Haba mana..ka zo sai ja mana rai kake yi bayan ka san halin da muke a ciki so kake yi zuciyoyinmu su buga kafin ka gaya mana me ke faruwa?”
Wani kalar kallo
Baban Fati ya yi mata wanda hakan ya sanya ta kawar da fuska tana ta faman harare-harare.
Fashewa da kuka Mallan Idi ya yi sannan ya ce “in da ace ina da ikon kwatar Yarinyar nan jiya da na yi wallahi! Abunda ya bani mamaki ya sanya ban shiga abunba shine da k’afafuwanta na ga ta shiga wajensa sai dai shigarta ke da wuya na fara jiyo ife-ifenta to dai har yanzu da nake gaya muku tana chan a wajensa sai abunda Hali ya yi.
Ku yi hak’uri dan Allah ku….”
Bai kai ga idawa ba saukar tab’arya ta dira a goshinsa daga Ramma dan a zuciye ta saka hannunta mai lafiya ta d’auki tab’aryar dake yashe a gefenta ta maka masa duk da kuwa tana fargabar me Ma’ah zai yi mata idan ya ji labari duk da ta ji Mallan Idin ya faiyyace ba sa shiri amma dai uba ai uba ne!
Tayi ta samu daga Maman Kubra dan haka suka shiga jifansa suna rad’a masa
dukkannin abunda suka samu, duk tsare gida da masifar Baban Fati kasa hanasu ya yi, sai da Mallan Idi ya ga suna shirin yi masa illa tukunna ya tashi ya fita da gudu dan kansa.
Cikin b’acin rai Ramma ta ce “da ka tsaya mana, shege mugu! Tun jiya ka ji Yarinya ta na ihun neman taimako amma baka zo ka fad’a ko ka tattaro jama’a an taimaka mata ba sai yanzu da ta kwana a hannunsa!”
Sai kuma ta fashe da wani Irin kuka mai d’aci.
Cikin b’acin rai
Baban Fati ya ce “ai ga Irin kalar rashin hankalin naku da baya barinku ku ci riba a kasuwa, na tabbata inda ace mun lallab’a mutumin da tsaff zai bayar da shaida against shi Ma’a d’in a gaban y’an sanda har ma da kotu.”
“Ko ba ke ce kika ce min y’an sandan sun ce baku da shaidar ya tab’a kashe kowa ba, ta waya??”
Ya yi maganar yana kallon Maman Fati.
Cikin takaici Ramma ta ce “duk da ya kasance ubansa Wallahi ka ji dai na rantse idan ba wata kwakkwarar shaida aka samo ba to a banza! Duk fa munafuka…”
Cikin katseta da b’acin rai ya ce “ai sai ku yi, ku kuka sani!”
Daga haka ya d’aga labule ya shige d’akin Maman Fati.
“Hmmm”
Kawai Maman Fati ta ce a ranta ta shiga aiyyana ‘ ka ce hakan mana tunda ai ba kai ke zaune a cikin bala’in Unguwar ba, da an yi magana ka ce baka da kud’in chanja gida, maza kenan…..’
Mallan Idi kuwa zuciyarsa fes! Haka ya fito daga cikin gidan dan ya san ko ba komai ya fara rama kaso d’aya a cikin d’ari na k’untatawa da Ma’a ya yi masa, tunda ya haifesa ya rasa zuciyar matarsa gaba d’aya soyayyar da take yi masa da kulawa duk suka koma kan d’an daga baya ma sai da suka yi baram-baram shi da ita wanda har gobe bai gama fara gane kanta ba gaba d’aya ta tsaneshi ta tsani sha’aninsa.
BULAMA ✍️
0806 402 1951
ANA MALIK!!
Book 01.
Page 26.
Humairah Bulama.
Mikiya writers Association.
Cikin tangal-tangal Inna ta mik’e tsaye jikinta yana wani irin karkarwa ta nufi k’ofa sawayenta ko takalmi babu.
