in huta, don bazan iya rayuwar ba. Tun da har ina son ka Al’ameen akan me bazan so abinda kake so ba, ko mene ne shi balle kanwarka ta da, Intisar?�
Ta dago ta dibeshi cikin ido, babu komi ciki kwayar idonta face gesture (motsi mai nuna zahirin abinda ke zuciya) ta ce,
“Al’ameen ka tuna son Saratu ne fa ya kwantar da kai kamar ba zaka rayu ba, baka tunanin nima in na rasaka ba mamaki irin halin da zan tsinci kaina ciki kennan? Zuciyarka ce ke ciwon da har abada bazaka warke ba saboda tunanin ka rasa wadda kake so. Imagine yadda kake jin Saratu a rai haka nima da baka so nake jin ka.
Na jure huldar ka da mata bila-adadin a Miami, akan me bazan iya jure wannan kalilan ba? Don mace daya? Ni dai ko ukku zaka karo in har zaka barni a matsayinda nake, to zan iya jurewa. Abinda ma nayi dazu wallahi zuciyace ta ciwo ni, don ina ganin Babana da ya haifeni bai damu da farin-ciki na ba.
Amma yanzu na gane ‘So daga Allah ne�, babu kuma wani abin halitta da ya isa yayi yadda yaga dama da shi sai ko Ubangijin daya assasa mana shi a ruhi, don haka bana kishin son da kake wa kanwarka illa in roki Allah nima ya sammin ko gutsire ne daga cikin wannan son na Intissar a zuciyarka Ameenu.�
Ya kai hannu ya dagota daga durkuson da tayi bisa kafafunshi ya zaunar ta gefen shi ya ce, “Ihsan ba haka bane, ba wai bana son ki ne ba, bana sonki zan aureki? Illah don dukkanmu mu samu kwanciyar hankali.
Ki diba kiga tun dawowarmu gida muke cikin matsala, ke matsalata da ke na farko Babar ki bata sona.
Na biyu kina da azababben kishi. Irin rotsen da kikewa mata a turai a kaina yana tsoratani, kar in hadaki da yarinyar mutane ki kashe musu ‘ya ni kuma bazan juri wannan ba, iyayenmu ma bazasu yarda ba, bayan haka ma nasan Saratu akan haukar da taga kina yi ne ta furta abinda ta ce.
Ba abinda zai sa in hakura da Intisar yadda kema bazaki iya hakura da ni ba, ba yin kaina ne ba wallahi daga Allah ne. Kiyi hakuri I don’t meant 2 hurt u amma ko daya ban taba tunanin akwai macen da zan so ba haka a rayuwata har muka dawo.
Tun ganina na farko da ita ban kara tunanin kowa ba, ban kara tunanin komi ba sai ita, ban kara dubar wata mace da sunan so ba sai ita. To mai wannan son idan ya sami abin nan da yakeso Ihsan ina zai iya adalci? In zo Ubangiji ya azabtar dani kan danne maki hakkoki? I’m sorry to say, ko a yanzu bana jin zan sake samun nutsuwa ban sami Intisar ba, ina tsoron danne maki hakokki da ke kaina, don haka kiyi hakuri Ihsan mu rabu, don hakan shine kadai hanyar samuwar peace of mind na kowannenmu, watakila hakan na nufin wani kebantaccen al’amari garemu duka? Sai kiga Allah ya musanya maki da mafi alkhairi na.�
Ihsan kuka take tukuru, ba abinda take fadi a zuciyarta face la’ana da Allah ya isa ga duk ma wata mace mai sunayennan uku: Saratu, Intisar da Fatima. Tsakaninta da Intissar Li’ilafi dubune Allah ya isa kwando-kwando. Cikin dan lokaci duk ta mallake mata zuciyar miji tun kamin ya aure ta, Allah sarki! To ina ga ta shigo gidan?
Ashe lokaci yazo da zata koma gefen Aminu tayi kallon rayuwarshi da wata? Ita kuma haka Allah yaga dama da ita? To amma yaya zatayi, tunda ta amince son shi take da zuciya daya. Ta tsinewa kasar haihuwarta da tayi mata wannan cin amana. Inama batace su dawo Nigeria ba! Shin a duniya zata ki wani dan adam kamar yadda ta tsani Saratu-Intisar?
