wa Abdulwahab rashin son tafiyar da zai yi. Lokacin sallar Isha'i na yi ya tafi ya yi alwala ya wuce masallaci. Bayan an idar da sallah su na dawowa daga masallaci Abdulwahab ya kawo wa Mudassir buƙatarsa na tafiya ƙasar Ghana kai kaya da yake son ya yi. Ba dan Mudassir ya so ba kan dole ya amince da tafiyar. Su na zuwa gida ya dinga yi wa Layuzah masifa ya na cewa duk laifinta ne ta sa mijinta zai aika shi wata uwa duniyar. Dariya kawai ta yi ta ci gaba da yi wa Maheer wasa. Ammabuwa kuwa sai ta ce.
"To ai gwanda ka yi tafiyar ma ko mutum ya ɗan huta na wasu kwanakin. A yi mutum kullum ya na gida ko tafiyar kwana ɗaya baka taɓa yi ba fa."
Ƙanƙance ido Mudassir ya yi yana kallon Ammabuwa ya ce.
"Au haka ne? Dama duk ƙarya kike zuba min da kike cewa ba kya son in dinga yin nisa da ke? To ai shikenan,Aboki ni fa daga yanzu na koma ɓangaren zirga-zirgar ƙasa da ƙasa."
Dariya sosai suka yi gaba ɗayansu,sannan suka ci gaba da hira mai cike da nishaɗi da barkwanci. A wannan ranar basu rabu da junansu ba sai misalin sha ɗaya da rabi na dare. A daren kuma Ammabuwa ta haɗa wa Mudassir kaya a ƴar ƙaramar jaka ta saka masa duk abinda zai buƙata. Sannan suka kwanta suka raya daren nasu cike da soyayya.
Washegari ana idar da sallar asuba Malam Sallau ya zo da tawagar da za su yi tafiyar a mota. Sallama Mudassir ya yi wa su Ammabuwa da Layuzah dake riƙe da Maheer da ya tashi tun asuba bai koma bacci ba,banda kuka babu abinda yake yi. Su na gama sallama ya bi Abdulwahab suka tsaya a zaure ya bashi wasu ƴan kuɗaɗen da zai yi amfani da su ko da buƙatar hakan ta taso. Rungume junansu suka yi sannan suka yi musabaha hannunsu na riƙe da na junansu Mudassir ya shiga mota yana ɗaga wa Amininsa hannu........
MUGUWAR MACE.
NA HAMIDAH SANUSI AHMAD HAERMEEEBRAERH ✨✍️
*Yanzu muka fara wannan labari na MUGUWAR MACE mai cike da sarƙaƙiyar rayuwar zaman aure,makirci,butulci,sihiri,tare da cikakken ilimin zaman duniya. Idan ki na son a ci gaba da yin wannan tafiya tare da ke sanya 1k ɗinki ta wannan account ɗin 9031416423 Opay Hamidah Ahmad Sanusi. Sai ki tura shaidar biya ta 09031416423. Don girman Allah idan har kin san za ki siyi novel ɗin nan ne da niyyar ki yaɗa shi a group ɗin da idan kika bari suka siya a waje na nima zan samu alkhairi to ki yi haƙuri kada ki siya,domin idan kin siya kin yaɗa kin kashe min kasuwa. Don Allah mu so juna domin Allah kada mu dinga zalintar junanmu.*✨✍️
PAGE 14.
Zuwan Mudassir ƙasar Ghana ya sanya idamuwansa sake buɗewa akan kasuwanci ƙwarai da gaske. Lokacin da za su dawo gida Nigeria bai yi shawara da kowa ba ya saro wasu daga abubuwan da suke da shi a can wanda mutanenmu na Nigeria ke da buƙata suka kamo hanya da sauran yaran Abdulwahab suka dawo. A wannan lokacin ne ɗaya daga cikin yaran Abdulwahab mai suna Iliya ya kai masa gulmar yanda Mudassir ya dinga facaka da dukiyarsa a Ghana. Nan take shaiɗan ya yi uwa ya yi makarɓiya ya dasa wa Abdulwahab wani ƙulli a cikin zuciyarsa game da aminin nasa kuma Yaya ga matarsa. Tin daga wannan ranar alaƙarsu ta fara sauyawa,sai ya zamana kafin Abdulwahab ya kira Mudassir sau ɗaya ya kira Iliya sau biyar. Mudassir na kula da hakan sai ya ja baya ya koma yin ayyukan da ba lallai ne sai ya nemi izinin Abdulwahab ba,sannan ya kame bakinsa bai sanar da matarsa ko ƙanwarsa sauyin da yake gani a tattare da abokin nasa ba.
