An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨🦋
BY RABI'ATU KABIR ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM)MIEMIEN HABIBI)❤️& AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI) ♥️
FULANI❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
PAGE1️⃣
Matashiyar budurwa ce yar kimanin shekara 17, take tafiya cikin natsuwa sanye da kayan makaranta, da alama daga makarantar boko ta taso.
Da sallama ta shiga gidan, tun a bakin kofa take jiyo irin muguwar ashariyar da wata yarinya take yi, wanda da alama fada suke yi ita da wani yaron a cikin ƴan uwanta.
Da shigarta gidan ba ta yi kasa a guiwa ba, ta kai ma bakin yarinyar duka, duka yarinyar bazata wuce shekara 8 zuwa tara ba, a razane ta dago, ta bude baki da niyyar ƙara yin wani zagin, amma ganin wadda take tsaye a gaban ta yasa ta yi sauri ta kame bakinta da hannu biyu tana zare ido.
Kunnenta matashiyar budurwar ta ja ta murɗe da ƙarfi tana fadin,
“Zainab, me nace miki akan zagi? shi Mukhtar din da kike zagin sa’an ki ne?"
Tuni idanuwan ta har sun cika da hawaye na azaba da tsoro cikin rawar murya tace,
“Addah dan Allah ki yi haƙuri, shine ya fara ɗaukan min abu kuma na yi masa magana ya dake ni”
Dara daran idanuwanta ta dago ta kalli inda yaron yake, dan kimanin shekara 10, wanda tun shigowarta ya sha jinin jikinsa, kallo ɗaya tayi mishi wanda tun kafin ma ta ce wani abu yayi saurin fadin,
“Addah wallahi ba gaskiya ba ne, ita ce na aje abu ta ɗauka kuma ba ma nawa ba ne, na sani abokina ne, shi ne ta lalata, na mata magana ta taka min rashin kunya.”
“Shi ne sai ka daketa ko?”
“A’a” yace yana zare ido.
“To sai ka mata mi?”
“Addah ki yi hakuri dan Allah,” ya fadi yana ƙasa da kansa.
Kwafa ta yi ta saki kunnen yarinyar tana fadin
“Kun yi sallar azahar?”
Tana binsu da ido alamar amsa take jira. Cikin sauri suka je suka dauko buta a bakin rijiya.
Ta ce, “Allah ya shirye ku ku kam”
Idonta ne ya fada kan Baba Zainu da take zaune tana faman aika mata da harara, tana aikin awara ta saidawa da suke yi.
Ɗan kauda kanta ta yi kadan tace,
“Baba sannu da gida.”
Dogon tsaki ta ja tana faɗin,
“Muguwa, sai bayan da kika gama cin zalin yara sannan kika ganni kenan? To wallahi ni dai ki fita daga ido na dan akan yarana zan iya yin komai, ke fitsarar da kika yi ma da dukan ki akayi ai da baki kawo yanzu ba.”
Ta faɗa tana kara banka mata uwar harara.
Ɗauke kanta ta yi kawai ta nufi kofar ɗakin su ba tare da ta ce mata komi ba, saboda ba ta da lokacin fitinar matar nan wadda ita komai za'a mata laifi ne, dan ma dai ba yar jarababbiyar tsohuwa bace ta ganta da faɗan ma sai yafi haka tana jin kila bata gidan ko tana can tana baccin asara.
Bata kai ƙarshen tunaninta ba ta jiyo muryar Hajja ta ɗaga labule tana fadin,
“Zainu wai hayaniyar menene nake faman ji? Lafiya ba za a bar mutum ya yi bacci ba?”
