maka, ka sake mun hannu wlhy karnama rashin mutuncin daze sanyaka mamakin gaske" Jiki a mace ya saketa yace
"Hilwa ki tausayamun karki cutar dani" tsaki tayi ta shige ban dakin dake cikin bedroom din ta barshi tsaye, jiki ba qwari ya fito ya jua zuwa masaukinsa gaba daya ji yake tamkar ya zunduma ihu tsabar tashin hankali.......
Manga na zaune tana danna wayanta kiranshibya shigo rejecting tayi haka ya dinga kira tana rejecting har kusan so biyar, messega ya sending mata
"Dan girman Allah ki dauki wayana Hilwa" tsaki taja ta kashe wayan gaba daya, ana haka sega mamanta ta shigo d'akin zaune ta tashi tace
"Sannu innoh" tafada yayinda maman tasha mur
"Manga wato ke kinfi so ki kasance cikin tsinuwar Allah da mala'ikun sa ko? Ki sani wlhy nida kene labarin kince mijinki ya sakakeki ya qara zuwarmun, ke mahaukaciyar inace, ke mijinki tafiya yayi ya barki nu kuwa yanzu shekarunki ishirin da biyu a duniya ni kuwa shekaruna sunfi 30 banga iyayena ba, akan laifin dabasu sukayiba bakuma ni nayiba, tunda na aureshi akan bani yakeso ba wata er uwarshi yakeso ya kwasoni mukazo nan hukuncin kenan dayake mana nida iyayena da nashi iyayen, akwai baqin cikin dayafi ka zauna ka tara 'ya'ya tare da mutum amma ace ba sonka aranshi, har akan qiyayyar dayake maka dan an masa dole yabaro gidansu kaima ya sanya ka rabu da naka gidan, bansan halin da kowa nawa yake cikiba, ko iyayena suna raye ko suna mace, ki sani wlhy bazan yadda ki kashe aurenki ba dolene ki zauna da Ali Abbas koda bakyaso, kece nake saka ran zaki sadani da mahaifana, ke bakya ma kallon rayuwarmu bamuda dangi akusa damu sekace wasu mayu, maganar ta karshe da zan gaya miki itace, idan har kikace bakysasn mijinki kinaso araba auren to bani bake har abada kuma ban yafe miki ba" da sauri ta kalli Innoh, ita kuwa ta miqe ma tabar dakin, kukan kam ranar Manga tasha shi ba iyaka seka wacce akace gobe zaki mutu.......
Qurawa Ali Abbas ido me martaba yayi bayan gama jin bayanin daddy, sannan ya nisa ya d'aga wayarshi,fulani ya kira ba jimawa segata ta qaraso a fadar, zayyane mata komai yayi sannan yace
"Dukkkanin abinda yaron nan ya aikata arayuwa laifin nake gani, tarbiyar yara kacokam an d'aura ta akan iyayene mukuwa maza maza sabida nauyin ayyukan dake kanmu muka baku ragamar komai, haqiqanin gaskia kinyi mun sakaci da tarbiyar yaro kuma ni yanzu dagake harshi kun janyomin tozarci mafi muni na tabbatar wannan abin seya tabamun mutuncina a idon duniya, dakinja shi ajiki dole ne ya sanar dake damuwarshi koya nemi shawararki yanzu wannan haukan dayayi wa gari ya waya??" duqar da kanta tayi cikin b'acin rai lallai seta koyawa Ali Abbas hankali
"Me martaba dan Allah a gafarcemu,inshaa Allahu hakan bazata qara faruwa ba" murmushi yayi sannan yace
"Ke hafsatu sanar dani kanki tsaye zaki iya zaman auren dashi ko kuwa?" sadda kanta tayi qasa batace komai ba" daddy ne yace
"me martaba ni inaga abar Ali da matarsa tunda ya buqaci hakan, ita manga dama tanaso sanda akai auren ai" shiru me martaba yayi can kuma yace Baban Manga
"Malam Iro menene ra'ayinka game da auren erka da Ali?"
