Share this page
zuwa tara dai-dai yana gama k’irgawa Sarkin k’ofar Fada (wanda yake tsaye a bakin k’ofar shigowa ta waje) ya ware murya ya ce “Gyyyaaraa kintsi!!! Gimbiya Zakiyya y’ar sarki jikar sarki yayar sarki, an gaisheki sarauniya.” A take waennan bayi da suke cikin fadar suka sake shan jinin jikinsu suka sake k’amewa k’am! Dai-dai Sojoji guda biyun nan da suke tsaye k’yam suma a bakin k’ofar ta ciki suka kama hannun k’ofar ko wanne ya rik’e handle d’aya a tare suka bud’ata suka wangale mata k’ofar sannan suka saki kafin su durk’usa alamun girmamawa a gareta. Ta tsakiyar bayin nan da suka hau kan layi ta zo ta wuce alkyabbarta na jan k’asa bayi mata (masu lamba d’aya) guda goma a bayanta suna binta sai Hadimai maza guda biyu. Bata ko kalli kowa ba ta je ta nemi guri ta zauna a kan dardumar dake a hannun dama, kan pillow d’aya babba ta yi zama irin na sarauta, yayinda bayinta suka nemi waje suka zauna a k’asa bakin k’ofa suma suka jona layin waennan bayi suka yi irin zaman su. Ta na wucewa sojojin nan suka mik’e suka mayar da k’ofar suka rufe ko gama rufewa ba su yi ba Sarkin k’ofa ya sanar da zuwan y’ar uwarta Gimbiya Sakina, Kamar yadda aka yiwa Gimbiya Zakiyya haka aka yiwa Gimbiya Sakina, yayinda ta k’araso ta zo ta zauna a kan babban pillow na kusa da Gimbiya Zakiyya bayinta kuma suka zauna a wajen zaman bayi. Wani irin kallon-kallo suke aikawa juna wanda kana gani ka san na tsana ne da hassada….. Suna a haka Gimbiya Salaha itama ta shigo da bayinta goma da Hadimai maza biyu, sai dai ita da ta zo ba a kan babban pillow ta zauna ba a kan k’arami ta zauna (d’aya daga cikin waenda suka yiwa na gefen Gimbiya Zakiyya k’awanya.) na Gimbiya Sakina. Bayan ita y’an mata ne manya da k’anana suka yi ta shigowa wajen su shidda! Kuma ko wacce idan ta zo sai an yi mata k’irarin na daban an gaisheta an bud’e mata k’ofa an rufe kuma tare da bayinta guda goma da Hadimai maza biyu take zuwa. Duk cikinsu baya ga Gimbiya Zakiyya da Gimbiya Sakina babu wadda ta zauna a kan babban pillow duk a kan k’ananu suke zama. Sai da suka gama zama tukunna Gimbiya Giwar mata ta shigo wadda hatta su Zakiyya sai da suka rissinar da kai a lokacin da ta zo shigowa! Kuma an fi minti d’aya ana yi mata kirari, sannan kalar kayan barorinta mazan da matan ba kalar na su Gimbiya Zakiyya bane ba, kuma ko da ta zo zama ba a ga lokacin da ta zauna ba dan kareta bayinta suka yi. Bata dad’e da zama ba Gimbiya Mai Babban d’aki ta shigo! Ita ma sai da kowa ya rissinar da kai sannan itama bayinta kalar kayansu daban yake kamar na Giwar Mata kuma itama ba a ga lokacin da ta zauna ba dan sai da suka kare koina ta zauna tukunna suka juya suka je suka zazzauna a wajen zaman su na bayi. Bayan ita sai Gimbiya Shalele wadda itama yadda aka yiwa Mai Babban Daki da Giwar mata hakan aka yi mata dukda kuwa ta kasance y’ar k’arama dan in baka sani ba ma idan ka kalleta za ka d’auka budurwa ce, dududu ba ta fi 25 ba gashi tanada k’aramin jiki sannan bata tab’a haihuwa ba dan sai da Marigayi Sarkin K’asar ya kwanta jinya ma tukunna ya aureta a lokacin tana