ni de bazan iya cigaba da rayuwa dake nihal tana tare dakeba,tunda na fuskanci kaman ba kanki dayaba,dan kin nu na mata tadena guduwa idan ta ganmu ba matsala bane amman mai ne amfanin wai tamanta abinda da yafaru tsakanin mu,Samiha ki sani cewa dukkanin wani makiyinka ba ka kokarin dawowa da shi gareka ni sai anjima idan gidan su ma zaki koma da zama ki koma ga gurinnan.
Basma Basma dan alllah ki tsaya ki saurareni taya kike tunanin rayuwata zata tafi dede ba tare dakeba,kinsani cewa kece duk wani farinciki na bayan yaya Dr bani da wani farinciki face ke dan Allah kada kiyi fushi dani akan wanann kiyi hakuri besty,ko juyowa batayi ta kalleta ba,hakanne yasa Samiha ta hakura ita ma tayi hanyar gida da niyyar zuwa gobe tasan ta huce sai ta tura mata message ta waya ko taje gida.
Ta koma gida tana zuwa ta iske yaya Ahamd da yaya Dr suna zaune a farfajiyan gidan suna ta shira,yanayin yadda ta gaidasu ne ya tabbatar musu tabbas akwai matsala gaba daya idanuwanta sunyi wani iri alamin tayi kuka.
Samiha zo nan inji yaya Dr mai yafaru dake naga kinshigo gidan gaba daya wani iri yanayinka babu komi yaya ki fadimin gaksiya kinsani sarai babu wanda ya kai ni saninki ki fadamin abin dake damunki kafin ranki ya baci.
Wani matsanancin kuka ta kece da shi mai matukar tsuma zuciya gaba daya hankalinsu ya tashi yaya Ahmad ne yayi saurin cewa "Dan Allah Samiha kiyi shiru da wanann kukan dan Allah "a rayuwar yaya Ahamd babu abinda ya tsana irin ganin hawayan Samiha duk da cewa yanzu babu wata kauna a tsakaninsu amman dede da minti daya bai taba jin sonta ya ragu a ransaba nan sukayi ta rarrashinta har sai da ta tsagaita kukan.
Tom yanzu fadamin mai ne yafaru yaya nihal gaba daya wata zabura sukayi suka mike tsaya Samiha nihal Kuma?ban gane nihal ba .
Ta kwashe komi ta basu labari bata rage Koda mitsitsin abuba"Innalillahi wa inna ilahee raji'un shine kawai abin da suke furtawa"sakayya tun mutum na gidan duniya tom wanann abin darasin ga wasu da ke yunkurin cutar da yan uwansu musulmai tashi ki shiga ciki Allah yasa midace.
Har ta mike ta kusa kofa ta juyo tace "Yaya sai Dr ya ansa tace Aah ba kai ba Yaya Ahamd sai ya juyo dan Allah ka kira Basma kabata hakuri"mai yafaru?naga tare Kuka fita tayi fushi ne dan na karbi number din nihal nace zanyi mata magana akan komi ya wuce tadena Jin kunyar mu murmushi yayi saboda shi tunda yake ya jima bai ga yarinya mai hankali da ta wakkali kamar Samiha ba,karki damu inshallah idan na koma gida zamiyi magana.
Nagode sosai yaya ta wuce da dan fara'a a fuskarta domin duk wani abu da zai jawo mata nisa da Basma bata so, tana son Basma tana kaunar Basma dan duk son da takeyiwa yaya Dr bata ki ace su auresa su biyu ba saboda Basma kawace ta kirki wacca samin irinta a yanzu na da matukar wahala.
Tana shiga taga momy bata parlour sai tayi farinciki sosai saboda bata son momy ta fuskanci halin da take ciki,nan tana shiga dakinta tayi wanka ta gabatar da sallan azahar ta xauna tana ta tunanin rayuwa da yadda ada abotar su take su uku,komi tare sukeyi babu wanda ke son damuwar dan uwansa.