"Ranka ya dade inaga abar musu aurensu Allah shi kadai yasan ma'anar yin hakan" godiya sarki ya masa ita kuwa fulani tace
"Ranka ya dade ina roqon alfarma abani dama na hukunta Ali Abbas daidai da laifinsa,sabida ya cancanci hukunci gaskia" Murmushi me martaba yayi yayinda qirjin Ali Abbas yayi mugun domawa sabida yanda takira sunansa kanta tsaye yaune karonta na farko data furta kalmar ita kanta ta sani tun bayan da aka sanar mata sunansa, ya tsorata ainun da yanayinta ba kad'an ba, kasa daurewa yayi ya duqar dakai sosai
"Ummu dan Allah ayimun sassauci" banza ta masa,me martaba yace
"Kije kimai hukuncin daya dace dashi kowane irine injini, kuma hukuncina na gaba shine karka kuma zuqarmun nan koda gaisuwane she bayan shekara daya idan ka nutsu ka tariyo cewar addinIn Allah na tura saudia ka koyo ba wofintar da aure ba" kuka Ali Abbas ya soma yayinda kowa ya watse har me martaba aka bar shi shishi kadai a fada.....
*Bayan sati Biyu*
Har yanzu huddy babu wanda ya mata zancennan domin daddy yasan halin Amminta bata barwa Allah lamuranta, ko Ali Abbas be mata zancen ba ita kuwa bata nemi sanin komai ba........
Ali kuwa tunda aka gama wannan zaman rabon dayaga Manga koya samu wayarta, gabaki daya hankalinshi ya gama tashi, gashi baze iya tambayar fulany ba waneshi ma tunda bata amsa gaisuwarsa, idan yaje bangarenta ma bata fitowa,yakuma bincima an tavbatar masa Manga bata gidan......
A adamawa Manga nacan cikin dangin mahaifiyar Ali Abbas tana samun gata da kula na musamman, ba laifi tanajin dadin zamanta dasu........
Mom Nu'aiym
Kuyi hakuri da wannan se kuma gobe inshaa Allah..
[7/6, 8:24 AM] +234 813 124 3554: *HASKE WRITER'S ASSO. (Home of expert and perfect writer's)*
*👑ALI ABBAS👑*
*Sadaukarwa gareki qawa ta gari Fulany saddy*
*Ina baran adu'arku mamana batada lafiya*
09
Zirga zirga Ammin huddy keyi tamkar me yunqurin naquda, gabaki d'aya hankalinta ya tashi jin wannan xancen da daddy ya gaya mata, tayaya ma d'iyar wulaqantacci irin su Baban Manga zata auri d'an sarki even so ma ace wai kishiyar erta, ina Manga tayi matsayin dazatayi kishi da Hudaisan ta? Ina ita ina matsayin likita? Wacece ita dazata yi wannan haukan? Wato ma cutar ta Manga keyi duk zaman da wannan munafukin mijn na huddy yakai Manga gidansa tanayi ashe zaman aure suke, Allah ne ma be bata haihuba kenan da yanzu ta haihu..."Wlhy indai ina numfashi baze tab'a yiyuwa inbar auren nan na su ya d'ore ba, sena ga bayan wannan mangar sena wulakanta rayuwarta sena sanya ta gudu da qafafuwanta daga Nigeria gaba d'aya, dangin ubanta da uwarta zata koma koma ta shiga duniya, da wanne huddy zataji a rayuwa?" kwafa tayi bayan data gama sambatunta tabar cikin dakin ta dauki wayarta ta dannawa huddy kira.....