Sosai Mudassir ya kai zuciyarsa nesa game da yanda Abdulwahab ya dinga ɗaure masa fuska da nuna masa iyakarsa,sai Mudassir ya nuna sam bai ma gane abinda yake yi ba,harkar gabansa kawai ya sa a gaba tare da ƙoƙarin kawo cigaba a cikin kasuwancin da suka sha wahala wajen ginawa. A hankali Malam Sallau ya kula da abinda ke faruwa a tsakanin aminan junan. A matsayinsa na amintaccen yaron Abdulwahab sai ya tsaya ya tsananta bincike akan lamarin,babu jimawa kuwa ya gano abinda ke faruwa. Ba tare da sanin kowa ba ya ɗana wa matashin dake son ya ture Mudassir daga rayuwar Abdulwahab shi ya kafa tashi kujerar tarko.
Watarana Malam Sallau ya karɓo takardun wasu filaye da ya siyo wa Abdulwahab sai ya je shago ya bawa Mudassir a gaban Iliya da mutanen shagon ya ce ya bawa Abdulwahab,babu ɓata lokaci Mudassir ya karɓa ya saka su a cikin jakar da yake zuwa da ita shagon nasu da niyyar idan Abdulwahab ya taso daga aiki ya biyo shago sai ya bashi,idan kuma bai biyo ba in sun je gida sai ya bashi,daga nan sai ya ci gaba da harkar gabansa. Malam Sallau na zaune ya na ta hirarsa amma gaba ɗaya hankalinsa ya na kan Iliya da ke ta kallon mutane ya na zuge jakar Mudassir. A hankali ya zare takardun ya fita daga shagon da sauri ya nufi shagon da suke kwana ya ɓoye,ya na gama ɓoyewa ya dawo ya ci gaba da aikinsa kamar babu abinda ya aikata. Da ganin haka sai zargin da Malam Sallau yake yi akansa ya tabbata. Sai da ya bari an tafi sallar magrib ya shiga shagon su Iliya ya ɗauke takardun. Da dare bayan Abdulwahab ya koma gida Malam Sallau ya je ya bashi labarin duk abinda yake faruwa da kuma hasashen da yake yi akan Iliya. Cike da tsantsar nadama da danasani tare da jin nauyi da kunya Abdulwahab ya ce.
"Bana tamtama akan abinda ka sanar da ni Malam Sallau,amma ina so don Allah ka taimaka mini domin kama Iliya hannu da hannu domin na ji daɗin hukunta shi akan abinda ya sa na aikata."
"Yauwaa Alhaji an zo wajen. Ina so gobe da safe a gaban Iliya ka tambayi Malam Mudan takardun nan da na nuna maka,da ka tambaya ka bar min komai a hannuna."
Sallama suka yi da Malam Sallau Abdulwahab ya koma cikin gida cike da nadama,a wannan ranar ya gane cewa lallai matansu sun yi ƙoƙari da suka riƙe zumunci suka ƙi ba wa ƴan gulma damar shiga tsakaninsu. Tunani ya fara yi ta yaya ma har ya bari wani bare zai raba shi da mutumin da ya fara taimaka masa a rayuwa? Duk dukiyar da ya tara yake alfaharin zamowarta tasa da taimakon Mudassir ya tara ta. A wannan daren kasa bacci Abdulwahab ya yi. Asuba na yi ya watsa ruwa ya yi alwala ya tafi masallaci. Bayan an idar da sallah kafin Mudassir ya fito daga masallacin Abdulwahab ya gudu gida,domin kunya yake ji ya haɗa ido da shi ballantana har su yi magana. Ya na kwanciya bacci mai daɗi ya ɗauke shi har Mudassir ya shirya ya samu Layuzah ya tambaye ta ko Abdulwahab ya farka kuwa? Sanar da shi ta yi bai farka ba,dan haka sai ya tafi kasuwa da zummar idan Abdulwahab ya je zai bashi takardun a can.
Abdulwahab na farkawa Layuzah ta sanar da shi zuwan Mudassir,shiru ya yi kamar wanda ruwa ya cinye,gani yake yi kamar kowa ya san abinda ya aikata a gidan. Sai kawai ya ɗakko mata zancen zuwan Gwaggo Kande domin ta kula da ita har ranar da za ta haihu. Cike da jin kunya Layuzah ta ce.