da shekaru goma ciff a duniya (lokacin da aka haifi Sarki ZainulAbidden). Ba ta dad’e da zama ba busa da sarewa suka karad’e koina! A take fuskokin Gimbiyoyin da suke zazzaune a wajen suka chanza. K’irari aka dinga yi sama da mintinu goma kafin a bud’e mata k’ofa ta shigo cikin takunta na k’asaita tana kallon kowa a kan hanci. Bayi ne mata hud’u a bayanta tsabar mulki ba su bari alkybbarta ta jaa k’asa ba a hannayensu suka rirrik’e mata yayinda Hadimai maza guda takwas suke mara musu baya. Tana zuwa gaba d’aya Gimbiyoyin wajen suka mik’e tsaye tukunna suka russunar da kawunansu alamun girmamawa da gaisuwa ga Gimbiya Mariya (Uwar Marayu) Uwar Sarki. Babu wadda ta kalla a cikinsu sai bayinta ne suka amsa musu da “Uwar Sarki ta amsa muku!” Daga haka ta wuce ta je suka kakkareta ta zauna a kan babban pillow d’in da yake kusa da na Gimbeeya Zakiyya y’arta ta farko a duniya. Gimbeeya Mariya ta kasance mata ta uku ga Marigayin Sarki, bata kai su Giwar mata da mai babban d’aki a shekaru ba dan su d’in sai da suka dad’e da Sarkin sosai tukunna da kyar ya yarda ya k’ara da aurenta. Ba ta kai su a nasaba bama dan ita a cikin gari ta zo sama ta ka rabo ya rantse aka aureta sab’anin mai babban d’aki da ta kasance y’ar Sarkin k’asar da suke makwabtaka da k’asar ta su ta KHAK’IL, haka itama Giwar mata y’ar Sarkin k’asar kusa da su ce…ba dan tsari ba sai dan girmansu ya sanya take basu girma matuk’a a baya sai dai kuma tun daga ranar da ta tsugunna ta haifi d’anta ya kasance Yareema shikenan idanunta suka bushe ta daina ganin girma da darajar kowa ta raina kowa take zuba rashin mutunci ga kowa, Hatta Gimbiya Giwar Mata ba ta ragawa ba! Wadda ko ba dan nasabarta ba a shekaru ma matar ta kusa sa’ar kakarta. Sai bayan ta zauna tukunna kunnuwan jama’ar wajen suka huta da k’arar sarewa da algaita, inda masu kid’in suka tsagaita suka jaa suka tsaya da gangunansu a bayan barori. Matan suna gama zama Mazan fada suka fara shigowa suna zama a kan tasu dardumar da take opposite d’in ta matan (ta hannun hagu) Sab’anin matan su duk cikinsu Galadima ne kawai ya zauna a kan babban pillow ragowar kuwa duk a k’ananu suka zazzauna dan yawancinsu ba jinin sarauta baneba. Sai Wambai da Waziri su kuma a kujerun su na kusa da ta Sarki suka je suka zazzauna. Wambai k’anin marigayi Sarkin k’asar ne yayinda Waziri ya kasance sun had’a Kakanni ne da shi marigayi Sarkin k’asar, gaba d’ayansu shekarunsu sun haura sittin-sittin dan ba Yara bane ba! Kamar yadda Marigayin Sarki yake da y’ay’a mata birjik! Har guda Arba’in (40), talatin da d’aya (31) sun yi aure ga takwas y’an mata d’aya bazawara sai Sarki ne aka samu Namiji d’aya rak! Haka nan shima Waziri yake da y’ay’a mata masu tarin yawa dan shima duk d’a Namijin da aka Haifa masa a ranar yake rasuwa wasu ma b’arinsu ake yi ta hakan ne ake gane Namiji ne a cikin, tun zamanin cutar mak’arta har yau y’ay’a maza basa zama a masarautar. Wambai ne yake da D’a Namiji guda d’aya Nuraddeen da Y’an uwansa mata tara waenda duk sun yi aure sai k’annensa biyu ne suka rage Na’ima da Nafisat. Daff da shigowar