" Amma ke dama huddy kinsan da wannan kika qura ido kika yi shiru? Sekace wata sokuwa mara hankali da wayo? Sekace bani na haife kiba, yarinya sakarya kawai mara wayau"
"To Ammi niya zanyi? Wannan qaddararmu kenan nida ita, tun anan na qara gane Allah shi karimun rahimun ne, saboda bantaba zata inda na sanya qafa Manga zataje ba,segashi wai itace uwargida yayinda nake binta abayan baya ma, Dan Allah Ammi nasan halinki karki soma shiga hurumin Allah wlhy niba ruwana, tunda har gobe mijina yana matuqar kulawa dani kuma yana sona ba iyaka, kimun adu'a akan rashin lafiyata domin ni ina ganin haske sosai a lamarin ina kyautata zaton cewan akaina za'a samu masu cutar cancer wacce zata warke" tsaki taja
"Nafi kowa sanin inshaa Allahu mutuwa ba yanzu ba, kuma indai cancer ne zaki warke sumul, abu daya nakeso ki gane shine wlhy indai ina raye sena raba auren manga da yarima, ke bakya ganin ma tamkar duk zaman da tayi a gidan ha'intar ki sukeyi?? Lallai ki kama kanki wlhy banza sokuwa wacce batasan ciwon kanta ba"
"Nidai Ammi bazan dena miki nasiha ba wlhy, kuma duk abinda zaki aiwatar indai danni ne kidena banso, sannan idan har bakijiba kika aikata wlhy nidai ba ruwana ko a wurin Allah" tsaki uwar tayi ta kashe wayar abinta...
A yola kuwa Manga ta soma shiga damuwa sabida kusan watanninta uku kenan, batasan ma'anar kawota yolan da akayi ba, gata dai cikin gata na musamman amma sam bata jin dadin gatan, wani yammaci tana zaune a d'akin matar data fahimci itace kakarsu Ali sabida yanayin kamannin dasuke da ita se kawai taji sallamar fulany, rungumeta tayi hadda shagwab'a ita adole se bayan sun huta sun natsa sannan fulany tayi kiranta da ban
"Auta nasan bakisan dalilin daya sanya nasa aka kawoki yola ba, nakuma sani bakisa dalilina na sanya ake ta miki gyare gyare ba,ki sani abu mafi farin ciki arayuwata shine samun labarin cewar ke matar yaro ce, bantaba samun farin ciki ba makamanci sanda naji wanda labarin, nasan zakiyi tunanin naso kaina da yawa ace duk abinda ya miki inaso ki koma masa amma ki sani na fahimci kece kadai zaki zamto abokiyar shawarar yaro, kece nake sakaran zaki daurashi akan turban danakeso duba da yanayin tarbiyarki da halayyarki ta kirki, ko tashin Ameer ina sane da yawan adu'o in da kike koyar dashi komai ya iya,daidai da toilet wannan bayajin dadin shigarsa se yayi adu'a bacci ma seyayi adu'a,ina sane da komai....ki sani Auta na dade ina burin inga an raba aurenki da mijinki daya bata in sanya Ali ya aureki koda bayaso, yanzu danasan ke mallakinsa ce bazan yi wasa ya rasa uwar 'ya'ya ta gari ba, hikima ta kawoki tanan shine domin dalili biyu, na farko inaso ya d'and'ani azabar da kika d'and'ana daya barki wannan shine hukuncin daya dace dashi domin kuwa hadimansa da huddy sun tabbatar mun cewa ko abincin kirki baya iya ci...na biyu kuwa inaso ne kisha gyara matsayin ki na matar Yarima be kamaceki ace kije masa hakan ba ya dace ki fito ajinin sarauta sak....zance na gaba kuma inasone asha shagalin bikin babu qaqqautawa ina fatan zaki bani hadin kai" Sam Manga ta tsani Ali amma yata iya uwarta dole ta kalleta tace
"Allah ya saka da Alkhairi Ummu na, Allah ya barmunke yanda duk kikeso a wurin auta hakan zanyi inshaa Allahu" rungumeta ummu tayi sannan ta ciro wani zobe dake hannunta ta sanya mata ta kuma zare wani a warwaraye guda biyu ta sanya mata tace "Wannan tsarine dan Allah ki kasance sanye dasu akoda yaushe kuma ki riqe Allah daa yawan Adu'a da azkhar safe da yamma kinji" jinjina mata kanta tayi alamar gamsuwa
"Nanda sati biyu zan turo mota zaki koma sokoto" murmushi tayi
"Ummu dan Allah ki tafi dani" hannunta ta riqe
"Auta Yola bata miki dadi ne?" murmushi tayi
"Ba haka bane Ummu na kusa dake nakeso na ganni ai"
"Auta sati biyu ai kamar gobene karku damu abinda akeyi ne ba a gama ba anan din ki kwantar da hankalinki, Nima kuma zan kwana biyu anan tukunna".