Nihal duk abin da dadyn ta ya kawo gida bata taba ci sai ta taho musu da shi makaranta sunci tare rayuwarsu na birge kowa,wani hawaye taji ya zubo mata amman yanzu duk sanadin namiji wanann abotar ta rushe(Mai muka dauki soyayyya minzabi mu rabu da kowa da komi na mu akanta bazan ce soyayyya ba gaskiya bace amman duk wani abu dake cikinta yafi kama da almara,duk wanda ya biya sharrin soyayyya da son zuciyar sa tabbas zai aikata abinda har ya mutu ba xai dena da na saniba,domin wani lokacin ba wai karfin soyayyyar da mikewa wadan da mike tare da su bane yasa mike aikata wani abin,tsantar rura mana wutar son su da shedan keyi shine ke jawo komi, adullokacin d a mika fada tarkon soyayyya yakamata mu nutsu mu Kuma san mai mikeyi saboda gudun aikin da na sani).
Haka tayi ta tunani kuka kuwa yaka sa tsayawa tana jin Ina ma tana da damar dawowa da rayuwansu tamkar da,Ina ma tana da damar da xata sauya komi da yafaru nihal Allah ya sani Ina sonki domin Allah.
Nan ta jawo wayarta ta lalubi lambar nihal ta shiga ta Whatsapp ta fara rubuta mata sako kamar haka.
ASSALAMUALAIKUM NIHAL FATAN KINA NAN LAFIYA,INA MAI NEMAN WATA ALFARMA AGURINKI WADDA NASAN TABBAS NAFI KARFIN TA AGUNKI,NIHAL INA ROKONKI DA ALLAH DA ANNABI KI MANTA DUK WANI ABU DA YAFARU A TSAKANIN MU KISA A RANKI BABU ABINDA YA TABA SHIGA TSAKANIN MU,NIHAL KODA BAKI AIKATA ABINDA KIKA AIKATA BA DOLE SAI WATA TA AIKATA DOMIN ALLAH YA RUGA DA YA RUBUTA HAKAN SAI TA KASANCE ACIKIN RAYUWA TA,KUMA BAN ISA NA KAUCE KADDARAR DA UBANGIJI YA RUBUTAMIN BA,DAN ALLAH NIHAL KI MAIDA KOMI BAKOMI BA,SANANN KI DAUKI KADDARAR DA ALLAH YA SAUKARMIKI HANNU BIBBIYU KI NEMI YAFIYAN UBANGIJI DONIN DAN SHI KIKE RAYUWA BA DOMIN MUTANE BA,DAGA KARSHE INA MAI SANAR DAKE CEWA NA YAFEMIKI DUK WANI ABU DA YAFARU TSAKANIN MU UBANGIJI ALLAH YA YAFE MANA BAKI DAYA,SAMIHA......
Bayan ta kammala rubuta wanann sako ta tura ta Kuma fita domin aiki,kamar wasa nihal na zaune a daki tana ta kuka dan tun bayan tafiyar su Samiha ta kasa fitowa kawai tana tunano irin abubuwan da ta aikatane a baya da yadda suke zumuncin su abaya,ita kanta a yanzu kyamatar kanta takeyi ta tabbata abinda tayi bata kyauta ba kwata kwata,kamar ance ta kunna data dinta tana kunnawa taga bakuwar lamba ta tura mata sako,tana budewa ta fara karantawa tunda ta fara karantawa har ta gama tana zubar da hawaye matuka zuciyarta ta sake karaye addu'a kawai take Ina ma ta mutu sai yafi mata sauki da wanann halin da take ciki,tana fara katantawa jikinta yabata Samiha ce sai gashi a karshan rubutun taga ansaka Samiha ,wani matsiyacin kuka ta fashe da shi take ta rai rashi wanda bata san ranar tsayuwar saba,haka tayi ta fama har tayi mai isarta.
Ashe akwai mutanan kirki irin haka haryanzu a rayuwa tabbas Samiha ke kawar kirkice bantaba tunanin zaki yafemin abinda na miki a dan karamin lokacin nan ba,tabbas Samiha nagode sosai da irin abin da kikamin abinda take furtawa kelan a ranta tana Jin Ina ma xata iya rubuta masa sakon kamar haka amman takasa kunya da nauyi gaba daya ya hanata yanzu Kuma bata da burin da ya wuce su hadu da Samiha domin tana son sukara ganawa su kalli junan su a matsayin abokai tana ta wanann tunanin momy ta shigo ta tararta a daki kuka taga tanayi nihal lafiya mai ya sameki? jitayi kamar tabawa momy labarin duk abin da yafaru amman sai ta kasa saboda bata son ta saka tsanar kanta azuciyar mahaifiyar ta kawai sai ta cigaba da kuka nihal kiyi hakuri ki sakawa zuciyarki ruwan sanyi babu wanda yafi karfin kaddara aduniyar nan Kuma babu wanda yafi karfin ubangiji ya jarrabashi a lokacin da yaga dama,duk da wani lokacin akwai sakacin mu amman komade mai ne abinda yaka mace mu idan abu ya samemu shine mu guji gaba domin duk abinda yafaru ya riga da yafaru hakane momy,tom Ina son ki rage wanann koke koken saboda bana jin dadi sa sannan Kuma ba a son mai ciki tafiya shiga cikin damuwa domin matsalane, inshallah momy zan rage.