"Ni dai gaskiya bana son Gwaggo Kande ta zo ta karɓi haihuwa ta. Dama ina a can Kuran ne idan ta karɓi haihuwar babu komai,amma ina a nan gaskiya ni dai a barta kawai,idan na sauka lafiya sai ta zo ta dinga yi wa jariri wanka."
Murmushi ya yi ya shafa ƙaton cikin nata da suke wa laƙabi da cikin ƴan biyu. Ba tare da ya ce komai ba ya ƙarasa shirin fita ya buga babur ɗinsa ya wuce kasuwa.
Ko da ya isa ya tarar da manyan shagunan nasa guda huɗu dake jere da juna sun ɗauki harami ana ta cinikayya. Shigarsa wajen ke da wuya yaransa suka je suna ta gaishe shi yana amsawa. Malam Sallau dake zaune a gefe ma ya gaishe shi yana kallon Mudassir dake zuwa shagon hannunsa riƙe da jakar bakkonsa da yake saka kayansa a ciki. Ya na zuwa ya fara gaishe da Abdulwahab wanda sai a wannan lokacin ya gane irin sauyawar da ya yi ashe ba kaɗan bace. Su da suke caccafkewa da abokinsa kuma amininsa su zauna a waje ɗaya,yau shi ne Mudassir ke risinawa ya na gaishe shi a ɗarare gudun kada a ce ya yi wani laifin. Nan take ƙwalla ta taru a idanuwansa yana jin kamar ya kurma ihu. Da ƙyar ya danne abinda ke taso masa a rai ya ce.
"Aboki ina takardun da Man Sallau ya baka jiya ka bani."
Cikin rawar jiki Mudassir ya isa gaban Abdulwahab ya na duba jakarsa ya hau neman takardun. Wani irin tausayinsa ne ya kama Abdulwahab. Kafin ya dawo cikin hayyacinsa Iliya ya isa gaban Abdulwahab ya ce.
"Ai Alhaji ba zai iya baka waɗannan takardu ba. Domin kuwa jiya ya zaci na wuce gida sai wani mutum ya zo ya bashi takardun shi kuma mutumin ya bashi maƙudan kuɗaɗe. A nan ne ma na ji shi Malam Mudan ya na cewa ai shi ne silar arziƙinka to shi ma zai je ya kafa kansa ya gaji da wahalta maka."
Salati Mudassir ya yi ya duƙar da kansa sai ga hawaye na zuba daga kwarmin idanuwansa. Ya kasa kare kansa domin bashi da kalaman da zai yi amfani da su ya kare kan nasa. Addu'a ya dinga yi Allah ya kare masa mutuncinsa kada ya ba wa maƙiya damar tozarta shi a gaban amininsa. Iliya na gama zuba miyagun kalamansa a kunnen Abdulwahab ya ji saukar mari ta inda bai taɓa zato ba. Idanu ya zaro waje ya na kallon Abdulwahab da ya miƙe tsaye ya na huci kamar wani zaki. Cikin tsananin ɓacin rai ya ce wa Iliya.
"Ka je na sallame ka daga aiki a ƙarƙashi na,sallama ta har abada Iliya. Sannan ka sani idan har baka nemi tafiya akan abinda ka aikata ba alhakin bawan Allah'n nan da ni kai na ba zai barka ka ji daɗi a rayuwarka ba. Sallau maza ku je da shi ya ɗakko takardun filaye na ya baka ka kawo min,ka karɓe duk wani makullin shago na da yake wajensa. Ga wannan kuɗin sallamar ka ne,domin ba zan riƙe maka haƙƙinka ba."
Kuɗi ya ƙirgo a drawer dake kusa da shi ya miƙa wa Iliya da kunya ta gama baibayewa. Malam Sallau kuwa a gaba ya saka shi suka shiga shagon masu aikin,nan fa Iliya ya hau duba kayansa ya na neman takardun da ya adana a cikin kayan amma bai gani ba. Dariya Malam Sallau ya yi sannan ya zaro su daga aljihunsa ya na kaɗa wa Iliya a gaban fuskarsa ya ce.
"An faɗa maka kai kaɗai ne ka iya makirci? Kalle ni nan ka gani Iliya. Duk makircinka na dame ka na shanye,sai dai ni makircina akan irinku yake aiki. Dan haka maza ka kwashe tsummokaranka ka ƙara gaba,ka yi wasa da damarka ta zamowa ƙaramin attajiri a ƙarƙashin mutumin da dukiyarsa bata rufe masa ido ba,baya kuma yi wa na ƙasa da shi mugunta."
