bace, dukda yake na sani rabuwa da gida ba dadi, koda a kadunan aka kaiki kuwa bare a skt ma, amma haka aure ya gada sekinyi hakuri kinji?" gyad'a msa kanta tayi yace
"Tashi muje zan miki wanka ne,nasan kin gaji" zaro ido waje tayi gaba daya,labbanta na motsi amma kalmomin datakeso ta fad'a harshenta ya gagara sarrafa haruffan dazasu aiko da kalmomin, kasa haquri yayi ya had'e bakinshi da nata, kasa hanashi tayi sabida tajima tana kwad'ayin wannan yanayin datakeji, yafi 2 mnts yana murzar bakin daya jima yana bashi sha'awa kanya saketa yace cikin isa
"Banasan gaddama, wanka zan miki, na tabbatar kinsan cewar ke d'innan matata ce bawai haka kawai zan miki abu ba" batace komai ba amma bata motsa ba....da kanshi ya miqar da ita tsaye sannan ya sanya hannu ya zare mata zip na doguwar rigar datake sanye da ita, atake ta fadi a qasa ,ta dawo daga ita se skirt,pnt da bra,take jikinta ya soma rawa ma, towel ya dakko ya sanya a kafadarshi sannan ya had'e jikinshi da nata ya soma b'alle mata bra d'inta yayinda yake amfani da gargasan gemun sa yana shafa mata bayan wuyanta dashi...... Wani iri Huddy keji tama rasa abinyi se hawaye kawaii cire ta yayi sannan ya cillar a qasa ya dawo da dubanshi zuwa gareta, da sauri ta runtse idanta ,murmushi yayi,kunyarta na burgeshi sannan ya ya sanya hannunshi ya lalubi waist dinta yasoma zare mata under skirt har qasa ya kaishi tana nan tsaye kaman statue ba laifi ya fada a zuci tanada qira me kyau, hannu yakai domin zare pants dinta da sauri ta daura nata hannun akan nashi, murya na rawa tace
"Ba gaddama nake maka ba yaa Ali,taimakona zakayi ka ragemun wannan kayan nauyin dake kaina, ka barni da wannan karna saka maka ihu" murmushi yayi ya daura mata towel daga qirjinta sannan yace
"Tunda kinji tsoro jeki kiyi wankanki, inyaso ki dauro alwala dagacan.....wani sanyin dadi taji a ranta ta juya da sauri zuwa toilet, koda ta dawo baya dakin, da sauri ta shirya cikin wata lallausan rigar bacci pink color....Tare suka sallaci sallar nafila sannan.. Suka kwanta, gabaki daya juya masa bata tayi ta nemi nutsuwarta ta rasa, birkito ta yayi ta fuskanceshi gaba d'aya, ya sanya d'an yatsa yana zagaye lips d'inata da suka dad'e suna d'aukar masa hankali, ya matsu ya kasance tare da matarshi kasancewar sa bame neman mata ba dacan, cikin wata murya dabata tab'a ji yayi magana da itaba ya kira sunanta
"Huddy?" bata d'ago ta kalleshi ba, cikin nauyin baki tace "Na'am yaa Ali"
"Inaso ki zamto mace ta gari,uwar 'ya'ya ta gari, Amintacciya wacce zata qaunaci mijinta dan Allah, kiyi supporting d'ina akan dukkan komai ki soni kuma ki qaunace ni, Nasan a tunaninki bana sanki sabida auren had'i mukayi, sam ba haka bane, ina sanki tun ganin farko huddy, dan Allah ki riqe amanar aure" murmushi tayi tanaso tayi magana amma sam ta kasa furta komai sabida tanajin yanda yake magana yana mata wasa da en yatsunshi akan cikinta, gano yayi gaba d'aya saqon daya ke kokarin isar mata ya gama saukar mata da kasala gaba d'aya, bakinsa ya cura a nata ya soma sarrafa harshen ta a hankali, kasa hanashi tayi gaba daya ta sake masa ragamar ta, ranar kuwa yaa Ali ya mayarda Huddy cikakkiyar 'ya mace, yaji matuqar dad'i daya sami matarsa a tsare kamar yanda ya kame kanshi haka ya samu matar data kare masa mutuncin ta har gidan aurensa.....