Cike da takaici zainu tace,
“Baba ni da wannan shegiyar yarinyar ce, daga shigowarta gida ta kama zaluntar yara. Ita dai idan tana gida yara ba su taɓa samun sakewa”
“Tsananin rashin kunya da rashin ganin girman nagaba da ita ai ba zai bari a takurata ba”
Hajja ta faɗi tana yaye labule ta fito tana ci gaba da faɗan,
“Kafurar yarinya ƴar nema ta dawo kenan! Kai mu dai wannan yarinya an haifar mana jafa’i, gaskiya Jafaru bai mani adalci ba da ya je ya auro mana wannan baƙar kadara, gashi nan da ta tashi mutuwa bata mutu ba sai da ta bar mana mugun iri”
A fusace budurwar ta waigo tana faɗin,
“Da ban shigo da niyyar tanka maku ba kaff din ku, amma Hajja saboda maganar da kika yi yasa dole sai na yi magana ki sani mahaifiyata ba baƙar kadara ba ce kuma da ikon Allah sai dai ki ga baƙar kadara a wani wuri ba nan ba”
Ta fadi tana juyawa tayi shigewarta ɗaki.
La masalli ala ina wuta!Hajja ta jefata, ta kama bambamin bala’i akan *Maryamah* tana zagin ta, tana faɗin bari Jafaru ya zo ya ɗau mummunan mataki akanta, Baba Zainu kuma na faman tunzurata.
Maryamah kam shigewarta ɗaki ta yi tana fadin,
“Kanku ake ji za ku yi ku gama, ni kam ai kun gama mani cin kashi in kyale a gidan nan wallahi”
Ranta duk a jagule ta cire uniform ɗinta ta daura zani da ɗan ƙaramin hijabi, ta dauki kayan wanka ta fito tsakar gida. Ruwa ta ja a rijiya ta nufi kewayen gida ta yi wanka kasancewar garin da zafi, daga nan ta dauro alwallah.
Bayan ta shirya ta fita tsakar gida ta nufi ɗan ƙaramin kitchen ɗinsu zata ɗauki abincinta, amma ga mamakinta babu, kamar ma dai ba a aje mata ba.
Ta fito ta kalli Baba Zainu tace,
“Baba abincina fa?”
“Ban dafa dake ba uwata” ta fadi.
Maryamah ta ce,
“Yanzu abin da nake so na sani shi ne kin dafa abinci ne baki aje min ba ko kuwa baki dafa ba gaba ɗaya?”
“Bakijin Hausa ne halan? Bakiji nace ban dafa dake ba?” ta ce tana kumfar baki.
Shiru Maryamah ta yi na yan sakonni sannan tace,
“Amma ba Baba ne ya kawo abunda aka dafa ɗin ba?”
Kafin a ba ta amsa Hajja ta hayayyako tana fadin,
“In shine ya kawo fa sai akayi yaya?”
Maryamah ta saki dan murmushi tace,
“Aikam indai Babana ya kawo abinci aka dafa a gidan nan tofa banga wanda ya isa ya hanani cinshi ba.”
“To ai sai ki bigeni ki kwata fitsararriya,” in ji Baba Zainu.
“Ba za a kai ga haka ba,” cewar Maryamah, “amma fa abinci sai na ci”
Ta fadi tana komawa kitchen ta fara buɗe kwanuka.
Tana fitowa da shi Baba Zainu ta yi karaf zata anshe tana fadin,
“Wallahi ba za ki ci abincin nan ba, In kin ci ita hassu in ta dawo taci me?"
Tayi haƙuri ko ta je gidan uban ta taci” ta bata amsa tana wuce wa.
Hankalinta kwance Maryamah ta shige ɗaki ta ci abincinta.
Haka ta bar Baba Zainu da Hajja suna mata tofin alatsine da muggan alkaba’i.
Bayan ta gama ta shirya cikin kayan islamiyya ta fito ta yi alwallah tana kiran Mubarak da Zainab su shirya, kowanne ya sanya kayan islamiyya su wuce.
Baba Zainu ta ce ba inda yaranta za su je, amma Maryamah ta ce dole su je makaranta, domin ita yayarsu ce kuma tana da cikakken ikon kula da su, dole ta taya mahaifinta tarbiyyarsu.
Tana faɗin haka tana ƙunshe dariya, ta san ta gama kunnata. Baba Zainu ta kunduma ashar tana kiranta mara tarbiyya, tana rantsewa dole sai ta ga bayan Maryamah a garin nan.
Ita kam Maryamah tace,
“Ai ga Allah na dogara kuma ba wani ɗan adam da ya isa ya yi mani abin da Allah bai yi min ba”
Ta tasa yaran suka fita ta bar su suna tsine mata...