Bangaran Samiha kuwa tana ta jira xataga nihal tayi mata reply amman shiru bakomi tundade ta karanta aishikkelau.Hankalinta Kuma da tunaninta yakoma kan Basma tafara tunanin ta kirata sai de tasan yar mai shegiyar zuciyace ba sauraranta zatayi ba murmushi kawai tayi tace "Basma baza ta taba iya samin farinciki ba inde babu ni,nima Kuma haka na tabbata xuwa gobe zata huce"tayi murmushi abin ta taci gaba da aikinta......
Ubangiji rabbi marasa lafiya na gida da asibiti Allah kabasu lafiya,iyayan mu da suka rasu Allah kasa sun huta,iyayan mu dake raye Kuma ubangiji Allah ka karawa rayuwar su albarka,ka kuma sake rufamusu asiri🤲🏼🤲🏼.
https://chat.whatsapp.com/FdN9LskESVf6ESy63R3QWf
CREATED AND WRITTEN
BY
ZEEY NASEER
*🌙MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION'S🌙*
We shine all over the world
https://www.facebook.com/profile.php?id=100094397072466
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~~~~~~~~~~
Page 33
Abubuwa sun cigaba soyayyya da shakuwa kullum na kara shiga tsakanin wadannan mutane biyu bada ban kan nayi karya ba da nace yanzu sunfi kaunar junanan su fiye da da,saboda yacca suke kaffa kaffa da dukkanin wani abu da zai shiga tskanainsu. Hakika Yaya Dr na matukar kaunar samiha haka Kuma Samiha.
Washegarin faruwar lamarin Samiha da Basma da safe Basma ta shirya Yaya Dr ya dauketa ya kaita har gidan su Basma,ta bata hakuri da mamaki sai taga Basma na kuka besty mai ne ya sakaki kuka tunanin yadda rayuwan mu ta sauya baki daya a baya bani da wadata kawar da ta wuce nihal karki manta ni ce Sanadiyyar haduwarki da ita,wallahi Samiha ina matukar jin bakincikin halin da nihal ke ciki Ina matuakar tausaya mata sai de zuciyata ta kasa aminta da ta yafe mata.
Kiyi hakuri Basma babu wanda ya isa ya wuce kaddararsa yanzu da Allah ya so akanki ko akaina zai faru muyi hakuri miyi yafiya ga juna rayuwan ma gaba dayanta takaitacciya ce babu wani abu da zai dawwama.
Hakane Samiha na yafewa nihal inshallah komi ya wuce kiyi hakuri kinji babu komi Basma kinsani cewa daman bana taba iya rikeki ko na kwana da fushinki.
Suna zaune suna ta shira kawai wayan Samiha ya dau kara mamakin wacca ke kiran ne yasa ta daga, tana dagawa taji muryan nihal Samiha dan Allah dan annabi kutaimaka ku zo gidan mu yanzu keda Basma da Yaya Dr dan Allah kar kuki zuwa nihal mai yafaru?ku zo ku kawai da kyar nihal ke maganar daga ji kai kasan tana matukar cikin tashin hankali mai matukar girgiza zuciya.