Sarki Nuradden ya shigo yana bubbud’awa da Hadimai kusan ashirin a bayansa. Zumbur! Gimbiya Mariya ta yi ta mik’e tsaye wanda hakan ya sanya mutanen wajen kaff d’insu suka sunkuyar da kawunansu k’asa. Ido cikin ido suke kallon juna ita da shi wanda hakan ya sake bak’anta mata rai. Cikin izza ta ce “Wambai a sanarwa Nuradden lokacin shigowarsa Fada bayan ya dawo daga hutun mako biyu na zaman fada da na bashi a yanzu.” Had’e rai sosai Nuradden ya yi yana kallon cikin idanunta tarr yana mamakin matar, kamar ba ita ce jiya-jiya suka gama had’a plan cike da had’in kai ba! Tunanin sa ne ya katse jin ta sake cewa “na d’auke Hadimai goma daga cikin masu take masa baya sakamokon jinkirin fita da ya yi a yanzu da kuma kallon cikin idanuna da ya yi!” Zuwa yanzu kam ya kai wuya dan wannan uwar rainin wayo ma kenan! Ai shi a ganinsa ita da shi yanzu kam sun wuce haka… ya yunk’ura zai yi magana kenan Wambai wanda yake uba a garesa ya ce “umarninki shine abin binmu.” Ya fad’i hakan ya na mai rissinar da kai kafin ya d’ago ya k’urawa Nuradden d’in ido sosai. Fuuuuuu ya juya ya fita, Hadimai goma suka bishi goma kuma suka ci gaba da zama a inda suke suna jira a tashi su bita su ji sabon post d’insu kuma. Iya wuya Waziri ya kai! Tabbas ya kamata su cire zuwan mata zaman Fadar safen nan da suke yi! Dan ya lura matar nan ta maida kowa kashin gindinta! In ya so sai su ji da rashin mutuncinta a cikin masarautar kawai kafin su san maganinta! Tsabar rainin wayo Waziri da Wambai kansu a ce ba su tsira daga tujarar ta ba!? Kalli fa yadda take bayarda umarni take rashin mutunci ga kowa!… Sannan idan fa basu kawo k’arshenta ba tana gab da dak’ile duk wata power tasu dan yanzu haka ma case ake yi akan sai ta cire kujerun su daga kan matattakala sun koma zaman kan pillow suma kamar kowa….. Shiruuu! Fadar ta kasance kowa da abunda yake sak’awa a ransa har zuwa lokacin shigowar Sarki. Dogarai guda goma rik’e da sanduna da takobi..biyar a layi gefensu ma wasu biyar d’in ne suka fara shigowa bayan doguwar sanarwa da kirari, suna shigowa kowa ya tashi ya mik’e tsaye aka sussunkuyar da kai, bayansu wata mata ce tafe wadda a k’alla zata kai kimanin shekaru 48 a duniya (Jakadiya) daga ita sai wasu Irin murd’add’un sojojin masarautar guda hud’u again sun sakoshi a tsakiya biyu daga cikinsu har da wasu zunduma-zunduman bundugu rik’e a hannayensu. Sai bayansu kuma wasu Yara ne y’an mata k’anana masu dai-dai da shekarunsa (Sarkin) sun ci ado na sarauta mak’ura guda biyu tukunna Hadimai kusan su ashirin suna take musu baya sannan daga k’arshe Dogarai guda hud’u suma duk dai suna take masa baya. Kayane na Sarauta masu asalin kyau da tsada a jikinsa, ya sha rawaninsa mai kunnuwa biyu fari k’al da shi da farin glass. Kirari ake zuba masa kamar za su amayo da mak’ogwaronsu yayinda shi kuma yake takunsa sannu a hankali cike da izza da isa. Kasancewar bashi da tsayi sosai hakan ya sanya sai da ya k’arasa har bakin stairs inda duk y’an rakiyar tashi suka jaa suka tsaya ya fara hawa tukunna aka samu damar fara ganinsa. Shekarunsa sun wuce sha hud’u