Cike da nadama Iliya ya bar shagon da jakar kayansa ya na nadamar abinda ya aikata. Sai dai a yanda ya ga ran Abdulwahab ya ɓaci ya san ba zai taɓa iya tunkararsa ba ballantana ya bashi haƙuri ya mayar da shi bakin aikinsa.
A wannan ranar Abdulwahab kasa ba wa Mudassir haƙuri ya yi. Domin bashi da bakin da zai bashi haƙuri. Sosai ya shiga ƴar wasan ɓuya da shi,baya fitowa daga ɗakinsa sai ya tabbata Mudassir ya bar gidan. Sannan baya dawowa gidan sai ya tabbata Mudassir ya yi bacci. A hankali matansu suka fara gane akwai matsala a tsakanin mazajen nasu har suka zauna suka tattauna akan lamarin. Dan haka a daren ranar Ammabuwa ta turke Mudassir a ɗaki ta hau tambayarsa abinda ke faruwa tsakaninsa da Abdulwahab.Murmushi ya yi ya ce.
"Ohh mata kenan akwai ku da sa ido,to hasahenku da ke da ƙanwar taki bai zamo gaskiya ba. Kun manta shi yana haɗawa da aikin gwamnati bayan kasuwanci? Sannan shi aikin gwamnati kamar aikin noma ne,a damina manomi ya fi aikatuwa da rashin lokacin kansa. Bayan damina ta ja baya ya girbe amfanin gonarsa sai aiki ya sauƙaƙa a gare shi. To haka lamarin yake a wajen Aboki. Ya sanar da ni cewar aiki ya yi masa yawa a office shi yasa kuke ganin kamar ba ma magana sosai kamar da."
Ajiyar zuciya mai ƙarfi Ammabuwa ta sauke kafin ta ce.
"Har na ji wani irin daɗi a raina Baban Maheer da ba saɓani kuka samu da Yayana ba. Allah Ya ƙara haɗa kammu ya bamu zama na aminci da amana."
"Amin Ya Allah Ummu Maheer."
Daga nan suka sauya salon hirar tasu har Ammabuwa ta samu bacci. Waje ya samu ya zauna domin kuwa yana so a wannan ranar ya kawo ƙarshen wasan ɓoyon dake gudana a tsakaninsa da abokinsa. Ya na nan zaune gyangyaɗi na ɗibansa ya ji dawowar Abdulwahab. Cikin sauri ya buɗe ƙofar ɗakinsa a hankali ya fita. A lokacin da Abdulwahab ya gansa sai da ya razana. Da sauri ya kafe babur ɗinsa ya ce.
"Ah Aboki baka yi bacci ba?"
"Ina fa zan yi bacci ƴan jarida sun fara ɗaukan rahoto akan irin zaman da muke yi da ni da kai a gidan nan?"
Cikin rashin fahimta Abdulwahab ya ce.
"Ƴan jarida kuma? Wa ya basu labarin abinda ya faru?"
"Mu je ƙofar gida mu tattauna."
Jiki babu ƙwari Abdulwahab ya bi bayan Mudassir suka je ƙofar gida suka zauna a dandamalin dake ƙofar gidan nasu. Shiru ne ya ratsa a tsakaninsu kafin Abdulwahab ya buɗe baki ya ce.
"Na rasa da wacce fuska zan kalli idonka na baka haƙuri akan abubuwan da na dinga yi maka a baya. Don girman Allah abokina ka yi haƙuri akan dikkan abinda ya faru a tsakaninmu. Har yanzu na kasa yafe wa kaina irin kallon da na dinga yi maka,da tozarci tare da kyarar ka da nake yi ma a kasuwa duk kuma a gaban mutane."
Murmushi Mudassir ya yi ya ce.
"Ban haƙurin ka ya karɓu Aboki,ina so ka sani tun kafin ka bani haƙuri na yafe maka,domin na san cewa zuciya bata da ƙashi,zama kuma ya gaji haka,zo mu zauna ne,kuma zo mu saɓa duk zaman da za ka ga ba a samun saɓani komai ƙanƙantarsa to ka bincika ɗaya yana munafurtar ɗaya ko yana yi masa zagon ƙasa. Sannan abinda ka aikata ai ba laifinka bane ziga ce irin ta maƙiya kawai ta shiga zuciyarka kai kuma ka yi aiki da ita."
"Hakane Aboki. Ka na da kyakkyawar zuciya. Allah Ya ƙara mana haƙurin zama da juna ya kare mu daga sharrin shaiɗanun mutane. Malam Sallau shi ne ya same ni har gida ya min bayanin komai,sannan ya yi min nasiha akan ruko da zumuncin da muka gina tin kafin wannan lokacin."