Ta tsani sunan, bata son ji, to amma me? In har da gaske tana son Al’ameen Bello, kenan dole ta tursasawa zuciyarta kaunar Saratu Bello? Tunda ta rigaya ta zamo wani bangare na gangar jiki, Jinin jiki, ruhi da kalbin Al’ameen?
Sai ta matsa sannu a hankali ta kara shigewa jikin Al’ameen kamar yadda yake a al’adarta, tamkar magen da ke jin sanyi, kanta ta kwantar bisa kafadunshi, cikin low and weak voice (mara amo kuma rarraunar murya) tace
“Aminu, ni fa na amince ina sonka, to akan me bazan so abinda kake so ba? Na rantse da Allah na amince ma auren Intisar da zuciya daya, ni ce ma zan je in rarrasheta, tunda akaina tace ta fasa aurenka.
Zan kuma yi kokarin danne wannan kishin da baka so, in kuma maganar Ann ne Allah ta saduda don ita tace in je in yi jiyyar ka a asibiti, na baka hakuri ta gane batayi dai-dai ba, don haka ka fidda shakku akan mu, don ta adalci ai ni ce mai karfafaka da kayi, kuma hakkina ne in shiga yi maka addu’ar yin adalci a tsakaninmu.
With my 100% go ahead (da goyon bayana dari bisa dari) ka je ka rarrashi Intissar ku shirya, kuma kada ka kara marar mun (little sister) na Al’ameen bana so..� da haka ta juya akalar hirar ga wadda yafi so suyi, tun suna Miami.
Tuni Al’ameen ya mance da duk wata damuwa da yake ciki, kuma hakika sunyi missing (kewar) junansu ba kadan ba, tun ranar da suka baro Miami basu kara samun kwanciyar hankali ba.
Don haka kowanensu cike yake da kishirwar dan’uwansa sun ma mance da matsalar data shiga tsakaninsu a baya. Sai Al’ameen yaji ranar tamkar irin renakun amarcinsu a beaches da resorts din Miami cikin bikini. Daga baya ma tausayi Ihsan ya rika ji, da yadda yaga jikinta na rawa, ya dubi irin cuzgunawa da maganganun soyayyarshi da ya yaba mata yanzun amma bata damu ba, burinta kadai ta nuna mishi kauna.
Sai ya janyo matarshi shima aka barje, ya kuma alkawartama ranshi ko ya samu Intisar ko bai samu ba, ba zai taba wulakanta ta ba, don ya amince Ihsan mai kaunar shi ce tsakani da Allah ba don wata tsiya daya mallaka ba, mai kuma kaunar duk abinda yake so.
A washegari wayar Ann ce ta fara tada ita daga barci, ta gode Allah Al’amin din ya shiga wanka tana cewa “Hello� Ann to shiga zaginta da cin mutunci na fitar hankali ta ce,
“kuma kin bani kunya Ihsan, mace kamarki, da gata da ilmi da aji ta dinga bin namiji daya yana garata kamar gare-gare abin wasan yara?
Wallahi kin zubar da mutuncinki, kamar yau ne ina nan a zaune ranar daya wulakantoki da kafarki zaki nemeni tunda baki sayawa kanki darajjah ba, ana nema a siyo miki kina watsarwa.� Ta ce,
“To Ann, ya na iya? Ina sonshi, ya zanyi?�
Ta kara kular da Ann to kwantsama mata ashariya ta ce,
“Son banza? Idan so cuta ne shi hakuri ba magani bane, har wata tsiyace Aminu Bello? Yana likita kina likita ki tsaya yana kada miki bindi?� Ta ce “lala! Ann, Aminu fa Malami na ne, ko a (ST. Bathalomew), daga gareshi na soma koyon psychology da psychiatry bafa wai likitan kwakwalwa ne kawai ba, koko wanda za’ace ga iyakacin field din shi kamar ni ba Malami ne a jami’o’in Miami. Kina ganinshi haka dan yaro Allah ilimin shi ya zarce tunani.�
Haushi ya ishi Ann, Ihsan ta yi nisa bazata taba waiwayowa ba. Luv is overall! Ta ja dogon tsaki ta ce,
“Kin yi asara dai, banza.�
A lokacin yana tsaye ya sakarwa kanshi shower amma bugun da zuciyarshi keyi ya tsananta, zafin da ke azalzalar kirjin shi ke neman kayas da shi, sai a lokacin ya tuna rabon da ya sha magungunan shi tun safiyar jiya.