Topha....
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
BY RABIA'TU KABIRU ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)❤️& AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
PAGE 2️⃣
Haka ta tasa kannenta biyu suka nufi islamiyya. Suna tafiya ta gamu da ƙawarta Aisha, wadda suke unguwa ɗaya tare da ita, ita ma da ƙannenta biyu amma duk mata ne. Suna tafe suna dan tattaunawa akan rayuwa.
Aisha ce ta kalleta tace, “Na ga kamar ranki a ɓace kawa, halan ke da mutanen gidanku ne?” ta faɗa tana murmushi. Numfashi kawai Maryamah ta sauke tace, “Ke da kika san komai, mutanen nan halinsu dai yana nan wallahi, sai dai Allah ya kyauta,” ta faɗa tana ɗan yatsina fuska alamar lamarin na bata takaici.
Aisha tace, “To ya za'ayi sai hakuri, kin riga kin saba da halinsu kam. Shekara 15 ai ba kwana biyar ba ne, tunda Allah ma ya sa kin dena masu wannan miskilancin naki, Kinaji kina gani suna cutarki ai da sauki”
Maryamah tace, “Ba za ki gane ba, dole ta sanya na buɗe bakina akan mutanen nan, wallahi gaba ɗaya su ba su da tunani, ba su san yakana ba sam”
“Allah dai ya kyauta,” cewar Aisha, suna shiga aji kasancewar har sun shigo cikin makarantar.
★★★
A can gida kuwa bayan fitar maryamah, haka ta barsu suna ta sababi, suna zage-zage akanta, wadda tana can tana karatunta ta barsu da ciwon baki.
A haka Baba Zainu ta yi awararta ta gama, tana ta saƙe-saƙe a cikin ranta na abin da ya kamata ta yi wanda rayuwar Maryamah za ta wulakanta ta koma ƙaskantacciya abar ƙyama. Haka dai ta dinga saka mugun nufinta akan Maryamah.
Hajja na gefe ita ma
tana nata tunanin sun mugun tsanar Maryamah, sun tsani su bude ido su ganta cikin gidan nan tana walwala, ba ma kamar yanzu da yarinyar ta zame musu ƙarfen ƙafa, duk ba suƙi su buɗe ido su ga ta ƙasƙanta ba, ƙasƙanta mafi muni a duniya, amma abin ya ci tura, ba kalan tuggun da ba su hada mata ba har a wurin mahaifinta, amma gaba daya yarinyar kamar mai aiki da rauhanai, sai ka ga ta tsallake, Duk da haka tana fatan wannan karon ta fada tarkon da za ta yi mata.
Haka ta cigaba da yan aikace-aikacenta ba tare da ta yi sallar azahar ba, bare la’asar, wadda ita kanta lokacinta ya ja. Da maganar da ake yi ma biyar har tayi, kuma da alama ba ta da niyyar yin sallar, ita kanta Hajjan da ba komi take ba, sai da aka kira la’asar aka idar a masallatai sannan ta tashi ta yi alwallah ta shiga salla, a haka hassu ta dawo gidan ba ko sallama, tana shigowa da mugun gudu ta watsar da kayan da ke hannunta ta fada bayi ba ko buta, ta fara sakin zawo mai wata mummunar ƙara har tsakar gida ana jiyo ƙarar, sai bayan da ta samu sukuni ne ta tuna bata zo da buta ba, nan fa ta hau ƙwala kiran “Babarmu, babarmu, kawo mani ruwa a buta”
Takaici ma hana Baba Zainu motsawa yayi, sai zuwa can da ta ji kiran ya isheta ta miƙe ta zuba mata ruwa ta miƙa mata.