"Da yardar Allah sai mun samu lada da Aljannar da Allah ke ba wa bayinSa da suka yi zumunci dominSa Abokina. To wai ni ina ka je yau da na ga ka fi kowanne lokaci jimawa a waje?"
"Kura na je na gaida mutanen gida na kuma ga Salma. Na so na taho da ita Gwaggo Kande ta hana, ta ce sun kusa jarabawar common entrance na jira har ta gama sai na ɗauke ta ta min hutu mai yawa. A nan nake samun labarin wannan sakarar Samira ta gaji da jira na ta yi aure."
Dariya Mudassir ya yi sannan ya ce.
"Ai kuwa ka ga da ka aure ta ta gyara wa shagwaɓaɓɓiyar matarka zama a gidan nan."
"Allah Ya yi min tsari da auren Samira, a barwa matata shagwaɓarta ina son ta a haka."
Daga nan hira ta ɓarke a tsakaninsu har basu san dare ya tsala ba;sai da Mudassir ya fara hamma sannan suka shiga gida suka kulle kowa ya yi ɗakinsa.
Da asuba bayan su Abdulwahab sun tafi masallaci naƙuda ta kama Layuzah. Kafin su dawo ta haihu lafiya a gida da taimakon Ammabuwa. Ko da suka dawo suka ji kukan jariri sai suka yi zaton Maheer ne. Mudassir ne ya ce.
"Kai anya wannan kukan na Maheer ne kuwa? Ko dai Layuzah ce ta haihu?"
Da sauri suka ƙarasa shiga cikin gidan. Su na zuwa suka tarar da zannuwan da Ammabuwa ta goge jini da su a rataye a igiya tana ta shanya wasu. Gefe ɗaya kuma ga ƙatuwar tukunya nan ta ɗora ta na dafa ruwan zafin da za ta yi wa jariri da Mamansa wanka. Farinciki ne ya mamaye zuƙatansu sai suka hau godiya ga Allah suna tambayar abinda aka samu. Cike da murna Ammabuwa ta ce.
"Addu'a ta ce ta karɓu Maheer ya yi aboki shima kamar iyayensa."
Cikin tsananin farinciki Abdulwahab ya shiga ɗakin ya ga Layuzah kwance a gado ta tasa jaririnta a gaba tana kallo cike da so da ƙauna. Su na haɗa ido ta tashi zaune ta na miƙa masa jaririn da aka naɗe cikin zani. Hawayen farinciki ne suka sauka a kuncin Abdulwahab ya karɓi yaron ya yi masa kiran sallah,cikin rawar murya ya ce.
"Mahaifina Malam Musa ya yi takwara Layuzah. Ya Allah ka sa yaron nan ya yo gadon kyawawan halayyar masu sunansa. Allah ka yi masa albarka Ka raya mana shi akan tafarki madaidaici."
"Amin Ya Allah Baban Aabid."
Kallonta ya yi cike da tsokana ya ce.
"Tooo Aabid kuma?"
Kai Layuzah ta gyaɗa ta ce.
"Ƙwarai da gaske,ai na ji labarin yanda Abbanku yake da yawan ibada da dogaro ga Allah a wajen Gwaggo Kande. Shi yasa zan dinga kiransa da Aabid saboda shima ya yo gadon yawan ibada da tsoron Allah."
Waje Abdulwahab ya fita da yaron ya kai wa Mudassir tare da sanar da shi sunan da ya raɗawa yaron. Addu'a shima ya yi wa Aabid sosai sannan ya yaba da sunan da za a dinga kiransa da shi. Ruwa na tafasa Ammabuwa ta haɗa ruwan wankan jariri ta je ta karɓe sa a hannun iyayen nasa da ke ta murna. Tambayar Maheer Abdulwahab ya yi,sai Ammabuwa ta ce.
"Ai yau sarkin rikicin ya san ƙaninsa ya zo duniya ya zama babba. Ya na can yana bacci bai tashi ba."
Dariya suka yi gaba ɗayansu ta shige ciki ta fara yi wa yaro wanka. Ta na gamawa ta shirya sa da ɗaya daga cikin kayan jariran da Abdulwahab da Mudassir ke yawan siyo wa a duk lokacin da suka fita wata ƙasar ko suka shiga kasuwa suka gani. Ta na gamawa ta kai wa mazan jaririn ta kwashe wa Layuzah ruwan wanka suka shiga banɗaki
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 13