*Sokoto*
Yaro na sani lallai bakasan inda nakai Manga ba, kuma kasan nayine sabida na hora ka akan danyen hukuncin daka aikatawa yarinya, sam bakaiwa kanka adalci ba kuma ka tozartar damu da kanka ma, bazan iya doguwar magana dakai ba amma zan sanar dakai abu daya
"Manga zata dawo nanda kwana daya, kuma inaso a shirya kuje da ita dubai amata siyayya, sannan idan kun dawo lallai ashirya bidiri daidai da yayan sarauta akuma wadata ta da kayan gida masu kyawun gaske,wannan guess house dake samaroad amar gyara me kyau arkilla ta mata nisa gaskia banaso, idan zaku tafi dubai kuje da huddy itama ka sauya mata nata kayan gidan, ka kuma mayar da ita gidanka na Arkillah badan komai ba sedan ita tanada wayonta kuma ta gama mallakar hankalin kanta sosai,kaji tsoron Allah yaro kayi adalci tsakanin matayenka guda biyu, kayo halin mahaifinka domin shi sam ba macuci bane yanada adalci" godiya sosai ya mata kanya bar wurin
*Yola 2 sokoto*
A hanyar su manga na zuwa sokoto daga yola gashi tafiya ce me nisan gaske ta kwana d'aya, cikin dare wuraren 3 suna bacci yayinda driver ke tafiya kawai sukaji harbi, a firgice manga ta tashi ta tashi tsohuwar dasuke tare,salatin driver sukaji sannan sukayi parking a hankali, motocine en fashi suka tare sunfi qwara ashirin, daga nan aka soma operation nacin zarafi, Raping en mata sukeyi yayinda suke suke harbe ilahirin mazan dasukayo tukin bayn sun karb'e kud'ad'en hannunsu se wanda Allah yasa beyi gaddama ba ake bari, sun kusa sokoto ma sanda abin ya faru dashi, tashin hankalin driver din befi seda yarima ya sanar masa karsu taso da tsakiyar dare ba, lallai su kwana a kaduna su taso da asuba, ya gama gigicewa sanda yaga an wurga Manga cikin motar en fashin nan, yanaji yana gani itada wasu en mata uku aka tafi dasu, zaman dirshan yayi yana kuka, ga sauran mutane sun saka en uwansu da aka harbe agaba suna kwasar kuka, da qyar ya lallab'a tsohuwwar dake tare dashi suka hakura suka kamo hanyar sokoto....
"Kallo d'aya zakawa Ali Abbas ka tabbatar yana cikin farin cikii mara misaltuwa, ya kasa ya tsare a gate din se tsaki yake yanajin zafin driver dabaya daukar wayarshi, Manga dama bata dauka koda yayi kiranta a waya sedai ya mata message shidinma bata replying nashi.....Sauke ajiyar zuciya yayi ganin motar ta shigo gate din ya koma inda yake saran zasu parka,mamakin ganin an fito batare da Mangaba yakeyi jikinsu duk a mace, da sauri yaje kusada Driver
"Kai Idris ina kuma ka baro Hafsat" tsohuwarce ta saka kuka
"Wlhy Ali saceta akayi, en fashi suka tare mu cikin dare wuraren asuba mazance kan azo mafara, sukaiwa wasu fyade sukaje da wasu, wanda suka kwasa ne hadda Manga, ohni Iyajo ya zanyi da raina wannan bakin cikin, nasan ma yankasu zasuyi tunda agaban mu sukayi harbi mutum yafi ashirin" tamkar ta watsa masa ruwan zafi haka yajiyo saukar kalamanta tsaye yayi tamkar an dasashi a wurin, da qyar ya daga kanshi ya kalli idris
"Idi da gaske wai abinda nakeji, mangan tawa er fashi suka tafi da ita" sadda kanshi qasa yayi bece komai ba, yasani ko shaqeshi se Ali yayi, cox shine da kanshi ya zab'i idi sabida ya yarda dashi, kuka kawai ya somayi ya juya gun fulani da har iyajo takai mata rahoto, kowa hankalinshi ya tashi sabida yarima ya koma tamkar wani mara hankali......