Bayan ta fito ma ko tunanin wanke hannu ba ta yi ba, ta fada kitchen tana kiran “Babarmu ina abinci na?” Ai fa Baba Zainu ta kara hawa tana fadin, “Yo waccan tijararriyar yar ta ɗauke ta cinye, shegiyar yarinya mai kama da ‘ya’yan mayu” Bata rai Hassu tayi tace, “Ban gane ta cinye ba ah, haba Babarmu wallahi ba zai yiwu ba”
Baba Zainu tace, “To sai dai ki yi hakuri, tunda ga awarar nan na gama ko ki yanka ki soya ki fara ci kafin ki fita suyar, ko kuma ki jika garin kwaki ki sha tunda akwai”
Rasa abin fadi Hassu tayi ranta a bace tace ita wallahi ba za ta ci duka ba, sai dai Baba ta bata kuɗi ta siyo wani abu ta ci. Hakan Baba ta kunce bakin zani ta dauko wata dukunkunanniyar dari biyar ta bata tace, “Ungo ki dawo mani da canji” Hassu tace, “Nan fa ɗaya Baba, a wannan zamanin abin 500 nawa yake, ba ma isata zai yi ba”
Bayan fitar Hassu, Tasallah aminiyar Baba Zainu ta kwada sallama a gidan. Baba ta amsa mata tana fadin, “Yauwa Tasallah, kamar kin san maganar ki nake a raina wallahi, daman ko ba ki zo ba to nima zuwa dare za ki ganni a gidanki, dan wallahi na gaji da halin waccan shigiyar ɗiyar mai kama da ‘ɗiyan aljanu, mafita nake nema.” Ai Hajja na jin haka ta yi wuff ta fito ɗaki tace, “Allah dai ya yi miki albarka Zainu, ni kaina tunanin yadda za mu yi mu kauda ɗiyar nan nake. Tunda ita dai yanzu ba za ka cusguna mata ba shegiya, na rasa ya akayi bakinta ya buɗe ta dena tsoro da shakkar kowa, Ga Jafaru ba ya ganin laifinta, ba ya aiki sai fadin marainiya ce, Kai ai Maryamah ta haifar mana jaraba wallahi, ita kanta bata san ba da son raina na hada zuri’a da ita ba, amma da ta tashi mutuwa maimakon ta mutu da cikin jikinta sai da ta haifo shi.”
A dai-dai nan Malam ya zo zai shiga cikin gidan, mura da ya tashi da ita ne ya matsa masa ya sanya shi barin wurin sana’arsa ya dawo gida da wuri. Dakatawa yayi daga zauren, bai idasa shiga cikin gidan ba yana sauraren su. Su kuma suna ciki ba su san da zuwansa ba, mugun nufi ya toshe musu kwanyar kai, sun kasa gane cewa ko maganar da za su yi ba ta kamata su yi ta a tsakar gida ba, su dai kawai mafita suke nema.
Tasallah tace, “To Zainu ke ce nace in raka ki wurin wani malami a ɗai-ɗaita rayuwar yarinyar nan, amma shegen son kudinki ya hanaki.” Zainu tace, “Kinga Tasallah, ni fa ki aje maganar malamin nan a gefe mu yi wata.” Tasallah tace, “To ga shawara,” har suka hada baki wurin cewa “Mun ji ki, menene shawarar?” Ta ce, “Ina yaron nan ƘYALLE NA DUNA?” Suka ce “Eh.” Ta ce, “To kun dai sanshi, shi har matan aure ma haike masu yake, me zai hana mu sameshi mu bashi aikin haike ma yarinyar, mu fadi masa ya tabbatar ya mata kaca-kaca yadda ba za ta moru ba, ko ta rayu ta kasance bata da sauran amfani.”
Aikam suka yi shewa harda Hajja, ta koma kamar wata sa’ar su suna kashewa, ta manta cewa surukarta ce suke tare suna kullama jikar ta mugun nufi tsabar ƙiyayyar uwar yarinyar da tsanar da ta yi mata.
Jiri Malam Jafaru yaji yana shirin kadashi ƙasa, yayi saurin dafa bango yana kiran “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” a cikin ransa. Nan take ya ji kansa ya buga hade da ciwon kai mai tsananin gaske, wani gagarumin tashin hankali ya taso masa wanda da za a gwada jininsa a wannan lokaci, to tabbas sai an bashi gado.