amma basu kai goma sha biyar ba, dukda yanayin yarinta still k’aramin jiki Allah ya wadatasa da shi wanda hakan ya taimaka wajen sake fidda Yarintarsa muraran! Sarki ZainulAbiddeen kenan d’a kuma jika ga Sarki sannan Sarkin k’asar ta KHAK’IL a yanzu! Wanda tun lokacin rasuwar Mahaifinsa lokacin yanada shekaru biyar a duniya ya ke bearing sunan Sarki Wambai kuma yana acting as Sarki, girma da ya riskesa da wuri sakamokon jin dad’i da asalin kwanciyar hankali da Hutu da kuma bala’in Gimbiya Mariya ya sanya aka mik’a masa sarautar tasa kachokam watanni biyu da suka wuce…… BULAMA ✍️ 0806 402 1951 ANA MALIK!! Book 01. Page 11. Humairah Bulama. Mikiya writers Association. Lokacin da ya zo zama wani labule ne ya sauk’o da kansa fari k’al mai tsananin kauri ya rufe kafatarin ilahirin kujerartasa har sai da ya gama zama tukunna labulen ya yaye ya d’age ya koma jikin ceiling d’in mai adon p.o.p ya manne kamar babu shi. Sai da ya zauna tukunna Jakadiya itama ta taka ta je ta zauna a k’asan kujerar tasa dai-dai wajen k’afafuwansa. Dakaru da sojojin da ya zo da su kuma suka juya a yadda suke a kan layi haka suka k’ame a tsaye a layi daga dai-dai inda stairs d’in da ya hau ya fara zuwa inda yawansu ya k’are. Bayi kuma suka je suka zazzauna, y’an matan Yaran nan suka tsaya suka durk’usa suka kwashi gaisuwa tukunna suka je suka zauna a kan manya-manyan pillows na wajen zaman mata. Bayan sun zauna haka nan aka fara tashi one by one ana zuwa ana kwasar gaisuwa, na mata Jakadiya ce ke amsa musu da yawun sarki Yayinda Dogarai suke amsa na zaratan mazan da suke zuwa suna kwasar gaisuwa ga Yaron da har yanzun bai gama rufe shekaru goma sha biyar a duniya ba. Dama kwasar gaisuwar itace main purpose na zaman Fadar safe ga waenda Allah ya zab’a ya bawa damar ganin Sarki dan in ba a nan d’in ba ko ita uwar tasa ba ta isa ganinsa ba! Duk wasu ragowar muhimman abubuwa kuma sai a zaman Fadar rana ake yinsu wadda ita ta banbanta da ta yanzu dan babu mata da wasu daga cikin mazan ma sannan hatta bayin da suke wa Fadar Ado sallamarsu ake yi sai an gama tukunna suke dawowa, iyaka masu Sarauta da masu fad’a a ji ne ke yinta……………. Bayan an gama kai gaishe-gaishe Sarki ya amsa daga nan ya yi musu sallama ya mik’e ya fice shi da tawagarsa daga haka Fada ta fara watsewa, sai da kowa ya fice tukunna Bayin nan suka tashi suka hau shara da goge-goge, sai da suka gama tass tukunna waensu masu kimanin yawansu suka zo suka chanje su, dukda sai nan da kusan awanni biyar tukunna za a yi zaman fadar yamma hakan bai hanasu hawa kan layi su zauna su nutsu kamar yadda aka tarar da bayin safe ba. ************** Kafin awanni biyu labari ya gama zagaye unguwa ‘Ma’a ya yi garkuwa da Dije’ Inna sai da ta suma sau biyu a tsakankanin nan mutane sun rufu a kanta ana ta lafiyarta Yayinda Asabe da Kaka suka dasa kujera a tsakar gida suketa maganguna ala dole su sai kowa ya yarda Dije fa da k’afarta ta bi Ma’a babu wani garkuwa da ya yi da ita. Duk da cewa Ma’a ya yiwa kowa iyaka da Gidansu ta karkashin k’asa sakamokon matan layi da suke kai k’orafe-k’orafen sa wajen Maama, amma hakan bai sa Inna ta ji shakkar shirya zuwa ta sami matar ba dan ta san ita kad’ai ce za ta iya kwato mata y’arta. Babu yadda su Iyya ba su yi da ita ba amma ta ce musu ‘sai fa ta je! Tun kafin ya yi mata illa, a barta kawai ta je.’ A k’aidar Ma’a idan kike je gidansu wajen Maama to ko dai ya illata d’anki ko kuma mijinki ko dai wani naki saboda akasarin masu zuwa idan suka zo suka tafi sai ya ji sabon labari…ita kuwa Maama da ta ga an daina huld’a da ita sam Allah bai sa ta kawo a kanta shi ne ba, ita Mallan ma ta zarga a ranta ta ce maybe ko shine ya ke binsu ko y’ay’ansu shiyasa kawai itama take harkarta ita kad’ai dama kuma kusan duk kunyarsu take ji ma dan ya janyo mata raini a wajen kowa, dan haka itama sai ta jaa jiki k’ark’ari idan abu ya faru na farin ciki ko akasin haka ta shiga ta jajanta ko ta yi murna. Dawowar Minu wanda biyu a cikin samarin gidan nasu suka je takanas suka taho da shi ce ta taimaka Inna ta samu dama aka barta ta tafi gidan Maama dan shi da ragowar samarin d’ari bisa d’ari suka goya mata baya akan ta je d’in dukda kuwa a tsorace suke. Wani d’an k’aramin clinic ya kaita nan kusa da su ba da nisa ba, dukda kuwa babu ko sisi a jikinsa. Sai da ya ga ta shiga hannun Likita har an fara dubata tukunna ya nutsu hankalinsa ya d’an dawo jikinsa. Da farko Likitocin k’in karb’arta suka yi saboda yanayinsu da suka gani dan har Oscar ya fara yi musu hauka Ma’a ya yi saurin dakatar da shi ya ce musu “k’anwarsa ce!” Ba dan sun so ba suka karb’eta dan d’aya a cikinsu ya sansu kuma ya gane su ya san su waye su d’in. Babu yadda ba’a yi da shi a kan ya fita ba amma k’ememe ya tsaya ya ce a yi komai a gabansa kuma ya hanasu cire mata hijabi. Da dabarun su na Likitoci sukayi amfani aka samu aka duddubata suka gano ba komai bane sai shock ya sanyata ta suma sannan jininta ya yi low sosai. Likitan ne ya rubuta abubuwan da ake buk’ata tare da bill d’insu ya mik’awa Ma’a ya ce “ya biya sannan akwai guda d’aya da basu da shi kuma yanzu za a jona mata drip ne dan haka ya yi k’ok’ari ya kawo, ana buk’ata urgent.” Ba shi da ko sisi a jikinsa sai naira 20 gaba da baya dan gaba d’aya tattalin arzik’insa ya k’arar a wajen hidimar fara sana’arsa ta sayar da rake, dan hatta bencin da aka bubbuga musu wajen guda uku sai da suka ci masa kud’i ba na wasa ba. Su Oscar sun so su d’auko ko na uban waye ko su saka a yi musu a kyauta ala dole amma sai ya hanasu saboda tun ba yau ba dama ya yi alk’awarin ba zai tab’a ciyar da Mama da abunda bai dace ba komin k’ank’antarsa yana so komai ya zamo ta hanyar halal. Yanzu kuma ga Dije wadda saboda itan ne ma ya ke so ya fara sana’o’i sosai dan aiki ba ya a cikin lissafinsa, kuma ya san d’awainiyarta dole tana buk’afar kud’i sab’anin da wanda daga shi sai Mama. Lissafin wajen dubu hamsin ake yi yanzu haka ga kuma wani drip na daban wanda zai je ya siyo. Likitan yana gama bashi takardar ya juya ya fita, sai da ya gama k’arewa fuskarta kallo tukunna shima ya juya ya fito wajen su Scorpion, suna ganinsa suka yo kansa suna tambayar sa ‘ya mai jiki!’ Shiruuu ya yi kawai yana lissafi, Oscar ya matso still a buge yake har yanzu ya ce “kawo in je in gigita Rabiu mai chemist ya had’o min kan komai!”. D’agowa ya yi ya k’ura masa ido kamar wanda ya ke so ya hango ta inda zai samo kud’in rubuce a kan fuskarsa, wanda k’ura masa idon da ya yi ya sanya Oscarn ya d’an jaa da baya ya sunkuyar da kansa k’asa. Agogon hannunsa mai tsada wanda ya saitawa timer lokacin fara shirye-shiryen operation d’in da suke da shi yau ne ya yi k’ara! Dan haka ya d’ago shi ya kalla lokaci.. Ya gama ganin lokacin amma bai janye agogon ba idanunsa a kan agogon kyarr!! Har yanzu, sai da ya gama lissafe-lissafensa tukunna ya ce musu “ku saka ido” Daga haka ya juya ya bar cikin reception d’in. Bayan kamar awa d’aya ya dawo…ya siyo d’ayan abun da suka ce basu da shi ragowar kuma yana k’arasowa ya had’a ya bayar da kud’insu tare da kud’in gado da service da kati da komai. Nan da nan aka had’a komai aka jona mata har yanzu ba ta san inda kanta yake ba! Scorpion ne kawai a kaff cikinsu ya lura babu agogon hannunsa wanda ya fita da shi yanzun, murmushi kawai ya yi a ransa ya na mamakin Ogan nasu…… Sama-sama take jin maganarsa kamar waya yake yi… “Eh, mun yi har mun gama aikin yanzu haka baya ma duniyar!” Shiruu ya d’an yi alamun ana yi masa magana ta d’ayan b’angaren ne kafin chaan ya ce “To ko kana buk’atar ganin gawartasa ne a je a d’aukota?” Zuwa yanzu jikin Dije har ya fara karkarwa dan ta fahimci muryar waye gashi ta ji ta a kwance, ba ta kai ga bud’e idanuwanta ba dan haka ba ta fahimci a ina take ba!… Tsaki ta ji ya yi kafin ya ce “arresting d’ina fa ya yi? So kake in zuba masa ido in kyalesa!?” Chaan ta ji ya ce “wannan kuma aikin su Scorpion ne, su kuma b’angaren d’an wanchan mutumin ka barni da su ba ni buk’atar ka yi komai mun riga mun gama magana da Alaji.” Cikin d’an fushi bayan ya gama sauraron wanda suke wayar da shi ta ji ya ce “babban case d’in ya ci uwarsa! Ka san yadda za ka yi wannan ba damuwa ta baceba!” Yama gama fad’in haka ya kashe wayar ya juyo yana huci zuciyarsa tana tafarfasa. A kan hannunta idanunsa suka sauk’a…ta damk’e zanin gadon da take kai da dukkan hannuwanta biyu kamar zata fasa shi ne. A hankali ya k’arasa inda take ya tsaya a kanta ya k’uraa mata ido, motsi ya ga idanun nata sunayi suna karkarwa da gaba d’aya ilahirin jikin nata ma. “Damn it!!” Ya furta a hankali wanda hakan ya sanya ta fahimci yana tsaye a kanta ne kusa da ita! Ba ta san lokacin da ta zabura ta mik’e a razane ba, jikinta yana wani irin karkarwa. BULAMA ✍️ 0806 402 1951 ANA MALIK!! Book 01. Page 12. Humairah Bulama. Mikiya writers Association. Yama gama fad’in haka ya kashe wayar ya juyo yana huci zuciyarsa tana tafarfasa. A kan hannunta idanunsa suka sauk’a…ta damk’e zanin gadon da take kai da dukkan hannuwanta biyu kamar zata fasa shi ne. A hankali ya k’arasa inda take ya tsaya a kanta ya k’uraa mata ido, motsi ya ga idanun nata sunayi suna karkarwa da gaba d’aya ilahirin jikin nata ma. “Damn it!!” Ya furta a hankali wanda hakan ya sanya ta fahimci yana tsaye a kanta ne kusa da ita! Ba ta san