ba aduniya bare kuma sati, idan Allah yayiwa Manga tsawon rai ka sanar mata ta riqemun yara na amana,kuma ban yarda akaimun su wurin Ammyna ba koda anganta, idan kaga Ammy na kace da ita nayafe mata amma idan tayi qoqarin rabar yarana ta koya musu muguwar aqida ban yafe mata ba, babu ita babu yarana ko bayan raina,kuma itama ta yafe ni" rufe mata bakinta yae yace
"Haba mana Huddy inshaa Allah bazaki mutu ba zaki tashi garau, ciwo aiba shi bane mutuwa" murmushi tamasa cikeda qauna lokaci d'aya zafafan hawaye suna kwaranya daga idanta tace
"Yaa Ali nasani ba'a gayawa bawa ranar mutuwar sa amma kalli fa yaa Ali ko fitsari da kashi a kwance nake yinsa,kalle ni ko yanzu meye marabana da gawa banda numfashi banafa iya tashi, yaa Ali kalli sumar kaina yanda ya dawo ba komai ajiki tamkar wata tsohuwa ka tabbatar nakai mataki na qarshe a cancer,bazan rayu ba yaa Ali taimako daya zakamun shine kamun adu'a har bayan ranka adu'ar ka kurin nakeso, kuma dan Allah banida gadon komai dukiyata ka bayar a gina rijiyoyi da masallatai a qauye yanda na taho duniya a tsirara haka zan komawa mahaliccina gado fitinane, sadaqatul jariya kurun zata bini a kushewata ka taimaka kamun wannan" hannunta ya riqe sosai yana hawaye yace
"Nasan bazaki mutuba Huddy inshaa Allah zamu rayu cikin aminci ki dena diremun wa yannan bayanan dan Allah" numfashinta ya soma rawa wanda hakan ya sanya yaje ya kira doctor aka dara mata aux sabida ya taimaka mata wurin numfashi, a haka kuma ya barta da manga wanda koda suka dawo da doctor bata numfashi ashe mutuwar kenan wata razananniyar qara ya saka ya qara matse Manga gagam wanda seda manga ta firgita ya furta
"Na tausayawa hudaisa sabida batasan mutuwa,sam bata shiryawa mutuwar taba ta sanar dani tsoro takeji bataso ta mutu, yaa Allah ka gafartawa matata Allah mata rahama" rarrashinsa manga ta somayi seda ya dena kukan sannan yabar gidan gaba daya....
*Bayan wata shida*
Zuwa yanzu su Manga sun faulawa Allah lamuransu game da rashin huddy ta riqe yaran huddy da gaskia, madeena kuwa bazaka tab'a cewa wai bakwaini aka haifeta ba, yanda ta girma tayi b'ul b'ul da ita gwanin sha'awa.....Shirin tafiya Niger suke hutu sabida sosai suke buqatar ganin gida dukkansu....
*Nigeria*
Gidan Manga dake Arqillah suka sauka ita da ahalainta, se murna suke sunzo gida, kayan ciye ciye kuwa gasunan an wadatasu dashi, Bayan sunci sun qoshi suka soma baccin gajiya, har yara, se washe gari suka shirya zuwa su gayar dasu ummu da kuma su Innoh.....Gidan sarki suka fara dira sunsha tarba me kyau acan ma, ummu tace
"Ni kuwa Auta naga se wani sussune kai kikeyi duk kin wani girma an dena shagwab'a yanzu kuma kunyana akeji?" murmutayi tace
"Ba haka bane ummu gani nayi ga yarana se kuma su ganni ina shagwaba" tae maganar cikin shagwaba wanda ya baiwa kowa dariya har Ameen yace laaa Ummi shagwaba kike kema, amma kullum sekina dungurin madeena wai kukan banza ne da ita da shagwaban tsiya" dariya suka qara sakawa ummu tace
"Gwara da ake dungurin kishiyata, dama anzo kwacen miji kuma kurwarshi kur" kwanciya akan cinyar ummu Manga tayi tace
"Uwa me dadi kaga ni bazan koma saudia ba idan kun tashi ku tafi abinku" bece komai ba se Ameer ne yace
"Idan mukace Amusement park bazaki hau lilo da dragon ba kuwa" kowa se ya kwashe da dariya Ameer an qara samun baki shekara shida se wayon tsiya, shafa bayanta ummu tayi tace
"Auta kinsan yanzu kin qara girma ko, kalli yanda kike neman b'allamun qafa dan Allah, lukuta niki d'agani dan Allah" murmushi tayi ta qara lumewa ajikinta tana cewa
"Kai ummu yanzu nice lukuta,tun yaushe rabon daki sakani a idanki,gwara ki barni in biya bashin danaci" rankwashin ta tayi ta dafe wurin tana shura kafa yayinda Abin ya matuqar burge Ali Abbas yakuma baiwa Ameer harma da Ameerah matuqar dariya suka kuwa dara ummin su tana shagwaba irin na yara...sun wuni suna raha abinsu se la'asar sakaliya suka bar gidan zuwa gidansu innon Iroh Baban Manga....Bayan gaishe gaishe aka kuma shiga hirar rabo, anan ne Baban Manga ke sanar musu mahaifinshi yazo ban haquri kuma komai ya wuce dan Haka su shirya zuwa Niger kai Madeena aganta tare dashi zasuje kuma bazasu dawo ba shida innoh kasancewar an saka rana mahaifinshi zeyi murabus shiya hau karagar mulkin.....sunyi murna matuqa daga haka aka tsaida ranar tafiyar....