A can cikin gida kam Baba Zainu ce ke fadin, “Kai amma kawata baki taba bani shawara danaji ta dari bisa dari ba irin wannan wallahi, na ji dadin shawararki fiye da yadda kike tunani. Yanzu ya kike ganin za a yi kuma yaushe abin ya kamata ya kasance, yau ko gobe?” Da sauri Tasallah ta tareta da fadin, “Ke dadina dake garaje, wane kuma irin yau ko gobe? Komi fa sai mun tsara shi dan kada mu je kwaɓarmu ta yi ruwa. Daga nan zuwa sati guda dai za mu yi komi ya kamma.
Yanzu gobe sai ki zo muje dabar su ƘYALLE NA DUNA ɗin, duk da dai shi ɗin mutum ne mai hatsari, amma ai biyan buƙata ta fi komi, shi da ke shiga gidaje ma balle ace ya samu wannan a ɓagas,” ta faɗa tana dariya.
Gaba ɗaya dariya suka yi suka hau shewa, Baba na fadin, “Zan so in ga wannan ranar, zan so ganin wannan yarinyar ta wulaƙanta, kinga daga ranar da ta ga ta koma fanko duk wani rashin kunya, jinkai da bakar gadara ai ta ƙare,” ta faɗa ceke da zumudi tana hasaso cikar burin nasu......
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
BY RABIA'TU KABIRU ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM(MIEMIEN HABIBI)❤️& AHMAD JAMIL AHMAD(HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
PAGE3️⃣
Cikin mawuyacin hali malam jafaru ya dafa bango, ya bar gidan saboda baya son su san da zuwansa, balle su yi tunanin ko ya ji su ne su canja ƙudurin su akan yar marainiyar shi kuma amanar shi, Haka ya fita jiri na ɗibar shi amma ya dake cike da ƙarfin hali ya nufi gidan aminin shi malam Sale.
★★★
A can makaranta kuwa, karfe shida aka taso su sai da ta biya ajinsu muktar a nan ta samu zainab a bakin ƙofa tana jiran shi, dan haka ta kaɗo kansu suka kama hanyan gida, ita da su Aisha, da suka zo dai-dai inda zasu rabu, Aisha ta kalleta tace, “Dan Allah ki kwantar da hankalinki ki kuma saki ranki, kinsan a duniya ba abunda yafi baƙanta ran makiyi sama da yaga murmushi a fuskan wanda yake ƙi.”
Kallon tayi na ɗan wani lokaci kaman bazata bata amsa ba sai kuma tace, “Hakane, inshaa Allah zanyi ƙoƙarin yin hakan nagode sosai da ƙwarin guiwar da kike bani, Allah ya barmu tare tawan ya baki ɗan amadudu musha shagali.” ta faɗa sakin murmushi.
Dukan wasa Aisha ta kawo mata, ta kauce tana dan murmushin gefen baki tace, “To sahiba da alkhairi.” Aisha tace, “Allah ya sadamu dashi,” tace “Ameen.” Nan suka rabu.
A gida ta iske su Zainab sun rigata isa kasancewar gaba sukayo da ta tsaya tana magana da Sahiba kamar yadda tace. Da sallama ɗauke a bakinta ta shiga gidan, duk da tasan ba amsata zasuyi ba, amma dole ne ta fita hakkin zaman tare, tunda tasan amfanin sallaman, ga tarin mamakinta, sai taji Baba ta amsata har tana cewa, “Da ita Maryamah kin dawo kenan.” Cike da dumbin mamaki, ta kalli Baban amma kasancewanta miskila, sai kawai ba ta ce komi ba sai eh da ta amsata da shi, wanda ya kara kular da Baban, wadda duk cikin shirinta ne, ba da tana gudun bata shirin ta ba da sai ta mata tass.
Ɗaki ta wuce, ta shiga da sallama, amma ranta fal tunanin, To anya kuwa lafiya? Meyasa yau baba ta amsata, kuma har ta shigo ɗaki bata ji tana sakar mata baƙaƙen maganganu ba da muggan zargin da ta saba?” Oho dai kawai tace tana me ɗage kafaɗanta.
A haka ta cigaba da canja kayanta bayan ta gama, da taga akwai kamar minti 40 kafin a kira sallah, yasa ta fita tsakar gidan inda taga Baban na aikin tuwo tace, “Kawo na ƙarasa miki" ta faɗa kamar bata son yin maganar.
