har zuwa inda ya adana motarsa. Ya bude mata gidan baya ta shiga ya rufe, ya aje jakar a gefe ya zago ya zauna mazaunin shi, ya kakaro murmushi mai kwantar da hankali ya ce,
“Nayi fama da cuta ne Hajiya, amma alhamdulillahi naji sauki, nayi zaton an fada maki?�
Tayi ajiyar zuciya tace ban zaci abin yayi kamarin haka ba, shin me ke damun ka? Ya lumshe ido yayi murmushi, ya bude su duka a kan ta ya ce,
“Ciwon Zuciya!�
Wadannan su ne kalami mafi muni da ta taba ji a rayuwarta, suka kuma diran mata tamkar kibiya a kahon zuci. Muryar ta na karkarwa tace kai ko meke damunka, da har ya janyo hakan? Me ka rasa a rayuwa da zaka sanyama ranka damuwa? Yayi murmushi yace in kin so Hajiyana, zan iya murmurewa kamar ban taba yi ba, haka in kin so, zai iya zama ajali na. Tace (tana mai girgiza kai da karfi)
kada Allah ya nuna min wannan ranar!
Daga haka ta ja bakinta tayi shiru. Ganin ya dau hanyar gidan Babansa ta daka mai tsawa mai firgitarwa ta ce,
“Kai, ina zaka kai ni? Gidan Babana zaka kai ni! Ko baka ji ba?� Ya ce,
“Na ji Hajiya na, kuma a bisa umarnin ki nake har kullum.�
Ya karkatar da kan motar ya dauki hanyar Kaduna. Sai da tayi sallah, ta huta suna hira da mahaifiyar ta kan kayan da ta turo daga can Dubai din, ya shigo daga masallacin da ke kofar gidan, bayan ya samu jamin sallar laasar, duk suka dube shi.
Babar Hajiya, wadda ta fara tsufa sosai amma yanayi irin na hutu da daular da take ciki ke son boye tsufan nata karfi da yaji, tana ta tsokanarsa yadda ta saba amma a yau bai iya ya tanka ba, taraddadin dake zuciyarsa kadai ya ishe shi. Ta dubi Hajiyar cike da alamar tambaya tace,
“Shin me ke damun Mai gidana ne, duk ya lalace haka? Ciwo ko matsala? Hajiya ta kyabe baki tace umh masa! Ni ma haka na gan shi, munafurcin su can da su da uban su zai cinye amma ba ni ba, na fi karfin kurwar su Intasar Allah! Tunda ku sun lashe ku, to ku je kuyi ta bin su na yafewa Saratu, sai ta je ta kara jika malaminta, na yarda ita na haifawa ku, na amince yayan tara da nayi nakudar ku na haife cikin wahala da kaka-ni-kayi, duka nata ne, ni kuma ina rokon Allah ya bani masu jin kaina.�
Ta soma sheshshekar kuka. Ya ji guiwoyinsa sunyi sanyi kalau, fiye da shigowarsa. Ya tabbata rashin nasara, ya tabbata garesa, Shi kadai yasan yadda kukanta ke girgiza zuciyarsa. Ya alkawartama ran sa idan ta hanashi zai hanu, shi kuma yayi jinyar zuciyarsa har sai ta mance da Intisar! Zai zabi Hajiyarsa akanta!! Zai zabi mahaifiyarsa akan soyayyarsa!!! Zai zabi farin-cikin Hajiya akan na shi, domin samun tsira a gidan duniya da tserewa daga azabar lahira. Duk da haka zai fadi, domin ta yanke masa hukunci.
Ya zamo daga cikin kujera yazo har inda take, cikin kaskantar da kai da tsananin girmamawa ya ce,
“Hajiyana, ba mayya bace Intisar, ki daina illata ta hakan nan, ki daina fadin muggan kalami akanta don Allah? In Iyayenta suka ji zasu yi kararki. A yanzu haka tana tare da Iyayenta bata gidan mu.