*Bayan wata shida*
Har wannan lokacin ba gadanga ba labarin sa, gabaki d'aya iyayen ta sun tashi hankalinsu, sabida yanda taketa rama,yaudai Baban Manga da Inno ne zau e a tsakar gida suna tattaunawa
"Innoh gaskia ni al'amarin yaron nan gadanga ya gama tsoratar dani,yanzu ace ko waiwaye, idan da mutuwace wlhy munji labarinta yanzu, amma ba wannan, ni ina ganin kawai Allah a abki fir'auna a zuci ya mana" kan Innoh tai magana har manga ta qaraso wurin aguje
"Haba Baban Manga dan Allah ka kyautatawa Mijina zato, wlhy na tabbatar gadanga baze tab'a aikatamun hakan da gangan ba, iya tsawon zamanmu dashi sati uku zallar soyayya ce a tsakanin mu da kulawa, ko sanda yace zeje dani ya tafi wlhy sabida rigima na yamun wayo, kamai Adu'a idan yana raye Allah ya bayyanar dashi idan kuma ya mutu Allahu ya bamu ilimin sanin hakan, na tabbatar gadanga ze dawo gareni" nisawa Baban manga yayi
"Mangan Inno ki sani koni nan wayannan kalaman iya bakina kawai suka tsaya amma sam zuciyata bata aminta dasu ba, sabida nasan halin Gadanga halinshi ba haka yake ba, bana fatan mutuwa yayi, ammafa ki sani a qa'idar aure idan namiji ya tafi abinshi da gangan harna tsawon watanni 4 tofa babu aure,idan kuwa fad'a yayi toko shekaru hud'u be wa'adin indai muddin be dawo ba dole a raba auren ki auri wani, wannan tsarin ba nawa bane manga na musulunci ne"
Tana kuka tace "Niko shekaru dari gadanga zeyi zan jirashi na tabbatar ze dawo gareni, dan Allah Baban Manga ka dena fadar zancen raba auren nan,wlhy inasan mijina" tausayinta ya kamashi yace
"Allah ya zab'a miki mafi alkhairi Manga, aalhj ya sanar dani ki shirya kayanki jibi zakije sokoto hurin hudaisa, dukda yake nasani cewar bakwa shiri amma haka zakiyi hakuri, a yanda naji batada lafiya ne, kuma ma acewarsa bazakine wurinta matsayin er aiki bane zakijene a matsayin er uwarta ya sanar da ita hakan, zance na gama kije da komai naki na karatu zaki soma makarantar gaba da sakandire acan kan Allah ya bayyanar mana mijinki ko labarinshi, banso hakan ba Amma bazan iya masa gaddama akan lamuranki ba, sabida Alhj yayi duk yanda akeyi ya d'auke ki matsayin 'ya, ki kame kanki ki sani fa danigiyar auren wani a kanki bawai sagaga zakina yin wannan haukan nakiba.... Kuka kawai take, batason zuwa sokoto itakam tafiso ta zauna gida tayita jiran gadangan ta amma yata iya batada zabin daya wuce bin umarnin iyayenta......
*Sokoto*
Koda Manga tazo gari mamaki tayi ganin cewar har cikin jikin huddy ya fito, sedai fa tayi baqi sosai ta rame har tsoro ta baiwa Manga, tunda tazo gidan bataga Ali ba, kodai dan bata fita ko ina bane ohoooo....
Satinta biyu da zuwa wani yammaci tana zaune sega Ali Abbas yazo parlor d'in, tashi tayi ta sunkuya ta gaidashi, ga mamakin ta wannan wasan dayake mata sam beyiba, fuskarnan a hade alamun ba wasa yace da ita
"Ke Manga kikace da huddy bakyason course da aka baki? Me kikeso a miki to? Late admn fa na sanya aka baki, karatun dole sekinyo zab'i a kanshi? Idan kikace dole se kinyi Law idan kuma ba alkhairi bane a gunki fa? Med lab aka baki kuma shi zakiyi, idan kinje ki bari inga sakamako mara kyau kiga yanda zamuyi dake, akwai driver daze kaiki jami'ar gobe ki fara registration" lokaci d'aya taji qirjinta ya doma kuma ta soma wani tsoron shi, muryarta na rawa tace
"Kayi hakuri yaa Ali inshaa Allah zanyi" miqo mata kudi yayi yace
"Ungo wannan keba indigen din nanne dake ba, na kd ne, zaki biya registration sannan kuma ku biya ta bank dashi, na sanar masa ya kaiki gt ki bude acc goben" godiya ta masa sannan batare daya saki fuskar ba ya wuce abinshi.....