Ansar girkin tayi, ta cigaba da yin inda take gudanar da komi nata cikin tsafta, ta tuke tuwan lumui ta kwashe, sannan ta maida miyar wadda daman Babanta riga da tayi jajjage ta daka daddawa kawai hadawa tayi, sai ta nufi bakin rijiya inda ta wanke tukuyan tuwon da baki bakinta, gudun kada yayi kanzo, ta cikata da ruwa ta aje a gefe, buta ta ɗauka tayi alwallah ta shige ɗaki.
★★★★
Da ƙyar malam jafaru ya iya kai kanshi ƙofar gidan malam sale aminin shi, Lokacin da yaje ya samu malam sale na alwalah saboda magriba da ta gabato. Ganin yadda yake tafiya yana hada hanya ne, ya sanya malam Sale saurin tashi, tare da riƙeshi yana fadin, “Subhanallah Malam Jafaru, lafiya kuwa? Yi a hankali” zaunar dashi yayi a gefensa aƙwai ruwa, ya ɗauka ya bashi yace, “Ungo maza sha”
Kaɗan malam jafaru yasha yace, “Alhamdulillah”
Kallon shi malam sale yayi yace, “Kaɗan samu natsuwa sai kayi alwallah, muyi sallah in muka dawo sai mu tattauna"
"To ba laifi nagode sossai Malam” shi kuma yace, “Kai haba menene abun godiya kai kuwa”
Da haka Malam, bayan ya ɗan huta, ya jawo buta yayi alwallah, suka rankaya suka tafi masallaci.
Bayan idar da sallah, Malam Sale ya kalli Malam Jafaru yana fadin, “Muyi maganar yanzun ne ko mu bari mu sallaci Isha sai mu fita gaba ɗaya?” Nan ma Malam Sale cewa yayi, “Ba laifi, mu jira har ayi Isha din ta yanda in muka gama magana sai na wuce gida,” ya fadi cikin ɗacin zuciya.
★★★★
Bayan ta idar da sallah ta zauna, tayi azkhar ɗin ta na mairaice, wanda daman a dai-dai wannan lokacin take yin shi, In ta samu sarari, tayi bitar karatun ta, in kuma bata samu ba sai tayi uzirin da ya taso mata, to yau ma dai, bayan data kammala azkhar ɗin, tashi tayi ta fita kitchen, taje ta duba miyan da ke ta faman tafasa, gidan sai ƙamshin daddawa yakeyi.
Bayan fitar ta ne tace ma Zainab tayi sallah, ta amsa mata da eh. Tace Muktar fa ta ƙara tambayar yarinyar, amsa ta bata da bai dawo daga masallaci ba.
Da haka ta kaɗa miyan, ta sauke ta gyara wurin, Bayan ta gama komai, ta ɗauki na Hajja ta mika mata ɗaki wadda ta sameta tana jan carbi irin jan da zaka rasa, wai mema ake karantawa, Nan ma sosai tayi mamaki yau da Hajja bata hantareta ba har ta aje mata ta fito, ta leka ɗakin Baba tace, “Ta gama itama wai yau har da mata sannu da faɗin tadai zuba nata koh?” Ai fa, na mamaki da tsoron Allah suka taru, suka mata rubdugu, a ranta take Anya yau gidan nan lafiyan mutanen cikinshi kuwa? Aje tunanin komi tayi a gefe, taje ta zuba ma yaran tace, “Su wanke hannu, su kuma tabbatar sunyi Bismillah kafin su faraci.” Sannan ta ɗauki nata tayi ɗaki.
★★★
Bayan an idar da sallar Isha ne, su Malam suka nufo ƙofar gidan malam sale suka zauna a shimfiɗar shi.
Malam Sale ya karasa cikin gida yace, “A ba yaro ya miko mishi abinci da ruwa yana tare da malam Jafaru ne" daga haka ya fita ya koma wurin shi.
Yace, “To Malam, mu bari mu ci abinci ko?” Cikin sauri Malam Jafaru yace, “Malam Sale, abun da ke tafe dani wallahi, ko