A wani qaton gida cikin qungurmin daji suka kaisu, kallon kallo en matan keyi a tsakaninsu ko waccensu jikinta na rawa sosai....bame wa wani magana se kuka, suna nan zaune wasu mazan susu uku suka shigo suka zari wata matashiyar budurwa dabatafi shekaru sha hudu ba, aka kira wani me suna oga murus yazo ya qare musu kallo yace
"Wannan er shilar tawace,kuma waccen er fillon koma jan buzuce dagani zatayi mai itama tawace, su bana kisa bane, aikin sati uku zasuyi a mayar dasu kan hanya su kama gabansu, wayannan kuma kuci kuyi yanda kuka ga dama dasu, amma afara b'aremun er shila inci agaban wayannan" gabaki d'aya Manga da sauran yaran a rude suke, sun gama zarewa sosai sun tsorata ainun, yarinyace qara ma haka a gaban su Manga aka ware mata kaya tana ta kuka suka manna salatif abaki duka wangale masa ita, ba imani haka ya dinga dirzarta, tana gurnani tana wun tsila kafa, se ihu yake shi kuwa a haka seda yayi rawun shida sannan ya kallesu yace
"Yarinyarnan wata biyu zatayi, tanada dadi abinta sosai, abata kulawa anjima zan qara kunji ko?" da sauri suka amsa, yana fita dayan yace
"Kaga ogafa zagaye shida yayi, ban taba gani ba, gaskia sena dana, sudai su manga banda kuka ba abinda sukeyi, a haka suna kallo aka sake hayayyaqewa yarinyar nan, in wannan yafito wannan yashiga da qyar suka saurara mata.......ruwan zafi suka kawo suka sakata aciki tanata kiran Maman ta amma bata kusa yarinyar dai har suma tayi ba maceci.....
Da asuba akazo aka tafi da Manga, babu irin turjiyar dabata nuna ba, amma qememe aka jata zuwa d'akin oga, zaman dirshan tayi tanata uban kuka, ko a jikinshi yace dasu
"Ku fita wannan zan iya da ita, a hankali nakeso muyi bawai ta qarfin tuwo ba, waccen ma dan bata saba bane" ficewa sukayi suna shewa "Se oga, yasin operation na jiya muma ya mana gashi yanzu zamu more abinmu" dariya ya rufe dakin yayinda ya mayarrda da dubanshi zuwa ga Manga, bindiga ya ciro ya nuna mata yace
"Ke miqe kiyi tsirara ko wlhy yanzunnan na dauke kanki da alburushinan" jiki na rawa manga ta miqe, sabule doguwar rigar dake jikinta tayi sannan ta sab'ule ilahirin kayan jikinta se uban kuka takeyi, yana riqe da bindigar ya maso yakai hannunshi jikin nononta daya ya damqesu da qarfi sekace ze tizge su
"Banbancinki da waccen qwailar kenan,akwai kayan alatu, nafiso inyi miki wasanni tukunna ko kuwa er fillo?" runtse idanta tayi zuwa wannan lokacin tama kasa kuka tsoro me tsanani ya shigeta tana jinshi sanda yakai bakinshi saman breast dinta bayan ya hankadata kan gadon ya kuma haye ruwan cikinta, se warin sigari yakeyi da sholi alamar yasha ya qoshi......