Tun daga ranar da ya bata kudin bata sake ganin shiba gashi dai takan jiyo muryarshi sabida part dinsu take zama amma sedai ta jiyo suna raha abinsu shida matarshi, yaune ranar farko dazata soma zuwa lecture koda ta fito wuraren 7 ta ganshi zaune Huddy tayi matashin kai da cinyarshi yana shafa sumar kanta a hankali, kawar da kanta tayi gefe sannan tace
"Yaa Ali ina kwana, Aunty huddy ya jikinki" be amsa gaisuwar tba huddy tace "Naji sauqi Manga,skul din zaki tafi?" kan tabata amsa ta tsinkayo babbar muryarshi yana cewa
"Zonan Manga" zagawa tayi a kunyace tace "Gani" seda ya danja fasali sannan ya saki muryarshi dake da fad'i yace
"Manga ki sani kinada aure akanki, sannan dukkanin abinda kika aikata na batanci Allah yanaji kuma yana gani, kada kiyi amfani da damarki ta ya mace ki cuci igiyar auren dake kanki, inshaa Allah mijinki ze dawo gareki ko yaushe ne, duk abinda kikayi me kyau masarautar nan kikayiwa, idan kinyi mara kyau ma haka, motar da zakije skul da ita ki dawo da ita duk tanada tambarin nan gidan, driver daze kaiki ma na nan gidan ne kowa ya sanshi, dan Allah ki rufa mana asiri ki kare mutuncin aurenki" shiru kawai tayi masa yaci gaba
"Nine nake kula da komai da komai na karatunki, idan kina buqatar wani abu ni zaki tambaya, seki sanar wa huddy buqatunki ni kuma nasan zata sanar mun" godiya ta masa sannan ta tashi ta miqe zuwa skul din....
Allah sarki rayuwa haka Manga ke rayuwa agidan batare data samu wata walwala ba, gabaki d'aya tayi sanyi sedai ba laifi tana karatunta, bata wani ganin Ali Abbas agidan, yayinda kuma sam huddy bata mata wulakanci ko kadan, suna zaman lafiya tadai kula kaman huddyn batada lafiya sosai sabida yanda ta yamutse....
Sana'ar kukan ta kwanta parlor tanayi yau ma ita kadai sabida tasan ba kowa a bangaren huddy taje gaisawa da surukanta, sambatu takeyi
"Yaa Gadanga ga sauarari kukana a duk inda kake, ka gane ina cikin tashin hankali, yaa gadanga yau shekarana d'aya ban gankaba, kasan kuwa abinda nakeji, kasan rashin ganinka meyake sakani ji, bazan manta kaba arayuwa, banida sauran amfani idan baka nan yaa gadanga dan Allah ka taimaki wannan baiwar Allah ka bayyanar mana kanka" ta qara rushewa da kuka me ban tausayi.....Ali Abbas dake bayanta kuwa dafe kanshi yayi dake sara masa, da qyar ya iya d'aga kafarshi zuwa d'akin shi har wannan lokacin batasan da zuwanshiba
"Yaya zanyi da Manga ni Ali, ina zankai wannan tausayin datake bani? Mezan iya yi mata? Mesa arayuwa zuciya batamun adalci ba, tayaya zataso manga matar wani?? Tayaya zan kasa sukuni akan ta, tayaya zan zamto mara amfani agareta, yaya zanyi inga Manga ta dena kuka?? Yaya zanyi inga Manga tana walwala kona samu nutsuwar zuciyata, yaya zanyi da qaunarki Manga????? Ya akayi nayi saken da wani ya rigani mallakar zuciyarki? Kasa hakuri yayi kurun ya soma hawaye......