Na zo ne neman amincewar ki, kan abinda zuciyata ke so da albarkarki. Ina mai neman yardar ki kan son auren Intisar diyar Aunty Amarya, a sabili da azabar sonta da ke neman hallakani. Ki ceci rayuwata Hajiya, ki ji tausayina. Ki daina laakari da hujjojin ki marassa madafa.
Intisar ta ki ni, ta bujire wa ingantacciyar soyayyar da take mun saboda ke, saboda sanin halinki na rashin kyautayi da adalci a gareta. Ki taimake ni ki nuna masu ba haka bane, ke ma uwa ce mai tausayi da jin kai tamkar sauran iyaye, ke ma uwace da ta san ciwon dan ta, take kuma son duk abinda yake so.
Bijirewar ki na nufin alamura da dama cikin rayuwata. Ba na nufina in tursasa ki bisa raayina ba, Illa ki ji kai na ki tausaya mun., ki yi min alfarma cikin dimbin alfarmomin ki da basa karewa a gareni. To a yau ma ina neman alfarmar ki irin wadda ban taba nema ba! Ina kuma mai tabbatar maki zan yi biyayya ga duk hukuncin da ki ka yanke a gare ni.�
Ya sunkuyar da kai yana mai sauraron hukuncin nata.
A zaune take kurum tana mai sauraron kowacce kalma da kowanne harafi dake fita daga bakinsa, tana kuma auna ta a bisa maauni na hankali da tunaninta. Ta kasa gasgata me kunnuwanta suke jiyo mata, ta dauki alamarin cikin irin mafarke-mafarken da take a dan tsukin game da yayanta da Intisar.
Sun fi minti talatin shiru, babu wanda yayi koda kwakkwaran nunfashi balle hadiyar miyau. Sai a lokacinne wasu zafafan hawaye suke zubo mata, wadanda ita kadai ta san ko na menene, ita kadai ta san me take sakawa take kuma warwarewa a zuciyar nan tata. Bakin-ciki ne? Farin-ciki ne? Tausayi ne? Nadama ce? Ita kadai ta barma kan ta sani.
Hukunci na karshe data yanke shine mikewa ta bar masa falon, ba tare da ta ce da shi komi ba. Alameen ya ji hantar cikin sa ta kada, yayan hanjin sa sun dunkule waje daya. Ya yi nadamar furta kalaman sa ga mahaifiyar sa, data daukaka kaunarsa a zuciyarta fiye da ta kowa a duniya. Wadda burinta a kullum shine dawwamar su cikin gata da farin-ciki.
Amma a yau, sakamakon ta shine zabar wadanda ta ki jinni a duniya fiye da kowa a matsayin abinda yake so da kauna mai tsanani, yake burin ya zamo wani bangare koko ginshiki na rayuwarsa, kuma wai har yake gaya mata in har bata amince ba, zata yi asarar shi itama. Anya Hajiyar ta cancanci wadannan kalami?
A lokacin ya ji ya tsani kan sa, ya tsani komi dake cikin duniyar kuma ya tsani ita kanta Intisar. A ganin sa duk ita ta jawo masa, samun sabani da Hajiyar sa. Yayi nadamar dawowar sa Nigeria a yau. Inama bai biyewa Ihsan sun dawo ba! Inama. Inama Sai ya ji wasu dunkulallun hawaya sun kwararo bisa kundukukin sa.
Ya mike cikin yankewar buri da fidda rai da komi na rayuwar duniyar ya nufi dakin da Hajiyar ta shiga, yasa hannu ya murda kofar sai ya jita gam-gam da mukulli.
Ya juya ga kakar sa Haj Iyami, wadda ke zaune cikin kujera tana kallonsu kawai cikin rashin fahimtar abinda suke ciki. Ya zauna a gabanta ya kama kafafunta ya shiga rera mata kuka mai matukar motsa zuciya, yana magiyar ta nema masa gafarar Hajiya, in ba hakaba bai san yadda zai yi da rayuwar shi ba.