Mom nu'aiym
*HASKE WRITER'S ASSO. (Home of expert and perfect writer's)*
*👑ALI ABBAS👑*
*Sadaukarwa gareki qawa ta gari Fulany saddy*
10
Dukkanin wasu adu'o i dasuka zo bakinta su takeyi na neman tsari, gabaki daya shi kuwa se yagalgalar ta yakeyi harya wurgar bindigar gefe d'aya, ganin fa ya zare ilahirin kayan jikinshi yana qoqarin aikata mata abinda bashi kenan ba ya sanya ta rarumo wuqar datagani an manna Apple ajiki tayi ta sanya iya qarfin ta ta kaiwa abar yanka, lokaci daya ya qwallah qara hade da riqe abar da saura mata kad'an ta guntule ta fadi qasa gaba d'aya, gigicewa yayi ya soma zagaye dakin yana ihu sosai, bindigar ta janyo ta saisai ta masa tace
"Idan ka qara kwallah qara wlhy harbeka zanyi har lahira" shiru yayi har lokacin yana riqe da abar yana runtse ido, igiya ta gani saman gadin alamun idan an kawo mace nan ake daureta , umarnin kawntawa wurin ta bashi sannan ta ajiyr bindigar da nisa ta kama dukta daddaureshi shi kuwa bashida sukunin iya aiwatar da wani abin. Salatif ta gani irin qaton nan, ta sanyashi ta rufe mai baki, sannan ta boye bindigar ajikinta ta bude d'akin ta fito, ta sake rufe qofar dakin, a hankali cikin sanda ta leqa d'akin da en matan suke ta tarar sun tasa wacce akawa fyad'en agaba sunata kuka rufe dakin tai da key taje ta sanar musu meya faru sannan tace su nemi hanyar barin gidan kota wane hali ne, dayar ce ta kalleta tace
"Aunty ni sunana Hannatu, wannan da akawa fyd'e qanwa tace sunanta humaira, wannan ce ba gidanmu daya ba ban santa ba, amma tace su nanta salaha, kefa yaya sunanki?" murmushi tayi na qarfin hali tace
"Sunana Hafsatu Manga, amma anfi kirana da Manga" jinjina kai tayi tace
"Ina wa ennan mazan dake tare daku"
"Suna ta bayan dakin nan da alama giya suke sha, ki leqa zaki gansu a buge, muma ta window muka gani" miqewa tayi taga suna bacci awurin saman kujera, tace wa su Hannatu ku taso kafin sauran su dawo fa, akwai matsala idan suka samemu, ita da kanta ta goya humaira suka yo waje, hanyar dasukaga alamun ba'a yawan bi suka yanki dajin suka bi....Tafiya suke ba qaqqautawa, duk wanda ya gaji da goyon Humaira seya baiwa d'an uwanshi sabida sam ita bazata iya tafiyaba, qishi ne ya soma damunsu suka fara kasa tafiya se kuka suke, Manga duk tafisu qarfin hali, lallab'asu tayi suka ci gaba da tafiya har dare yayi gari ya soma duhu suna cikin dajin basuga alamar gari gaba ko baya ba, har gari yayi duhu, kafin kuma ajima kadan hadari ya taso gadan gadan, dukkansu sun tsorata ainun musamman ga hadarin yazo da wata iska me qarfin gaske.......
A b'angaren Ali Abbas kuwa ya gama rud'ewa matuqa, zaune kurun yake amma sam hankalinshi baya tare dashi, huddy ce tazo ta sameshi ta cikinta daya dan tasa harya bayyana ta kalleshi sosai tace
"Dukda yake yaa Ali yaune rana ta farko da zancen Manga ze shiga tsakanin dakai amma inaga Manga sam bata buqatar wannan dogon tunanin dakake da damuwa, adu'arka take buqata Allah ya kub'utar da ita yakuma kareta daga sharrin masu sharri,nima kuma zan tayaka inshaa Allah" nisawa kurun yayi bece kalaba, se kwantar da kanshi da yayi saman cinyarta cikeda jin tausayin kanshi idan yau akace Manga ta mutu shi ina zai shiga? Runtse idanshi yayi ya bud'esu a hankali duk saukan ruwan saman da ake tare da buguwar zuciyar sa yake sauka, ko wane hali Mangan shi take ciki yanzu, koshi yanzu yanajin sanyi wataqila yanzu ma a waje take, qila ma bata tare da kowa yanzu, wataqil kuma sun kashe ta" zabura yayi daga kwancen da yake
"Kai ina baze yiyuba Inshaa Allah" ya furta a sarari sannan yakoma ya zauna ya qara dafe kanshi, sosai ya baiwa huddy tausayi, ita gabaki dayama tsorata ma tayi da yanayinshi, ta tashi kawai tayi ciki tana jin zuciyarta na mata zogi......