*Niger republic*
Kowa seda ya hallara aka daura mahaifin Manga kan mulkin qasarsu ta yamai, inda abin Mamaki Mahaifiyar Manga ciki ne da ita harna watanni hudu amma bata gayawa kowa ba se manga acewarta kunya ma takeji wlhy, haka dai akai shagulgula irin na al'ada masu ban sha'awa aka watse, mahaifin Baban Manga ya baiwa me martaba sarkin musulmi da ahalinshi haquri kuma komai ya wuce......
Tafiya takeyi a sukwane,tayi baqi qirin zaka rantse da Allah ba Ammyn su huddy bace yanda ta lalace, a wani gindin ice ta zauna, a garin na Akrah dake cikin birnin Ghana se kallon motocin dake shawagi takeyi, sam bata iya tunano rayuwarta ta baya ko sunan ta, gabaki daya ta fita hayyacinta kowa kallon mahau kaciya tuburan yake mata, Mahaifinsu huddy daya taho gana siyan wasu qarafa acan ya hangota zaune tana zare idanu, kallo daya ya mata qirjinsa ya doka, me taxi din ya tsayar ya fito daga cikin motar yaje gareta,kallonshi tayi amma sam bata gano shiba, gashi dai a kasan zuciyarta tanaji tasan wani abu gameda wannan mutumin amma sam ta kasa gane komai, shine yayi qarfin halin kiran Allah
"Asabe kece anan, haukace wa kuma kikayi?" yana fadar sunanta komai ya soma dawo mata ta soma zare ido tana mai magana tsawa ya mata yace
"Tunda naji mugun abinda kika aikata ne ya dawo miki na denw nemanki, ki sani tun na sakeki bakida igiyar aurena akanki,sannan kuma yarki hudaisa Allah ya mata rasuwa tun watanni takwas da suka wuce, tace kuma kimata gafara, ni kinga tafiya ta....." hannu ta daura akai ta zunduma ihu yana sauri ya shige taxi din yabar agun kokadan baze iya taimakon wamda be taimaki kanshi ba shikam....mdaya dawo ya sanar wa kowa yanda sukayi iyayenta ne sukaje nemanta suka dawo da ita amma maganin duniya sunyi bata magana se idan ta haukace...mm
*Bayan shekaru biyu*
Kallon d'uwawun Manga Ali Abbas keyi har inda ta bacewa ganinshi, tashi yayi yabi bayanta a dakin data shiga yace bayan ya zauna yana shafa duwawun dayake matuqar daukar hankalin sa
"Manga wai kinsan kin qara budewa, ni arayuwa inasan jikinkin nan wlhy, kina burgeni sosai, bana iya dauke idona daga gareki duk sanda na ganki" murmushi ta sakar masa tace tana shafe kwantaccen sumar qirjinsa
"Yaa Ali aini takace, kayi yanda kakeso da jikina" sirirn hancinta yaja yace
"Kinga ni naga nawar inmiki ciki ma wlhy, yau dai sena miki ciki, ai madeena ta zama budurwa kusan shekaru uku fa,sisin ya isa haka" zillewa tasomayi ya soma mata cakulkuli tana qyalqyala dariya, samun sa'ashi tayi ta haye ruwan cikinsa tace
"Nice da kaina zan ma ciki yau, ka kwanta abinka kawai" dariya suka kwashe dashi dukkansu.....
Tammat bi hamdillah.......
Wanda suka aiko saqonni da wanda sukamun waya akan aqarawa Ali Abbas tsawo don Allah suyi hakuri wlhy abubuwan ne sukazo da haka basan raina bane,bakuma naki daukar shawaranku bane kuna raina
Suby ladan kece ta farko
Pheey tawa ina matqar yinki
Hafsatul Elham ina qaunarki besty na
Halima Umar keta dabance my fulani bata biyunki
Phertyma zahra babbar qauna ta Allah ya nunamun aurenki
Maman khadyy ubangiji ya kawo mana zuri'a rayayyu kuma muminai
Kdeey ke kikebin pherty inayinki sosai sosai
Doughter Allah ya kawo miji na gari kuma yabaki hakurin rashin mijinki na baya
Duk wanda ban anbaci sunanshi ba yana raina......naso inja lokaci me tsawo banyi rubutu ba,amma akwai wani saqo akwai saqo me dauke da tarin ma'anoni me ma'ana wanda sam zumudi baze barni naja lokaci me tsawo batare dana isar da wannan saqon me matuqar muhimmanci ba....Amma fa saqon dole se maganganu masu nauyi sun shigo aciki kazancewar yanayin saqon dole batsar itace agaba, Allah ya gani salo da tafiyar rubutunce zatazo da haka bani ba, so duk wanda yasan ze zageni karma ya soma bi,dan gaskia zan iya shari'a dashi ko waye.......Na sake maimaitawa saqon zezo ne da maganganu masu nauyi kuma wanda ze amfani kowa so bazan hana kowa bi ba......
Zaku iya ganin shi yau ko gobe ko anjima koma yaushe idan Allah yayi......
Mom Nu'aiym ke muku fatan alkhairi.
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 16