Ta kai hannunta kansa tana shafawa tace ya isa Maigida na, ko Nafi zata yi fushi da kowa a duniya bazata yi fushi da kai ba! Ta na sonka, son da kai din baka sani ba, na tabbata ba kai ka sata kuka ba, ita kadai tasan dalilin kukanta. Ka tashi ka tafi gida, dare yayi, gobe ka dawo lokacin ta nutsu sai mu zauna a yi maganar.
Ina! Alameen ya tabbatar mata bai zuwa ko nan da can batare da ya san hukuncin da Hajiyar ta yanke a kansa ba. Ta kada ta raya harta gaji tace tunda kwana zaka yi, to ga makullan sassan baki can bisa T.V ni zan je inyi sallah. To a lokacin ne shima kunnen sa ya jiyo mai kiraye-kirayen sallar maghriba da ake ta yi a masallatai, ya mike ye fita, a masallacin ya samu dabinon da yai buda baki, ya sami jami a masallacin cikin gidan, bai baro masallacin ba saida akayi sallar Isha’i tare da shi, ya sake mikewa ya bade shafa’i da wutri.
Ya dade cikin sujjadarsa, yana mai zubar da hawaye, cikin kai kukansa ga Allah subhana, mai juya alamura yadda yaso, yana mai rokon sa da ya fidda Intisar a zuciyarshi, tunda Hajiya bata son ta, ya karfafa masa raunanniyar zuciyarshi, ya bashi ikon yin biyayya ga mahaifiyar shi, ya karkato da kafaffiyar zuciyarta ta yafe mishi! Ta fahinci ba ya da nufin tozarta ta, kuma ba shi ya daurawa kansa kaunar Intisar ba.
Abu ne da shima yafi karfin sa, yafi karfin iyawar sa, yafi karfin duk wani kokari da zai yi ya fidda ta a ran shi!! Ya bashi hakuri da dangana, ya sa yafi karfin zuciyarsa, domin shi kansa ya san yana cikin sahun mutanen da basa iya controlling zuciyar su musamman akan abinda ta ke tsananin so.
Har zuwa sanda ya koma cikin gidan, Hajiya bata bude kofarta ba, abinciccikan da Kakarshi ta sa shi a gaba da su domin yayi buda baki, bai iya ya hadiyi ko loma daya ba. Ya kara ramewa, ya kara zabgewa, ya kara susucewa yini daya rak, fiye da yadda yazo garin.
Sai da Assalatu Hajiya ta fito domin gabatar da alwallar sallar asubahi, ta ji wani abu ya tokare mata kofa sai rabewa tayi ta fito. Ba komi bane illa kyawawan kafafun Alameen da ke kwance a bakin kofar ta barci na dibarsa kadan-kadan, har ranta ta ji matukar tausayin shi. Wai Aminunta ne wannan?
Mutum maabocin kuzari, fara, kwarjini, ilmi na kwatance da cikar zati ya koma haka, duk a dalihin soyayyar Intisar. Wasu hawayen takaici suka zubo mata. Ba shakkah, Intisar, mayya ce! Furucin da ta dade tana yi a kan ta yau taga tabbacin sa.
Ta saki kurwar Faisal da Daddy Makarfi yanzu kuma ta dawo ta Aminun ta? Bazata taba amincewa ba!! Za tayi fito-na-fito da yarinyar nan a karo na biyu har sai taga karshen ta. Za tayi mata mai gabadaya ita da Saratu in ba hakaba, ta tabbata watarana daga ita har yayanta zuwa abinda ta mallaka, ba zasu tsira daga maitar yarinyar ba.
Tasa kafarta ta zungureshi yayi saurin bude ido, tare da hamzarin gurfana a gabanta yace cikin dusashshiyar murya.