Hmmmmm
Mom Nu'aiymm
[7/6, 8:07 AM] +234 706 571 7620: *Haske writer's Asso.(home of expert and perfect writer's)*
*👑ALI ABBAS 👑*
Billy galadanchi
Sadaukarwa gareki qawa ta gari *Fulany saddy*
*Wannan shafin sadaukarwa ne gareki ke kadai Jamila sani, kinfi kowa san littafin Ali Abbas, Allah yabar qauna*
*Gareku mom Areef, Rukeey,da kuma fatima Adams, wannan shafin tukwici ne a gareku, sabida k'aunar da kuke nunawa wannan littfin, Ali Abbas yace a gaidaku*
04
Da sallama Huddy tashigo parlor din,yanayin data tadda manga aciki ya bata tsoro, da sauri tayi kanta ta rungume tana neman sanin dalilin kukanta haka tamkar zata shid'e
"Manga Lafiya dai, menene? Koni na miki wani abinne ban saniba?" tana kuka tace
"Aunty Huddy yaufa shekara d'aya amma ko labarin gadanga babu, ina kuke so in saka rayuwata wlhy ina matuqar so da kewar mijina, mutum me tattali da kulawa dani, me lurar dani inda duk na kuskure, yaa huddy idan har ba'aga Gadanga ba banga amfanin rayuwata ba" da sauri ta toshe mata baki da hannunta
"Haba Manga, yaya zaki so kauce hanya akan d'an Adam, idan kikace bakiga amfanin rayuwarki ba idan bashi ashe rayuwar dakikai a baya kenan batada amfani kafin zuwanshi cikin rayuwarki,karki kasance cikin mutane wayanda basa karbar uzurin kaddarar datazo musu mana? Ki godewa Allah mana da tarin tulin ni'imomin daya wadatar dake dasu, kinsan ko koda lafiyarki aka barki kina cikin ni'ima? Wata tana tare da mijinta amma sam baida amfani agare ta,baya kula da cinta bare sha ko suturu, ita ke ciyar da kanta da yaranta, iyaye ko en uwanta basuda karfi, yanzu ashe ba ni'ima bace kinada masu tallafa miki dukda kasancewar sam mijinki be bar miki komai ba, idan mutuwa yayi akwai tanadin da madaukakin sarki ya miki, idan kuma yana raye adu'arki bazata fad'i qasa banzaba, yanzu ki kalleni da kyau ki gani Manga tsaye kawai nake amma sam banda lafiya kuma karki zata wasa ciwone dabaze warke ajikina ba,sedai na mutu dashi ni kuwa me zance?? A ganina ba san kaiba manga jarabawa ta tafi taki dukkuwa dayake nasan ciwo ba mutuwa bane, nida nake da wannan ciwon nayi imani zancen likitoci bawai dole ya zamto bazanyi rayuwa me tsayi ba, sabida tsarin Allah yafi na kowa, dan Allah ki fauwalawa Allah lamuranki Manga" shiru tayi sekuma jikinta yayi sanyi ta qurawa huddy ido tace
"Aunty kuma kema bakida lafiya? Mesa kikace bazaki warke ba? Meyake damunki?" murmushi huddy tai
"yanzu ki tashi kije kiyi wanka kiyi sallah lokaci yayi, kukan ya isa haka ki mana adu'a dukkanmu plss" jiki ba qwari ta miqe zuwa cikin dakinta,yayinda huddy ta miqe tana share kwallar daya zubo mata
Tana shiga dakinbta tarar da Ali Abbas ya sunkuyar da kanshi bemasan da zuwanta ba, zama tayi ta dafa shi tace
"Haba Yaa Ali? Mesa a rayuwa zaka kasa yarda da qaddarar da Allah ya daura mana? Dacen danake rayuwa batare da ansan da ciwon ajikina ba likitocin ne suka rayani? Yaya yanzu dan sunzo da zancensu na banza zaka gagara yarda da qaddara, idan kana hakan ni kuwa mezanyi? Kaine fa babba, ashe ba dagaske kake rarrashina ba kenan, bayan idona seka zauna kanata faman tunani, toka sani ni wlhy nafi yarda da cewar wannan likitan dayace bazan rayu da tsayiba seya rigani mutuwa sabida rayuwa da mutuwa a hannun Allah suke, ni kagama naji sauqi kafin su gano wannan ciwon ma ai kaga ni bantaba kwantawa ciwo ba bare in yarda da shirmensu" shiru yayi yana kallon ta yarinyar nan akwai imani a tattare da ita, ciwon cancer ba abin wasa bane yaga ita ko a jikinta, tundaga zuwa awo aka gano cancer din amma taqi ta nuna damuwarta sam, likitoci sun sanar masa ba lallai ta rayu da tsayi ba, bemasan taji ba se yau kodan kasancewarta wacce ta karanci aikin likitanci ya sanya tasan komai dan shidai yasan be sanar mata ba sam, tausayinta da kanshi yaji sabida besan yaya rayuwa zata kasance masa ba idan ba huddy yayi sabo da ita me tsananin gaske,yana kuma san matarshi tsakaninshi da Allah mabuwayi, rungumeta yayi yace
"Na sani huddy inaji ajikina wlhy bazaki mutu yanzu ba, likitan me shi ai besan gaibu ba, kuma dukiya ta sedai inga bayanta wurin nema miki lafiya da yardar Allah" qara rungumeshi tayi sosai sun jima a haka kafin tayi yunkurin shiga ban daki, wanka tayi sannan ta sauya kayan jikinta ta sallaci sallar magrib wanda koda ta idar baya nan ga alama masallaci ya tafi.....