Duk wata dibara da yake jin zai iya, a matsayin shi na likita yayi domin isa ga dakin barcin su inda ya aje magungunan cikin lokas, hannunsa na dama dafe da kirjinshi hakannan bugun zuciyar na kara karuwa fiye da farkon farawarshi, yana bin bango sannu a hankali da taimakon Allah ya isa ga lokar, yayi amfani da hannun hagunshi wurin fiddo magungunan.
Ihsan ta shigo, ganin halin da yake ciki bata san sanda ta saki flask din shayin da ke hannunta ba da tray din gaba daya, ta karasa da gudu ta tallabeshi, ta ce,
“Aminu, wayyo! Kirjin ne? Ka ga tun jiya baka sha magani ba, ka manta me Alfered ya ce, wayyo ni Ihsan na banu.�
Ya yi mata alamar ta kawo mai ruwa, ta jinginar dashi jikin gadon ta tusa mai filo a baya ya jingina sosai, da gudu ta sake yin kichin ta fiddo ruwa mai sanyi da tambulan ta dawo ta mika mai kana ta cicciri magungunan ilahirin jikinta babu inda baya rawa, tasa mai abaki tasa mai kofin ya kora magungunan da ruwa, daga shi har ita sunyi wujiga-wujiga idanuwansu sunyi jazur. Ta ce,
“I’m Sorry� ya dubeta da jan idon yayi murmushi itama tayi karfin hali ta kakaro iya fatar kyakkyawan bakinta tace “You’ve to rest, pls Aminu, I don’t want to lose u, ka dinga kula, don Allah?�
Wasu hawayen suka silmiyo ta gefen idonta. Ya kallet cikin jimami bai san me zai ce mata ba. To ba zai iya fadar mai dadi ba, da yace da ita yadda bata son ta rasashi haka shima baya son rasa Intisar.
Tausayinta ba inda bai bi tsoka mai gudanar da jinni a jikin sa ba, to amma ya zaiyi? Kamin ta ankara barci mai nauyi yayi awon gaba dashi, ta sauka gefen gadon ta zuba mishi ido kuri, tana mai kara kaunar kowacce halitta a jikinsa.
Haka kawai taji gabanta na faduwa lokaci-lokaci a duk sanda ta dubi Al’ameen, ta kai hannu ta share mai gumin da keta yankowa daga goshinsa, da taga wannan bazai mata ba, sai ta mike ta dauro alwalla da ada bata damu da ita ba, ta bude Al’kur’anin shi dake aje bisa durowa ta soma karanto mai ayoyin neman sauki data koya daga gareshi.
Karfe hudu na yamma ya mike tangarau cike da kuzari tamkar wanda bai da wata lalura, cikin hamzari ya fada toilet yayi (freshen-up) ya dauro alwalla kamin ya fito Ihsan ta shigo rike da kofin tangaran cikke da danyar madarar shanu mai sanyi wadda shanta ya zame wa Aminu lazim a duk yammci, ta aza bisa ‘centre table� ta koma ta shiryo reduced fat and salt meal bisa dan madaidaicin tray wato abincin masu cardiac/hypertension problem.
Ta zauna gefen gadon tana kallonshi yana sallah, zuciyarta cike da jin dadin ganin samun saukinsa, ya shafa Addu’an ya juyo ya sakar mata lallausar murmushi ba tayi nawa ba wajen mayar masa, yaja yatsar kafarta dake kusa dashi ya daga gira cikin tsokana yace
“Kai Ihsan, irin wannan tagumi haka, ranar da na mutu ashe ke sai asibiti…� ta yi sulu ta rufe mai baki da tausasan yatsunta, kamin ya ankara sai hawaye sharr! Wani na korar wani.
Ya janyo matarshi tsantsan yana dariya ya ce,
“I’m Sorry, haba Ihsan kamar ba likita matar likita ba. Ni na isa in mutu, ban aje masu yi min Addu’a ba? So take care of urself b’cos I care!�
Ta dago ta dubeshi cikin rauni da karaya.