Hajiya na, kin yafe mani? Tace kai ba na son zancen banza, tashin ka nayi ka je ka yi Sallah. Duk fadin gidan nan ka rasa inda zaka kwanta sai bakin kofa ta, salon ka jawo min magana ko me? Ya mike sum-sum-sum ya na fita daga falon yana waiwayonta, ta yi tsaki a ranta tace Allah ya isa tsakani na da wannan tsintattar mage.
Sai a lokacin ta tuna abinda yace da ita, wai Intisar bata gidansu, tana tare da iyayenta. Tace ni zaa gayawa karyar banza ko ko ni zaayiwa dadin baki wai don in yarda, yarinyar da aka kawo min ita daga daji, tun tana tsumman goyonta, yanzu haka ma wasu mutane Saratun ta debo aka biyasu su ce su iyayen Intisar din ne, don ta yarda a kakabawa danta to bazata taba amincewa ba.
Kwanan Alameen biyu kenan yana bin mahaifiyarsa tare da neman gafararta a bisa bacin ran daya lura bukatar shi ya sanya ta, amma taki ce masa komi iyakaci in ya dameta ta tashi ta bar masa wajen.
A na ukun ne Haj. Iyami dattijiya mai tsananin hangen nesa, ta samu Hajiyar a daki rike da hannun Alameen da bakin ciki, nadama da tashin hankali ke neman zautawa, ta zaunar da shi a gefenta amma shi din sai ya zame daga bakin gadon ya zauna bisa carpet a gefen kafafunta kansa a sunkuye, hakannan hawayensa basu bar diga bisa tafin kafarta ba.
Ta yi kira da kakkausar murya irin yadda bata taba yi ba. Ta ce Nafisa! Ke kam wace irin uwa ce? Na dade ban ga uwa mara tausayi irin ki ba. Ba haka ni da ubanki mu kai miki ba, mu kullum masu tausayi da kyautayi ne a gareki, tare da kaunar duk abinda ki ke so!
A da, na rantse na daina shiga alamarin ki da iyalinki, domin dai kin girma, amma zuciyarki ta yara ce. Shin wannan so ne kike wa Alameen ko kiyayya ce? Wannan ba so ba ne. Ba soyayya ce ta uwa ga dan ta ba. Na tabbatar miki in baki yi hankali da rayuwar duniya ba za ki yi nadama, a lokacin da bata da amfani!
Son kan ki yayi yawa Nafisa. Ita uwa har kullum hakuri take da son ranta ta barwa dan ta. Ba don a kan idona kika yi rainon cikin Aminu, kika kuma haife sa a hannu na ba, da sai in ce, ke ba uwar sa ba ce!
Daga haka ta juya ta fita. Hajiya Nafi, ta dago sannu a hankali ta dubi Alameen, ta hadiyi wani daddatan miyau daya makale a makoshinta. Haka sheshshekar kukan Alameen ko daya bai sa zuciyarta ta russuna ba. Ya ce,
“Wallahi Hajiya in kika hanani zan hanu, in kika yanke min hukunci bazan tsallake shi ba komi tsaurinshi. Na rantse da Allah wannan hukuncin da kika yanke a gareni na yin fushi dani ya fi komi tsauri da hatsari agare ni, fiye da rashin soyayyar Intisar!
Ban san me na fada wanda ya bata miki rai ba, ban san laifi na gareki cikin alamarin nan ba. Idan kika ce in barta, daga yau na bar ta har abada! Ko hanyar da ta bi bazan kara bi ba, zan je in lallashi zuciya ta in runguni kaddara, in roki Allah ya cire min kaunarta, in rokeshi gafarar hawayen da kika zubar adalilina. Ni dai fatana ki yafe ni, ki daina fushi da ni, don Allah Hajiya. Ya karasa cikin rishin kuka.�
Ta bude bakinta cikin kakkausar murya tace
“Ameenu! Wane alkawari ka yi mun a dawowar ka daga Miami?�
Ya dago cikin razana da dimaucewa ya ce,
“Eye, naam, wane alkawari ne? Hajiya wallahi na manta.�
Ta yi murmushi ta ce,
“Ka je ka tuna, in ka tuna kazo ka gaya mun sannan ne zaka ji hukuncin da na yanke kan bukatar ka. Ya bude baki zai yi magana ta daga hannu ta daura bisa labbanta ta tace Shhhhhh, bana magana biyu. Na farko dai bazan hana ka aurenta ba akan-kaina, tunda sanda ka je inda take har kuka kulla soyayyar, ina cikin gidan baka yi shawara da ni ba.