Ruwan saman na sauka kuwa su Manga suka samu wani kogon dutse suka shige a ciki, amma a banza sabi qarami ne ita mangar ma tana daga waje sekace me gadi, suna nan ana qwala ruwan samo suka jiyo maganganu sama sama
"Wlhy qyastu idan naga yarinyar datawa oga haka sena illata raguwarta,bazab kashe taba amma wlhy sena naqasa wawiya, sena cire mata nonuwa duka biyu, in cire mata ido daya kunne daya sannan in mata aski inci ta a banza in wurgar a dajinnan, nasani wannan zakunan zasu qarasa mana matsalar ta" tsaye sukayi suna nazarin wurin yayinda su Manga sukayi shiru se qarar saukar ruwan saman kakejiwowa gashi anata walqiya dan ma Allah yasa sun juya musu baya aida sun gansu, gaba sukayi suna ci gaba da zancen su manga suka gagara fito wa daga cikin kogon suna nan a takure, har aka dena ruwan se kuma suna shirin fitowa suka jiyo takunsu da shewar su
"Ai inaga fa sun samu sun gudu, kaga babu nisa zuwa qauyen yankara daganan, inkuwa hakane sunyi nisa bazamu same su ba" "Ni ai bama wannan ba Almakashi yanda yarinyar nan ta kassara rayuwar oga, sannan kuma gashi gabaki daya sun gama gane hide out dinmu, idan fa bamuyi hankali ba wlhy seta kawi jami"an tsaro anan kaga kuwa an yanka ta tashi kenan" Tarine ya sarqe humaira wanda gabaki d'aya ya mayarda hankulansu awurin suka juyo suna kallon kogon da suke ciki, d'ayan yace
"Ashana kaji abinda naji?"
"A kogonnan ne wlhy inaga aljanaine" kan wani ya qara magana tarin ya qara tasowa yarinyar se kukan neman ruwa takeyi
"Kaga Almaksashi yarannan ne zomuci uwarsu, tsorone ya sanya suka fito gaba dayansu banda humaira dabata iya tashi sam, dariya suka kwashe da ita sukayo kansu, sumar kan Manga ya cabko iya qarfin shi ta qwalla uwar qara ya turata seda kanta ya daki wannan dutsen take jini ya soma fita daga goshinta, ya qara yi kanta ze cafko ta zaro bindigar dake qirjinta ta harbshi a qafa, ita kuwa Hannatu ta qwace ta hannunshi suka nuna awurin dayan, hannatu ce ta harbe dayan ma a ciki, a take ya fadi wurin a mace shikam, dayan me suna Almakashi se riqe qafarshi yake yana ihu, aljihunshi suka lalubo suka dauke musu wayoyi Manga ta goya humaira dake kukan ruwa suka danna a guje....sunyi tafiya me nisan gaske yayinda jiri ya soma daukar Manga kasancewar dukda tayi amfani da dankwalin humaira wurin daure wurin dataji ciwo hakan be sanya jini ya dena zuba ba, haka ta daure saliha ta karbi humaira se bayan salla asuba gari ya gama wayewa suka isa cikin wani qauye da ake kira 'yankara, wasu yara manga ta gani tace dasu
"Kai inane gidan sarki?" kallon medan wayon ciki yayi ya kalli yanayin shigarsu yace
"Muje na kaiku gun meri dai shine sarkin garinnan" jin jina kanta tayi suka bi bayan yaron har zuwa wurin me garin, ba'ama soma zaman fada ba wannan lokacin seda jira kusan karfe tara sannan aka soma zaman fada, kafin nan har sunci abinci sunsha ruwa, an kuma gasawa Humaira raunin ta abisa roqon da Manga ta musu, zaman fada ya tashi anan su manga sukayi bayanin meya faru dasu tiryan tiryan, hankalin me gari ya tashi da kanshi yayi waya ma en sanda suka hallara garin, kai tsaye aka miqasu manga sokoto kasancewar dukkansu gari daya suka nufa, sunsha mamakin su a katsina suda sunmabar zamfara state sun doshi sokoto sanda abin ya faru, kenan ba qaramun yanka sukawa dajin ba sunsha wuya, A state C I D aka kaisu inda kowa ya bayarda Number din en gidansu, Manga bata da Number din
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 16