lokacin da ta zabura ta mik’e a razane ba, jikinta yana wani irin karkarwa. Sai da ta mik’e ta bud’e idanuwanta tukunna ta fahimci ashe a asibiti ta ke, wawwaigawa ta yi ta ga d’akin daga ita sai shi sannan kamar ma dare ne dan haka ta matsa sosai jikin bango wani mad’aukakin tsoro mai tafe da takaici yana lullub’eta…… K’uraa mata ido ya yi yana kallon yadda ta ke kuka yana jin sauk’ar hawayen nata kamar zubar ruwan zafi a kan k’irjinsa, a hankali ya matsa kusa da ita ya zauna a bakin gadon wanda hakan ya sanya ta sake mak’alewa sosai a jikin bangon ta kawar da kanta gefe ta k’ame sosai dan hatta sautin kukan nata ma ya tsaya dan sosai ta gimtse bakinta, sai uban hawaye da suke ambaliya wani na korar wani. A hankali ya ke kallonta cikin wani irin yanayi, sai da ya gama nazartarta ya gama hango tsorone tsantsa a tattare da ita, bayan ya tuna yadda Likitan ya ce masa ‘shock ne ya sanyata ta suma’, tukunna a hankali ya fesar da wani irin huci wanda ya sanyata ta sake k’ank’ame jikinta ta manne da jikin bangon kamar zata tsaga shi ta shige ciki sakamokon wani irin wari da numfashinsa ya feso mata da shi! Ba wai wari na k’azanta ko warin baki ba! Wani irin wari ne wanda ba ta tab’a jin kwatankwacin irinsa ba amma dai ta fahimci warin kayan shaye-shaye ne sakamokon yadda ta ji kanta ya yi wani irin mahaukacin sarawa a lokacin da ya fesa mata hucin numfashinnasa ita kuma ta shak’a. A hankali cikin wata iriyar calm murya sannan a slow sosai ta ji ya ce “Ba zan tab’a cutar da ke ba Khadijah.” Da sauri ta juyo ta ware kyawawan idanuwanta da suka rine ta zuba masa su wanda hakan da ta yi ya sake assasa mata tsana da matsanancin tsoronsa…kallo d’aya za ka yi masa ka fahimci shi d’in rik’ak’k’en d’an daba ne sannan yanzu da ta had’a idanu ta shi ta sake fahimtar a buge yake mak’ill!! Sai dai kuma wani ikon Allah a lokaci guda maganar ta sa ta soma yunk’urin yin tasiri a kanta saboda yadda take hango zallar gaskiyar abinda ya fad’a d’in a cikin kwayar idanunsa wanda hakan ya bada gudummawa wajen sanyaya mata ilahirin jikinta…… Kamar kuma wadda aka mintsina a take ta yi firgigit! Ta d’auke kanta lokaci guda ta dawo cikin haiyyacinta. Cikin takaici da tsoro ta fara k’ok’arin sauk’a daga kan gadon gaba d’aya, da sauri ya rik’e mata hannu ya ce “relax, ba ki da lafiya fa” Ya yi maganar a dake. Wani irin kallo ta yiwa hannun nasa sannan ta d’ago ta kallesa, wanda hakan ya sanya kawai ya d’auke hannun nasa. “Ina y’an uwa na? Mai yasa na kasance a nan tare da kai?” Ta yi masa cikin takaici tsoro da damuwa. A hankali ya runtse idanuwansa kafin ya bud’esu, sai kuma ya mik’e a hankali ya juya ya fita bayan ya sake ce mata “ki nutsu ba ki da lafiya” Bai dad’e da fita ba lokacin Dije har ta gama shirin fecewa wata nurse ta shigo, juyin duniya amma Dije ta k’i zama a asibitin nan ta ce “ita Gida zata tafi.”….. Dai-dai ta fito su Oscar suka taso dan su ya barwa jiranta amma kallon da ta yi musu ta k’ara sauri ya sanya suka gagara tsaida ita dan sun san basu Isa tsawatar mata ko su rik’eta ba….a baya dai Scorpion

Chapter 10 of 23