“Ka manta ne mahaifan ta lalace already? Are u dreaming? (kana mafarki ne) Ban ki ba dai daga Little Sister Intisar zamu samu masu yi mana Addu’a a gidan nan.� Ya girgiza kai cikin rashin kulawa da maganarta, ya ce,
“Ai ni yau Baban Babe ne, to Maman ga bakina a bamu abinci…� ya bude baki har ya bata dariya, ta dauko kofin madararshi sai ya girgiza kai ya maida hannunta inda ta dauko kofin yana cewa
“I need only you (ke kadai kawai nake so).�
Tai kasa da murya, sai in har ka kasa kunne ne zaka ji cewa da tayi
“U are always welcome!�
Ita dai al’amuran Al’ameen Bello, daga jiya zuwa yau na bata mamaki. Haka kawai ta ji jikinta yayi sanyi, kuma so da tausayin Al’ameen na kara dawainiya da ita, second bayan second, minti bayan minti, awa bayan awa da bazata ce so da tausayin Al’ameen ne ba.
How much do you like this story?
5/11/22, 08:13 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book three
*@Takori*
Page8ï¸âƒ£
A kalaminshi na karshe, wadanda kuma suke kalmomi na karshe a littafin da alama ma yanzun ya rubuta;
‘To in haka ne shi meye ribar sa a rayuwa? Da me ya yi riba da me ya tsira? Bai gani ba! Bai ci riba da son Intisar ba, bai ga amfanin ilmin daya nema don ta huta da shi ba, tunda Al’ameen billonnaire ne, baya bukatar a agaza masa, bai ga ranar da son da ya shekara yi mata yai masa ba. He is but a real loser! To amma tunda don ita ya nema, shi mai mallaka mata duk abinda ya mallaka a duniya ne koda kuwa ta auri Aminu ne ko waninsa, tunda dama tunda fari ya alkawartawa ransa hakan.� Ragowar bata iya ta karasa ba, saboda kwakwalwar ba zata iya ganewa ba…�.balle ta fassarawa zuciyar ta!
Inteesar ta daga ido sama tamkar mai kididdiga adadin juyawar fanka, wasu irin hawaye ne marasa dandano bare launi ke tsere ‘one after the other� (bi-da-bi) kan kyakkyawar farar fuskar ta. Abubuwa da dama ta tuna a wannan lokacin, wato kuruciyarsu da Faisal can baya.
Ashe dama abinda take ji game da shi a lokacin itama ‘son� ne? Gaba daya jikinta ba inda bai diba ba cikin kaduwa, dimuwa da razana, a take zazzabi mai zafi ya soma kokarin rufeta, saboda karkarwa da ilahirin jikin ta ke yi littafin ya zame ya fadi kan kafarta, dai-dai lokacin da Faisal ya murda kofar bandakin ya fito gabadayan sa.
Daure da towel faffada iya kungushi yana ‘combing� sumar kanshi sai ya daskare cikin matsanancin mamaki, suka dubi juna a gaggauce idanunta face-face da hawaye, tayi saurin juya mai baya, kana ta doshi kofa tana cewa.
“Dama Daddy ne yace in kirawo ka, kada a kara zama cin abinci kana gida baka zo ba� ta sheka da gudu zata bar dakin abin tsautsayi, sai gilashin ya fado ta kuma taka shi da kafarta hannun ya lankwashe amma saboda quality (karkon) gilashin bai fashe ba, kamin ta russuna ya isa gareshi sai suka russuna a tare, hannunshi ya riga isa bisa gilashin don haka natan sai ya sauka akan nashin, shi yai nasarar daukowa, yasa karfi wajen gyara lankwashewar da yayi, a yayin da ta jingina da bango idanunta a runtse, hakannan hawayen basu fasa kwarara ba kamar an sunce fanfo.
Ba komi take tunawa ba a lokacin face ranar da ya cire mata gilashi ta baya, lokacin ana shirye-shiryen tafiyarsu Riyadh ita da Khaleel, ta dinga bin inuwarsa a hasale tana “bani gilas dina Ya Faisal, kaga bana so� haka dukan da ya sha da filo da wakokin da ya kanyi mata na “come on beautiful Babe, Maman?�
Cikin nutsuwa ya maida mata gilashinta, suka sake dubar juna a susuce sai ta kara da gudu.
Ya dade anan tsaye yana tunanin me ta gani ya sata kuka? Me ta gani ya gigita ta haka? Bai yi tsammanin zata sake kulawa da al’amarinsa ba a yanzun dai da ta ke cikin son Yayan shi Ameenu?