* Wani yammaci naquda ya tasowa huddy batare da kowa ba, tasha wahala sabida kasa zuwa koda parlor tayi ta ciro wayanta caji, haka ta wuni dakin tana jiwo rurin wayar gashi Manga tana school, Ali Abbas yana ganin yayi ta neman wayarta baya samu ya kamo hanyar gida, tare suka shiga part d'in da Manga kallon juna sukayi lokaci d'aya qirjin manga yayi wani irin mugun dokawa. "Mesa nake ganin tamkar na saba gauraya idona dana yaa Ali aduk sanda na sanya idona da nashi,mesa qirjina yake linka luguden dayakeyi aduk sanda na ganshi?" wannan itace tambayar da manga kewa kanta a zuciyar ta, yayinda Ali ke cewa a ranshi
"Mesa arayuwa nakasa dauke idona akan Manga? Tayaya zuciyata zataci gaba da nunamun abinda baze taba yiyuwa ba? Mesa nakejin tausayinta yaya zanyi da raina?" A tare suka had'a baki wurin cewa juna "Sannu da zuwa!" batare sun shirya fitar kalaman ba murmushi suka sakarwa juna a tare sannan tace
"Sannu yaa Ali ya aiki?" amaimakon ya ansata seyace
"wannan gayun beyi yawaba Manga kalli qaramin mayafin dake kanki? Plss kisani akwai aure a kanki, ki sauya yanayin fitarki" duqar da kanta tayi tace "Allah yaa Ali hijabaina ne sukayi datti, wannan ne karon farko danaje school da mayafi ma" gyaran tsayuwar shi yayi yace
"Mesa?" bata fahimceshi ba tace "Na'am?" jan gashin gemunsa yayi yace "Mesa sukai datti?" sadda kanta qasa tayi tace "Sabida ban wanke ba" juyawa yayi ya soma tafiya
"k'waya nawane dake hijaban?" murmushi tayi "k'waya hud'u ne"
"sunyi kad'an gobe zakuje da Amadu driver kasuwa ki dinka k'waya ashirin" da sauri ta kalleshi tanaso tayi magana amma yatafi da nisa abinshi dole tabi bayanshi zuwa ciki, tana qarasawa tajiyo salatinsa, bin bayanshi tayi zuwa d'akin da sauri ganinshi tayi rungume da huddy da sauri tayi kansu, ita ta tayashi suka kwasheta zuwa asibitin uduth......
"Lafiya lau ta sauka cikin sa'o i uku ta sunkuto yaronta Namiji me matuqar kamanni da ita, murna awurin Ali Abbas ba'a magana, musamman data sauka lafiya,lafiyarta itace agaba da komai a wurin shi yana matuqar san matarshi ba iyakaaa....
Ranar suna yaro yaci suna Ibrahim, ana ce dashi Ameer, gabaki daya san duniya Manga ta dauka ta sakawa yaronnan, sabida ansaka masa sunan mahaifinta...
Huddy ta soma aikinta da asibitin uduth a b'angaren mata dama wannan fannin ta qware, yanzu kam akwai baiwar dake kulada Ameer dukda haka rabin rayuwarshi ne yanayine tare da Manga, dazaran ta dawo skul tofa yana wurinta inko bata zuwa skul ma bata barinshi awurin kowa se ita......