Dama kuma daga ku har ubanku ba ku dauke ni a bakin komi ba, baku dauke ni a cikakkar mai hankali ba. Na tabbata ba don ta bijire maka ba sai a yi auren ba da yawu na ba, sai dai a debo yayan shegiya a dire mini, a ce ga jikokina, in yaso ko in mutu, ko in yi rai, ba abinda ya dame ku bane. To a kan me zance ban yarda ba?
rashin yardar tawa baya nufin komi tunda kuwa Bello Makarfi zai aura maka ko na yarda ko ban yarda ba? Saratu zata maye maka gurbina ko na dawo ko ban dawo ba? Ta yi shiru cikin matsanancin takaicin da ba zai fassaru ba, tana zukar numfarfashi da kyar tana fesarwa da kyar. Ya dago idonsa jike da hawaye yace wallahi wallahi Hajiya, bani da wadda ta fiki, bani da wanda zai maye mani gurbinki, bani da kamarki kuma ban taba kwatanta matsayinki da na kowa a zuciyata ba! Ni dai burina ki yafe mini laifinda na yi miki, wanda na sani da wanda ban sani ba. Tunda kuwa ba kya son Intisar daga yau nima zan daina sonta zan daina kaunar ta. Ki yafe mani ki sa mani albarka. Ki taya ni rokon Allah ya sa na fi karfin zuciya ta kuma ya yaye mun kaunarta.
Ita kanta bata san sanda hawaye ya zubo mata ba, tayi saurin dauke su da yan yatsunta tun kamin ya gani. Ta mike tana nufin fita yayinda shi kuma ya bita da kallo, cikin rashin sanin abin yi kuma. Kamin ta kai bakin kofa ta ce,
“Allah ya yafe mana baki daya, ka tashi ka tafi wurin matarka haka zaka tayar mata da hankali. Kuma ka yi kokari ka tuno shin wane alkawari ka yi mun a ranar da ka dawo daga Miami? Bana nufin in tursasaka bisa raayi na, illah in tserar da kai daga tozarta alkawari!�
How much do you like this story?
5/14/22, 09:27 - Ummi Tandama😇: _____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page2ï¸âƒ£
Tafe yake a mota amma hankalin sa baya jikin sa. Kuka yake kashirban kaman karamin yaro. Duk da zuciyar sa tayi sanyi da yafiyar da ya samu daga gareta wannan bai hanashi kukan tashin hankalin da kalamanta suka tsomashi ba. Wane alkawari ne yai mata? Ya kasa tunawa.
Hajiya kin ce in koma ga matata, to ai gara in dawwama a nan kina azabtar dani daga hukunce-hukuncen ki, domin in na koma gareta bani da wani sauran amfani a gareta, me zan yi mata? Me zan ce mata? Rayuwata ta zamo impotent ba zata kara moruwa da ni ba, kowa ma ba zai kara moruwa da ni ba including Inteesar!
Na dauka zaki fahimce ni, na dauka zaki ji kai na ki ji tausayi na, na dauka zakiyi tunanin soyayyar da nake yi mata bata shafi kiyayyar da kike mata ba, na dauka zaki yi min alfarma irin wadda ba ki taba yi mun ba, na dauka zaki ce je ka Aminu ka auri Intisar, Allah yayi maku albarka, ya sa hakan shine mafi alkhairi a gare mu bakidaya., amma kamar ba kya tausayi na, me zan yi miki ki fahimci ni mai gudun bacin ran ki da fushin ki ne? Ban zaci zaki yafe mun ba tunda na yi sanadiyyar zubar hawaye daga idanuwanki.