Cike da son sake damalmala al’amarin Kaka ta fashe da kuka mai mad’aukakin sauti ta na cewa “Ni Khadija na ga abunda ya fi k’arfina! Yanzu Yarinyar nan saboda Allah a ranar da Mijin aurenta ya bar duniya a ranar ta kaiwa wani kanta?! Wacce iriyar masifa ce wannan Allah ya k’addaro mini ita a cikin zuriata.
Wallahi ni dama tun jiya da aka nemeta aka rasa har zan ce a tuntub’esa kawai dai ban yi tunanin zata yi wannan d’anyen aikin a ranar da Kamal ya bar duniya ba sam shiyasa na yi shiru.
Duk tsiya dai ai da sun jira ko arba’in ne an yi”
Dai-dai nan makwafta suka fara shishshigowa dan fitar Mallan Idi da jini a goshi yana gudu ya janyo hankalin y’an layin suka yo cikin gidan.
Ganin jama’a sun fara taruwa ya sanya Kaka ta zage dantse ta shiga fad’ar maganganun da duk wanda ya ji dole sai Dije ta fita daga ransa….
Wani abun mamaki a bakin k’ofar gidan su Ma’ah Inna ta tarar da waensu daga cikin makwabtansu waenda ba ta san ya aka yi har suka ji suka rigata zuwa ba.
Sai dai kuma duk d’insu sun ja sun tsaya sun gagara shiga, alamun jira suke wani ya d’auki wannan alhakin saboda tsoron wanda ke a ciki tare da Dijen.
Tashi d’aya kuma sai
Inna ta ji ba ta son shiga…..tun farko ita ba wai dan ta yarda da maganar Mallan Idi bane ya sanya ta zo ba dan in duk duniya za su taru a kanta to baza ta yarda da cewa ‘Dije ta taka k’afa ta tafi wajen Ma’ah a ranar da Kamal ya bar duniya ba.’ Kawai dai ta na so ta tabbatarwa da kanta cewa k’arya yake yi……to a yanzu kuma da ta k’araso haka nan sai tsoro da firgici suka rufeta wata zuciyar ta shiga aiyyana mata ‘To kuma idan da gaske Dijen tana ciki fa?
Ya zan yi?
Ya zan ji?
Me zai faru?
Me ya faru?
Me mutane za su ce?……..
A hankali ta d’ago idanuwanta ta kalli jama’ar wajen waenda duk suka ziraro mata idanuwa, waensu ta basu tausayi yayinda waensu kuma suke ji kamar su zuba ruwa a k’asa su sha dan murna.
A hankali Ramma ta matso tana shirin ce mata su koma gida idan idon mutane ya kau sai su dawo, kawai Asabe ta taho da jagwalgwalallan hannunta (wanda da farko ya yi kamar ya gyaru ta warke jiya tsakar dare kuwa kawai sai gashi ya fara ruwa sosai) ta ingije su ta saka dukkan hannuwanta biyu ta tura k’ofar da k’arfi ta shiga ta na kuka.
Sama-sama take jin hayaniya da koke-koke, a hankali ta d’an yunk’ura za ta tashi ta ji ta kasa sakamokon nauyin mutum da ta jisa gaba d’aya a jikinta! Kanta ne ya yi wani Irin sarawa gashi dama ta ji ya yi mata nauyi sosai a lokacin da ta yi yunk’urin duba waye a tare da ita.
Motsin da ta yi ya sanya ya gyara kwanciyarsa ya sake sakin mata nauyi har da saka hannu ya sak’ale ta, duk da bacci yake yi amma sam ba ya k’aunar abunda zai raba shi da yanayin da yake a ciki yanzun.
A hankali ta ware idanuwanta waenda suma suka yi mata nauyi sosai ta shiga kallon ceiling d’in d’akin wanda ya ji adon pop mai lights ga wata had’add’iyar chandelier..k’ok’ari take yi ta tuna shin a ina take dan dai tabbas ta san nan ba gidansu bane ba kuma ba Getso bane ba!.