Intisar dakinta ta nufa agigicenta ta maida kofar ta rufe ta murza key. Ta jigina da kofar ta sake runtse idonta da karfi, tamkar mai son farkawa daga mafarki. Abubuwanne ke tariyo mata can baya tamkar a majigi. Ta tabbatar Faisal shine mutumin da ta fara so a rayuwarta kuma mutumin da bazata taba samun mai kaunarta a duniya tamkar shi ba. Tausayinshi, yagama narkar da duk wani tunani da ta mallaka. Ta zargi kanta da cin amana ta kuma kirayi kanta da ‘butulu� dan adam mai manta alkhairi.
To amma wani bangare na zuciyarta ya kalubalanci hakan da hujjar cewa, a lokacinta da Faisal tsammani suke su ‘yan uwan junane sabanin haduwarta da Al’ameen. Hakannan Al’ameen shi ya koyar dai ta son shi, shi ya kimsa mata son shi karfi da yaji, bata san so na soyayya ba sai akan shi, don haka bata jin Allah zai kamata da wannan hakkin na Faisal sai dai kaso mafi rinjaye na zuciyarta na karfafata da cewa, yanzu ne ya dace tayi wani abu, yanzu ne ya dace ta sadaukar da kanta da soyayyarta (son da takewa Al’ameen) don nunawa Faisal wannan kaunar da ya wanzar da rayuwarshi nuna mata, tun tana a tsumman goyo. To wai ma ya akai ta so Al’ameen? Bata sani ba, illa may be because he is unikue (watakila don shi din na daban ne).
Ta yaya? Ta yaya zata nunawa Faisal din kauna bayan a yanzun ya nuna baya da lokacinta ma? Ta tambayi kanta, lokaci guda ta bawa kanta amsa da cewa ta hanyar auren shi mana Intisar? Amsar tayi mata nauyi a baka da zuci, wai Intisar matar Faisal in banda Allah mai juya al’amura ina wannan abu zai taba zuwa masu a rai?
A lokacin ne kuma ta tuna shima fa Faisal dan Hajiya ne! Wannan zuri’ar da tayi alkawarin ba zata sake kulawa ba! Wannan zuri’ar data nuna mata kiyayyar da ba wani mahaluki a doron kasa da ya taba nuna mata! Wannan zuri’ar da idan ta aura, ta sake jefa kanta cikin bala’I da masifa ne watakila ma fiye da na baya. Bayan yanzun da cikakken gatanta, ga Aunty, Daddy, uwa-uba dangi da uwa mahaifiya masu so da kaunarta. Zuri’ar Haj. Nafi? Ta girgiza kai da karfi, ire-iren maganganun Haj. kadai ke dawo mata wasu na bin wasu.
“Wai me yasa kike son ‘ya’yana ne, bayan ni na tsaneki? Har kullum mutum kanyi nisa ne da jinin makiyin shi, Saratu banda ke! Don naji ance komi Faisal kike ambato, har kuka kika yi da ya bar kasar, yayi maki kama da ‘ya’yan mutsiyatan kauye ne?
So nake bandakin nan ya fiki fari, ya kuma fi Faisal di na kamshi� Faisal ne ya sa miki suna Intisar, kuma da na ne, mallakina ne, don haka daga yau na kwace�. Ke Jikar Jummai ce, Jummai uwar Saratu�. Daga yau kika sake koda kallar min ‘ya’ya, sai na sa wuka na tsokale wadanna makafin idanun munafurcin, kina jina? Ta tuna amsar da ta baiwa Hajiyar a lokacin. A yau ma sai ta samu kanta da nanata su, sai dai sabanin sunayen da ta kira a wancen lokacin a yau cewa tayi…ba Faisal ba, ba Aminu ba� duk wani jininki ma idan na sake daga ido na dubeshi ba da kiyayya ba, ki ce ni shegiya ce na amince!
Ta kudurce a ranta daga yau dukkansu ko gaisuwar dayansu bata so. Aure kuma in har sai da ‘ya’yan Haj. Nafi ne, to ita Saratu ta yafe!
Ba irin bugun da su Hunainah da Anti ba suyi ba amma Intisar bata bude ba. Wuni tayi cin kuka da nadama mara amfani. Ta rasa meyasa rayuwar ta ke da matsaloli iri-iri tun tana jaririyarta. Dagabaya kuma tayi tunanin akan me zata bari soyayyar ‘ya’yan Hajiya ya wargaza mata rayuwa? Komi fa mutum ke daurama kansa don Allah baya daurawa rai sai abinda zata iya.