Samiha daman sarkin tsoro tuni ta rikice ta fara hawaye Basma tambayar ta take mai ke faruwa amman takasa dedeta kanta balle tayi mata bayani,da kyar ta samu tace mata nihal ce dan Allah kuzo mije ke ki nutsu ki fadimin mai ke faruwa tace tana son ganin mune ke sai kace baki san makircin yarinyar nan ba har wani tace tana son ganin mu mu wani dibi kafa mu tafi sai kace bammu hankali dan Allah Basma wai ke ba kya afuwane sai kace ba musulmi
Fiyau Samiha ta fice ta bar dakin,wanann ya tabbatar wa Basma cewa Samiha fushi tayi duk abin da yasa Samiha fushi kuwa ba karami bane domin bata da saurin fushi kuma inde tayi kafin a shawo kanta ana jimawa wanann ya tsorata Basma babu shiri ta dakko mayafin ta ta fito nan ta samesu suna kokarin jan mota ganin fitowanta yaya Dr yasa ya tsaya shiga tayi ya ja suka tafi babu mai cewa uffan,lokacin da Samiha ta fito kuka kawai Yaya Dr yaga tana yi bai tambayeta mai yafaru ba tace masa su tafi gidan su nihal haka yace ta shiga yayi kokarin jan motar shine bamsa ta fito.
Suna shiga gida suka tarar momyn nihal a falo tana kallo sai hankalinsu ya kwanta Basma ta kalleta tace daman bana fadimiki rainin hankalin ta bane,Basma dan Allah ya isheki haka ya isa,nan Samiha ta Kalli momy tace Ina nihal tace tana dakinta dakin ta wuce a hankali a tashi abin da ta ganine yayi matukar tayarmata da hankali gaba daya ta rude ta kwalalala wani kara wanda shi ya jawo hankalin su, su da suke falo suka shigo a guje suna shigowa suma tashin hankaline ya mamaye su .
Momy tayi kanta nihal nihal mai ke faruwa dake Ina cikin gida bansaniba gaba daya tana cikin jini yagaja yagaja abin tausayi nan momy ta ciccibeta ita da Samiha su kansu da suka dauketa sai da suka jike da jini.
Ku tsaya ni ba burina ku kai ni asibiti ba na sani cewa mutuwa zanyi shine dalilin da yasa nace ku zoku nasani cewa bazan rayuwaba shine dalilin da yasa nace ku zo dan girman Allah ku ajjeni ku ajjeni na samu na amayar da abin dake raina kafin na koma ga ubangiji.
Nihal na kuka basama da Samiha na kuka wiwi momy kuwa ta rasa mai ke mata dadi duk dakiyar zuciyar Yaya Dr sai da ya tausayawa nihal,shi kansa hankalin sa tashi saboda yanayin yadda yaga halin da take ciki tabbas ya tausaya mata.
Suna karasawa asibiti aka shiga da ita daga baya likitoci suka zo sukace inde ba ayi mata aikiba za a iya rasata ita da abundake cikin ta nan momy ta kira dady da kyar ta iya yi masa bayani yace babu komi ta wakilcesa ta saka hannu shima gashi nan zuwa nan momy ta Saka hannu ammanfa duk sun tsorata Kuma sun fidda rai da nihal.
Nan an fito da ita za ashiga dakin tiyata tana matukar jin jiki da shan wahala amman hakan bai sa ta kasa cewa a tsayba nihal Yaya Dr Basma duk ta nuna su suka zo kusa da ita kuka gaba daya suka fashe da shi banda da Yaya Dr da yayi suman zaune yama rasa mai ke damunsa ko banza nihal tare suka taso har shi kullum tana gidan su sannan tayi abubuwan alkairai iri iri agaresu bai Kamata yabari sharrinta ya lillini alkairain ta agaresu ba,nan ta bude bakinta da kyar dan Allah ku yafemin bana son naje kabari da zunubanku duk suka bude baki dan Allah kibari nihal Inshallah zaki sami lafiya zamuci gaba da rayuwarmu kamar yadda mika saba abaya komi zai dedeta,Basma tace na miki alkawarin xan baki aminci fiye da yacca na baki a baya zan kaunaceki fiye da yacca na kaunaceki a baya nihal kidena wannan maganganun inshallah bazaki mutu ba.
Juyowa tayi tana kokarin yiwa Yaya Dr magana fuskantar hakan da yayi ya matso kusa da ita ki kwantar da hankalinki nihal duk min yafe miki inshallah komi zai tafi dede Kuma zaki sami lafiya.
Nan yayi sauri ya bar gurin da sauri domin kuwa shi kade yasan mai yakeji baya son kuka ya kubce masa a gabansu.
Momy ce ta matso kusa da ita ya fashe da wani matsanancin kuka nan tayiwa yarta addu'a ta kuma yi mata fatan nasara inshallah za ayi lafiya lau aikin da yardar ubangiji.