Bana nufin in tursasa ka bisa raayi na, illa in tserar da kai daga tozarta alkawari ya tuno kalamanta na karshe. A lokacin zuciyarsa ta tariyo masa ranar da ya dawo, da kuma maganganun da sukayi shi da ita a dakin Faisal. “alkawari daya zan iya yi miki hajiya na, ba zan taba son ta irin son da Faisal ke mata ba!�
Amsar da ya bata kenan a wancan lokacin, maganar ta cigaba da amo har cikin kwakwalwarsa, ta bi har cikin jijiyoyi da tsokar jikin sa, ta zagayo ta fito daga bakin sa. Eh nayi maki wannan alkawarin kam, nayi Hajiya na, kina da hujjar hukuntani da alkawari na. na gode. To amma ba kiyi tunanin komi ya faru a bisa rashin sani ne ba? Ban san Intisar ce diyar Anti Amarya ba. Na so ta a Halimar ta, baa Inteesar ba, Ban san san sanda zuciya ta rinjayeni ga son nata ba.
Karar karon motoci sama da goma, tare da wuntsilawar da motar Alameen ta yi ta shiga katantanwa bisa titin, haka murje ta da wata kotuwar DAF mai cike da Hatsi tayi bisa titin da zai shiga da kai garin Minna kafin ya sadaka da Abuja, ya janyo hankalin alummar da ke wajen bakidaya suka ambaci. Inna lillahi wa inna ilaihi raji oun!
Cikin dan lokaci jamian tsaro suka cika wajen tare da motocin ambulance abin dai babu kyawun gani.
*****
UWA, MAHAIFIYA!!!
Tunda ya fita ta kasa sukuni, ta rasa me ke mata dadi, ta rasa inda zata tsoma ran ta ta ji sanyi. Ta kai gwauro ta kai mari a tsakiyar kayataccen falon, can kuma ta isa ga taga tana lekensa, har ya tada mota ya fita daga harabar gidan idanuwan sa basu bar tsiyayar da hawaye ba.
Ta koma cikin kujera ta zauna cikin mutuwa jiki, ji tayi tamkar ta zauna a cikin kaya, ta yi tagumi, zuciyar uwa! Haka kawai taji hawaye na zuba mata sharr-sharr. Ta san duk cikin yayanta babu mai son ta tare da yi mata biyyayyah tamkar Alameen, anya hukuncinda ta yanke a kansa tayi masa adalci?
Gaskiyar Innar ta ne son kanta yayi yawa, kuma wannan ba so bane! Ita uwa kullum hakuri take da abu koda tana so ta barwa danta, ya roke ta, ya kaskantar da kansa gareta irin yadda wani cikin yayanta bai taba yi mata ba.
Ya nuna mata fifiko akan bukatar shi. Ya ce alfarma ce ya ke nema irin wadda bai taba nema daga gareta ba! Ya zubar da hawaye irin wanda bai taba zubarwa a duniya ba, sabida tashin hankalin fushinta a gareshi. Koda sanda yake kankani bata taba ganin shi yayi kuka haka ba.
Ya nemi jin kanta da tausayi amma bata nuna ko daya ba, duk da cewa ba hakan ba ne zahiri a zuciyarta.
Ta nuna masa damuwar shi bata dameta ba, kiyayyar da ke zuciyar ta kadai ta sani, koda hakan zai zama ajalinsa bata amince masa ba, shin ita din wace irin mahaifiya ce?
Ta kai tunaninta ga yarinyarda aka kira da suna Saratu-Intisar. A iya saninta da yarinyar, shekaru goma sha takwas da suka gabata, tun tana jaririya kawo girmanta, bata taba daga ido ta yi mata koda kallon banza ba, bata taba bude dukkan idanun ta tangaras ta dubeta ba, sabida tsananin girman ta da kimar ta da take gani. Bata taba fada mata abu tace da ita ba haka ba. Bata taba yin musu da ita ba balle ta kai ga zaginta, duk kuwa da irin kyara, tsangwama, ukuba da rashin kyautatawar da take mata.