Ta yankewa kanta ‘solution� na karshe tayi murmushi ita kadai. Ta san cikin Iyayenta kakaf, babu mai matsa mata akan wannan kudurin nata. Sai ko Mamarsu Hunainah ita ko bata jin ta don ta tabbata Daddynta zai bata goyon baya dari bisa dari.
Ba ita ta fito ba sai karfe hudu na yamma, shi din ma azababbiyar yunwa ta fiddota. Su Hunainah na magana da Anti Hajjo a waya ta ce,
“Gata nan ma ta fito� ta mika mata wayan ta ce,
‘Hello Aunty� Hajjo ta ce,
“Ba wani Yello Aunty, nikan baki dauke ni Antin ba, da ko menene ke damunki da kin kira ni kin gaya mini, Saratu shin me yayi zafi ne haka? Na ji an ce tun safe kin rufe kanki a daki kina kuka.
Na dauka kasancewar mu kusa da ke, da tabbacin da kike da shi na iyayen kwarai ya isa ya sanyaya maki zuciya? Wannan kuntata duk na menene?�
Tayi shiru, Idanuwan ta sunyi rau-rau kaman ta saki kuka. In da Anti Hajjo ta san yadda take jin zuciyar nan tata, da bata zargeta da kuntatawa kanta ba.
Ita ba sauyin Iyaye ya dameta ba, damuwarta daban ne, daga ita sai Ubangijin ta suka santa. Hajjo ta ce,
“Koda bakya kaunar mu Saratu, mu ne dai iyayenki, kuma ba’a sake iyaye sai iyayen daki. Wannan rashin sakin jikin da kike damu ban sani ba ko don ki na ganin bamu isa mu zamo iyayen ki ne ba?� (Aunty Saratu ce ta koya mata, ba’a jin damuwan ta sai da dabara) Ta sa kuka da karfi tace “Aunty Hajjo me ya kawo wannan maganar?
Na rantse da Allah ba haka bane, ni abinda ke damuna daban ne.�
Hajjo ta ce, “Don kin ce kin fasa auren Al’ameen? Ke, yarinyar ki da ke kar ki bari ciwon hawan jini ya kamaki akan soyayya. Shi Al’ameen din yace dake ya damu? Yana can tare da matarshi Allah kadai yasan farin-cikin da suke ciki sai ke ki bi ki kuntatawa ranki?�
Ta share hawayen da ke zuba mata da bayan hannu, dai-dai sanda dan halak din ya yiwa falon tsinke, matarsa na biye da shi tamkar ta shige jikinshi don tsatsiba, ya zarce kai tsaye har inda take, ya ja tebur inda take ya daura kafa daya, dayar kuwa na kasa tamkar mai son jin kwakkwafin abinda ke sata kuka a waya.
Ihsan ta bisu da kallo kana tabi bayan su Hunainah da sukayi cikin dakin Anti. Intisar ta bude baki domin ta bawa Antinta amsar da tai niyya amma kwarjinin Al’ameen ya katse komi. So ta ke tace har wata tsiyace Al’ameen din da zata kuntatawa kanta akansa? Ita ba shine damuwanta ba.
Hajjo ta ji tayi shiru ta cigaba da cewa, “Ni dai shawarata a gareki Intisar, ki fidda damuwar komi a ranki, ki koma makaranta. A shirye muke damu nuna maki kauna ta kowanne fanni. Na san kina son Al’ameen, so bana wasa ba. Tunda har kika kusa salwantar da rayuwar ki akan tunanin bazaku iya auren juna ba.
Amma abinda na ke so ki gane shine, ki yi tunani, ke yarinya ce karama har yanzu cikin shekarun (teenage), wannan gigin son duk na dan lokaci ne, da anyi auren an haihu shikenan ya zama tarihi sai zaman hakuri da juna.
Abinda nake so da ke shine ki tsaya ki gina rayuwarki a bisa tubala na kwarai, in ba hakaba ba mamaki bada jimawa ba soyayya ta ruguzata. Al’ameen ya fiki wayo, daga shi har matarshi ba tsaranki bane a budewar kai da ilmi.
Don haka ki tsaya ki nemawa kanki madogara mai kyau tukunna, wanda shine
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 24 Chapter of 38