Anshiga aiki anbarsu kowa da tunane tunane aransa can sai ga dadyn nihal ya zo shi suka ce masa anshiga da ita shima kuwa ya tsaya jiran tsammani.
Bayan wasu yan mintuna likita ya fito ya fadi musu alhamdulillah ansami nasarar cire abin dake cikinta ansami da na miji amman ita Kuma Allah yayi mata rasuwa...............
Innalillahi wa inna ilahiee raji'un tashin hankali ba a saka maka rana ita Kuma mutuwa ba a sanin lokacin da zata wakana shikkelau fa rayuwa kelan ubangiji Allah yasa mucika da imani yasa muyi kyakkyawan karshe.
https://chat.whatsapp.com/FdN9LskESVf6ESy63R3QWf
CREATED AND WRITTEN
BY
ZEEY NASEER
*🌙MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION'S🌙*
We shine all over the world
https://www.facebook.com/profile.php?id=100094397072466
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~~~~~~~~~~
Page 34
Ba tare da sun luraba kawai kara sukaji suna wai gawa sukaga ashe momy ce ta fadi da gudu dady yayi kanta su kuwa duk cikin su babu mai karfin da xai iya daga kafarsa daga gurin dukkanin su babu wanda ya iya ansar dan da kyar yaya Dr yayi karfin hali ya karbesa,ya rone fari tas da shi kyakkyawa.
Samiha da Basma kuwa sun rugeme juna banda kuka babu abinda sukeyi domin kuwa na daya daga cikin ranar da baza su taba mantawa da ita a rayuwar suba nihal Masoyiyarsu da suka ta so tare ta mutu ta bar duniya.
Nan aka dauki momy aka wuce da ita emergency dady yayiwa Yaya Dr umarnin da ya bawa su Basma yaron ya mika masa mukullin mota yace yaje ya kirashi xai je ya anso gawar sai su tafi.
Kamar de yadda yace masan hakan yayi,andakko gawar nihal alokacin ne hankalin su ya sake gigita suka dimau ce sukamanta cewa a asibiti suke,a yunkuri dady da ca zaiyi su zauna anan saboda momy amman ina ya fuskanci gwammah a tafi gidan dasu nan ya saka su agaba yace su tafi mota.
Ya daga waya ya kira kanwar momy yace ta zo asibiti yanzu yakuma yi mata kwatancan dakin da xata shiga idan ta zo,nan ya wuce tunda ya sami wacca zata kula da momy.
Kafin suje yakira yan uwa da abokan arziki abin ka da mutum mai ahali kofar gidan har yayi dankam da mutane,nan aka shiga da nihal aka shiryata aka saka mata tufafinta na gaskiya tufafin da shine dukkanin managarcin tufafi duk kudinka duk mulkin ka,bayan ankammala shiryata akace mahaifinta ya zo ,ya shiga ya ganta yayi mata adduoi daman ita kadece yar su balla ace za a kira kannnenta.
Ana haka sai ga momy da kanwarta sun shigo da mamaki dady yace "Ya akayi kuka baro asibiti"ta farakane tace "Dole sai ta zo taga gawar nihal kafin akaita".
Nan ta shiga dakin ta tsugunna akan gawar nihal tace "Hakika nihal ke yarinya ce mai hankali da tarbiyya ke yarinyace mai gudun duniya,amman sai gashi lokacin da rayuwanki ta zo karshe kika lalace ki ruka aikata abin da ba dede ba,bansan dalilin hakan ba,amman Ina godiya ga Allah da sai da kika shiriya kika tuba tunkan mutuwa ta zo miki kuma nayi miki alkawarin zan so danki fiye da yadda na soki,zan kula dake fiye da yadda kika kula dake,Allah yayi miki rahama nihal".
Bayan ta kammala ta fito tacewa dady "Ina ganin yakamata abar Basma da Samiha suga gawar nihal domin tabbas sudin tamkar yan uwane agunta"
Hakane saka ayi musu magana nan akace suje suganta "Suna shiga ganin nihal cikin likkafani a daddare kowanannan su kukansa ya dawo sabo ji kake jigib jigib gaba dayan su sun fadi kasa babu mai motsi cikin su.
"Innalillahi wa inna ilahiee raji'un"nan akadaukesu akayi dakin momy dasu aka dauke gawar nihal domin kaita gidan ta na gaskiya na hakika.
Bayan antafi momy ta zo ta watsa musu ruwa duk suka farfado.