Ta dauki yayanta tamkar yan uwanta na jini, bata kula yayan kowa a duniya sai nata, sune ta mayar abokanta, yayyunta, kawayenta, abin gani ta ji farin-ciki kuma abin alfaharinta. Bata hada kaunar yayan ta da na kowa a zuciyarta. Bata dauki kanta a bakin komi ba face kaskantacciyar baiwa a gareta, duk da yakinin da ta ke da shi na cewa ita din diya ce ga Bello Makarfi.
A duk iya fadin tunaninta, ta kasa tuno ranar da yarinyar ta kuskurota ko da sau daya, ta kasa tuno ranar da yarinyar ta yi mata ba dai-dai ba. Ta kasa tuno ranar da yarinyar ta hantari ko daya cikin yayanta, duk da fada mata da take tayi da babbar murya cewa ta fita harkar yayanta, domin ita din ta tsane ta. Ta kasa tuno inda yarinyar ta taba gayama wani abinda take mata koda da subutar baki ne kuwa, har kuwa mahaifiyar ta, bata jin ta gayawa Saratu irin rikon da tayi mata a bayan ta. Kai iyaka tunanin ta bata taba ganin yarinya mai hakuri da yakanah kamarta ba, shin maye laifinta don Aminu ya so ta?
A kan me bazai so ta ba? Tana da qualities da dama da zaa so ta a kan su, me tayi mata ta tsaneta?
Rashin iyaye? To ai kowa ma zai iya rasa iyayen sa, ko ita a yanzu mhaifinta ya rasu, da uwar ta take zaune, sai a tsaneta?
Shegiya ce? To in shegiyar ce ma ai ba ita tayi wa kanta ba, ba ita ta jawa kanta ba, itama hakan ta budi ido ta tsinci kanta, kuma ko yau ta mutu zata shiga Aljannah kamar sauran halattattun yaya in har ta yi aiki na kwarai. Ko a yanzu ta tabbata da yarinyar zata fadi ta mutu, to bata da kaico a rayuwa!
Uwar rikonta da uban rikon ta kullum cikin shi mata albarka suke, bata wasa da lokacin sallolinta guda biyar duk rintsi, duk gajiya, duk sanyi, duk ciwo sai ta ganta tana sallah da asubahi, sai ta ganta tana sallah akan lokaci har wani mulmule ne baki wuluk bisa goshinta sabida tsabar sujjadah, kullum Kaman ana kara tisa shi ya fito radas.
Bata taba jin ranar da harshen yariyar yayi ashar irin na su Khaleel ba koda da kuskure ne kuwa. Bata taba jin ranar da wani ya budi baki ya furta wani kalami ga yarinyar, wanda ba na yabo da alheri bane.
Zata rantse wannan yarinyar bata san meye iskanci da shaidanci na wannan zamanin ba, da yammata suka sa a gaba, batasan kallace- kallace da karance karancen banza na zamani ba, bata san bata lokacin ta a abinda bazai amfane ta ba, to meye laifin ta? Me ta yi mata?
Ta tsaneta domin Daddy Makarfi na son ta fiye da kowa cikin yayan sa? To amma in tayi tunani duk wani da mai hakuri da biyayyah ya kan samu mafificiyar kauna a zuciyar iyayen shi. Idan Bello Makarfi bai tausasa mata ba, ina zata je ta a tausasa mata? Ina zata je ta ji dadin rayuwar ta? Bata da kowa, sai su sai Allah da ya halicce ta, ya dace tayi wa Makarfi uzuri akan wannan, in haka ne to meye hujjar ta na tsana da tsangwamar wannan baiwar Allah?
Babu! Illa ita din mutum ce mai son
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 29 Chapter of 38