*Bayan shekaru biyu*
Rayuwa me tsafta da aminci Ali Abbas keyi da huddynshi, yanzu level 3 Manga take a jami'ar usman d'an fodiyo dake sokoto, Ameer kuwa yafi sabo da Manga fiye da kowa a gidan, Ali Abbas ya dauke idanshi akan manga a tsawon shekarunnan yayinda zancen Gadanga sam bashi ba labarin ko wanda yajishi tsawon shekaru uku da wata hudu kenan,Manga girma ya zauna yanzu shekarunta 22 a duniya, ta zama cikakkiyar mace sedai fa damuwa fal a ranta har yanzu hoto da soyayyar gadanganta rad'am zane a zuciyarta, ko zancen raba auren akai mata kuka take sakawa tukuru.....
Duk iya qoqarin dan ganin ta dannewa kanta abinda takeji abin ya faskara, duk yanda taso ta hana hawayen dake idanta gangaro wa seda sukayi tattakin yin ambaliya daga manya manyan fararen idanuwanta zuwa lallausan kuncinta,zuciyar ta ke neman fasa qirjinta ta fito,duqawa tayi ta dafe qirjinta ilahirin sumar kanta ta sakko ta rufe mata kanta da fuskar gaba d'aya,jin zuciyar zata faso qirjin ta fito bilhaq ya sanya ta dafe wurin ta furta da iyakacin k'arfinta "Gadangaaaaaaa!!!! Ina kashigane arayuwa? Kasan kuwa rashin ka yana meman kaini lahira??? Yaa Allah indai gadanga yana raye Allah ka bayyanar mun dashi, in kuma ya mutu yaa Allah ka bamu ikon jin zancen mutuwarshi daga majiya me tushe...dafa bakinta tayi da sauri inaaaaa gadanga be mutuba inshaa Allah zaka dawo gareni mu rayu cikin Aminci da qaunar juna......Dafe kanshi yayi ya koma baya a hankali duk iya dauriyarshi seda yae k'walla...kwanciya yayi yana shiga d'akin a hankali ya furta
"Astagfirullah Allah!!! Allahu kamun gafara, Allah ka yafemun, ina zanje da Haqqin Manga ni Aliyu gadanga?? Ina zankai cutar dana mata, tayaya manga zata karb'eni matsayin miji, yaya zanyi idan ta gujeni? Ina zan saka rayuwata idan ta tabbatar ni Ali Abbas nine gadangan ta? Ina zankai abin kunyar dana aikata? Me zancewa me martaba? Me zan sanar da fulani Adama? Mezancewa iyayen manga? Mezance wa Mahaifin huddy? Mezancewa huddy....yaa Allah kamun agaji....Allah kabani mafita me sauqi....Allah kasan dalilina nayin hakan Allah ka gafarceni na cutar dake manga.....
Mom Nu'aiymm.....
Masu hasashe kun canka
[7/6, 1:53 PM] +234 706 571 7620: *Haske writer's Asso.(home of expert and perfect writer's)*
*👑ALI ABBAS 👑*
Billy galadanchi
Sadaukarwa gareki qawa ta gari *Fulany saddy*
*Wannan shafin tukwicine gareku en ALI ABBAS fan's group 1, ina yinku irin totally d'innan ku sani comments naku su suke qaramun qwarin gwiwar wannan rubutun, ina godiya sosai ga soyayyarku da wannan book*
*Shout out to all ALI ABBAS fan's*
05
Tasowa yayi yadawo k'ofar parlor din yana kallon yanda take kuka rayuwarshi tana tafarfasa, duka hannayenta biyu ta cura acikin sumar kanta ta jashi sosai irin cizgar da kasan tana jiyo zafin zuciyarta har cikin ranta, kukanta takeyi cikeda ban tausayi
"Ya zan rayu idan baka rayuwata yaa gadanga, nayi qoqari in kauda ka a idona da zuciyata amma nagano wahalar da kaina kawai nake, gangar jikina kawai ke tare dani amma zuciyata,ruhina da rayuwata sun tafi a duk inda yaa gadanga, yaa Allah ka tallafi maraicina, Allah ka bayyanar mun da duk halin da yaa gadanga yake cikin gaggauwa, Allah idan yana raye ka bayyanar mun da shi cikin gaggawa cikin kamanni masu kyau, yaa Allah idan har gadanga ya mutu....se kuma kawai ta qara toshe bakin ta