Nan ta xauna kusa da su tace "Nasani cewa Kun shaku da nihal amman hakan ba zai sa nace kuyi hakuri ku fawwalawa Allah ba,bata da wani gata agurinku illa kuyi mata addu'a ubangiji Allah yasa ta huta".
Nan momy tayi ta musu wa'azi,fitowa tsakargida sukayi Samiha ta gano momy ashe da ita akayi sutura,can ita ma Basma ta gano mamanta duk sun zo su ashe.
Da daddare lokacin Jama'a sun ragu wadan da suka zo daga wasu garuruwa kuwa sun sami makwanci sun kwanta,nan momy dady yana daki taje ta samesa ta mika masa takard gashi wanann likitane ya bani bayan na farfado yace nihal ce ta bashi bayan ta haihu da yake sai bayan anceto abin dake cikin ta ta rasu.
Karba dady yayi yana budewa ya fara karantawa "Bani da karfin da xanyi dogon rubutu amman dady momy dan Allah kutaimakamin kusakawa yaron da na haifa sunan yaya Dr yayan Samiha "
Mamaki ne ya cika su gaba daya tom mai yasa zatace asaka masa sunan sa,kodan bakomi bane watakil girman zumunci da amincin dake tsakaninsu.
Ranar da akayi uku ranar akayiwa yaron huduba da (SURAJ).
Bayan su Samiha sunzo momy take ce musu ansakawa yaro suna Suraja kallon kallo suka fara tom ko suna da wani dan uwa Suraj,nan momy ta basu labarin duk abin da yafaru da wasikar da nihal ta bada har dakko musu ita tayi.
Bayan tashin momy sabon jimami suka kafa tabbas nihal na matukar son yaya Dr Samiha ta juyo tace "Basma mai yasa nihal bata zo ta sameni ba tace na barmata soyayyyar saba,mai yasa bata zo ta rokeniba"Bamsa watakil tana tunanin baza ki iya sadaukar da soyayyyar ki bane kai innalillahi wa inna ilahee raji'un.
Har akayi aka gama zaman makoki babu wanda ya dawo dede cukinsu .
Ranar sun koma gida Samiha take fadawa yaya abin da yafaru ta juyoo tace "Yaya Dr nayi da na sani a rayuwata Yaya Dr na so ace nihal tabi ta hanya mai sauki wallahi da bar mata kai zanyi amman sai tabi ta hanyar da ta cutar damu wallahi tabbas nihal ba karamin so take maka ba,Allah yayi miki rahana nihal,haka Samiha tayi ta fama kamar mai sun batu Yaya dr kuwa yarasa mai zai ce mata Ida nuwansa sun kada sunyi jajir kai kana gani kasan yana cikin matukar tashin hankali.Mikewa yayi Ina zakaje yaya Dr zan kwanta Samiha bana jin dadi tom sai da safe .
Samiha ita ma ta tashi ta shiga daki bacci kaurace mata yayi ta kasa tana ta tunanin nihal saboda ita gani take kamar ita ce ta jefa nihal cikin halin da ta shiga da sauya rayuwar ta da tayi.Da taga baccin ba xuwa zai yiba ta tashi taje tayi alwala ta zo tayi sallah....
A bangaran yaya Dr kuwa bai san lokacin da hawaye ya fara zubo masa ba,saboda tabbbas idan yace bai taba son nihal ba yayi karya sai de soyayyyar da yakeyiwa Samiha ita ce abin da ta rufe masa Ido daga soyayyyar kowa,tabbas nihal yarinyar kirkice Kuma shine sanadin da yasa ta fara zuwa gun boka tunda da lokacin da ta fara turo masa sako a waya ya kirata sunyi magana ta fahintar juna bai wulakantataba tabbas ya tabbatar da cewa da haka bata faruba,shima yayi kuskure girman kansa bai amfana masa komi ba,Allah yayi miki rahama nihal.
Washegari da safe momy din nihal taje tana gyra dakin tana daga filo taga takarda ta dakko ta fara karantawa duk wani abu da yafaru tsakanin ta da su Basma da Samiha sai da tabawa momy labarin sannan ta fada mata tunda take bata taba aikata zina ba,sai da ta fara zuwa gurin boka ya nemi dole sai ya kwanta da ita tukunna aikin su zai yi,anan ta sanar da su cewa
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 15