"Idan ya mutu mutuwa zanyi nima, Allah karka kasheni banyi rayuwa ta Aminci nida gadanga ba, Allahu ka jib'anci lamurana Allah ka sassauta mun wannan rad'ad'in da zogin da zuciyana keyi" kasa daurewa yayi yaje ya tsuguna kusa da ita, hannunta datajejan zumar kanta dashi ya sanya hannunshi ya sauke ya qura mata ido, ita d'inma kallonshi takeyi,girgiza mata kanshi yae alamar ta dena kukan haka,amma ga mamakinta shi d'inma qwallah yakeyi, ganin haka ya sanya ta tsagaita nata kukan cikeda mamakinshi kawai se ya sake mata hannun ya miqe ya koma ciki, barin parlor d'in tayi,yayinda shi kuma ya shirya a gaggauce ya nufi sashin mahaifiyarshi, yana so yau ya sanar mata damuwar shi yanaso yau kad'ai ya nuna mata haqqinshi akanta, bashida abokin shawarar daya wuce mahaifiyarshi amma abin haushi da huddy da maneer ma bata sake musu wai adole sune ahalin gidan d'an fari......da sallamarshi yashiga cikin parlor d'in ba kowa, iso ya sanya wata hadima ta masa zuwa ciki, ya dad'e yana jiranta kanta fito a hakimce ta haye kilisarta batai magana ba shine ya duqar da kanshi yace
"Barka da yamma Ummu" amaimakon ta amsa masa setayi gyaran murya tace
"Lafiya dai?" jikinsa ne yayi sanyi ya kasa cewa komai ya sadda kanshi qasa kawai, miqewa tayi ta koma ciki abinta, gwiwa a sace ya tashi ya fita, mota ya cizga kawai ya nufi gidan zuhair, a parlor suka zauna ya tattare nustuwarshi cikeda damuwa yace
"Zuhair ina cikeda damuwa, cutarwar danakewa Manga abin ya isheni haka, shekaru kusan hud'u yanzu tunda few month ya rage, naksa aiwatar da abinda kace sabida inasan Manga, bazan iya aika mata da takardar saki ba, a yanda Manga keji na aranta na tabbatar mutuwa zatayi, koma gabaki daya taqi yarda da takardar, kuma wlhy zuhair ka yarda dani yanzu ina san manga so bana wasa ba,ina mata san da aduk fad'in duniya banta b'a wa mace irin saba, ya zanyi da raina ne wani?" shiru zuhair yayi nad'an wani lokaci kanya nisa yace
"Yarima gaskia tun farko kaine kayi kuskure da kanka, narasa wace qaddarar ce ta sanyaka komawa bayan munyi dakai bazaka koma a d'aura auren ba" nisawa yayi shima
"Zuhair kasani ai yanda ya zamto, alqawarin auren ta nawa mahaifinta,nasan girman Alqawari bazan iya karyawa ba" tsaki zuhair yaja
"kasan girman alqawari amma ka wofintar da igiyar aure? Aure fa ALi? Kasan kuwa ma'anar sa? Tanada haqqi a kanka kasan qarfin sha'awanta yanda yakene? Kasan yanda ake tsine maka tulin wannan lokaci ? Kasani wlhy Yarima kayi ganganci sabida yanzu bansan ta inda zaka soma ba,me martaba ma baze saurareka ba, bare ita uwar gayyar, mafita d'ayace ka aika mata takardar saki ta huta da wannan auren dabaida maraba da dabaibayi agareta" miqewa yayi
"Banida k'arfin aikata wannan Kuma,koda za'a kasheni bazan taba sakin Manga ba wlhy, dolene nasan abinyi yau d'inann bazab zura ido inga Manga tana kukan rashi na alhalin gani kusa da itaba" zuhair dai bece dashi komai ba harya fita, mugun tausayi ya bashi matuqa,yamai gudun haka yanzu wannan abin daya aikata koshi dayake amininshi baze iya bashi gaskiya ba wlhy......
Kai tsaye part d'insu ya wuce zuwa d'akin dayake mallakin shi, wani akwati ya d'akko a sama ya janyo wasu hotuna na manga da wani wanda suka dauka atare rabar d'aurin auren su, murmushi yayi ganin yandabtake ada da sauyin data samu a yanzu, wata leda ya janyo ya bud'e ya zaro wani mask wanda yake amfani dashi sanda yake matsayin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 16