Da wani irin masifaffan mahaukacin k’arfi ta yunk’ura ta tashi wanda hakan da ta yi ya farkar da shi ya tashi tare da ita sai dai har yanzun yana nan kwance a kan jikinta wanda hakan ya sanya ta kasa zama da kyau (tashin da ta yi ya zama kamar irin kishingid’ar nan ta yi). Dai-dai nan Asabe da Kaka suka shigo sai kuma Inna itama ta shigo tare da Ramma. Daga nan y’an layin da suke tafe tare da su aka hau lellek’owa kamar an zo ganin biri a gidan zooo.
Su kansu su Asabe sai da suka shiga shock d’in da ya d’auke maganganu da hayagagar su, saboda ba su yi tunanin za su ga komai intact ya tafi musu yadda suke so irin haka ba.
Su Ramma kuwa kasa motsi suka yi yayinda k’afafuwan Inna suka shiga karkarwa suka fara shirin zubar da ita a wajen.
A b’angaren Dije kuwa k’amewa ta yi k’am! Ta kasa motsi ta gagara cewa komai..ta san cewa a k’asa ta zube ta fad’i ta suma sai dai ba ta san ya aka yi ta dawo kan gadonsa haka d’are-d’are ba gashi kuma a jikinta a kwance wanda hakan ya sanya ita kanta ta gaza yarda da shi da ita dan in za a saka mata wuk’a a wuya ba zata iya rantsewa akan cewa babu abunda ya shiga tsakaninta da shi ba, ga wani irin masifaffen ciwon k’afar da tunda ta dawo cikin haiyyacinta ya yi mata sallama ga ciwon jikin da bata tab’a jin kwatankwacin kamarsa ba.
Kawai tsayawa ta yi ta kafe su da idanuwa yayinda shi kuma
ya tsaya ya na kallon ta ba tare da ya ce komai ko ya yi komai ba.
An kai kusan mintuna biyu a haka kafin ya bar jikinta dan kansa ya mik’e tsaye ya tsaya ya yi mik’a daga shi sai gajeran wando kamar bai san akwai mutane a cikin d’akin ba bayan tun shigowarsu ya san sun shigo! Bai juyo ba amma hatta y’an lek’e ya san abunda suke yi.
Mik’ewar da ya yi ne ya sanya aka rarragu wasu suka kwasa da gudu suka fice daga cikin gidan ma gaba d’aya wanda zuwa yanzu gidan ya zama kamar ana ganin sarki a gidan ne dan k’ofar gidan da soron gidan taff yake da jama’a ba masaka tsinke.
Cike da izza da gadara ya juyo bai ko kallesu ba ya k’arasa ya d’auko t shirt mai bottons ya saka ya b’alle mab’allan ya d’auki wayarsa ya daddana tukunna ya kara a kunnensa bai jima ba aka amsa, murya a dake ya ce “ka zo mu wuce.”
Daga haka ya nufi k’ofa…..
Guje-guje aka fara yi kamar wani dodo ne zai fito kafin ya fito kuwa duk an watse gaba d’aya gidan ya rage saura Kaka Inna Asabe da Ramma sai Maman Kubra da Gwaggo da Matar Mai unguwa wadda zuwanta kenan.
Bai dad’e da fita ba Tiger ya zo ya d’aukesa a machine suka wuce…….
Da kyar Ramma ta k’arasa ta sa hannunta mai lafiya ta fara k’ok’arin kamo ta Maman Kubra ta tayata suka janyota kamar wata wadda ta yi suman zaune Ramma ta mik’ar da ita, wanda azabar da ta ji ta sanya ba ta san lokacin da ta rissina ta rik’e k’afarta ba.
“Ki yi mata a hankali fa kin san sabon jini ce, k’afarki ko?
Asabe ta faiyyace sannan ta tambaya.
Ba su kulata ba su ka yi k’ok’arin mik’ar da ita suka zo suka wuce da ita tana tafe tana d’ingishi tana takawa da kyar. Zaninta ta gaba da ta baya da kuma sama-saman duk kana iya hango stain d’in jini-jinin da ya zuba ta sanadiyyar tsinin wuk’ar da ya chaketa a gefen mararta.
Allah ya taimaka ba su tarar da kowa ba dan ba’a san Ma’a ya bar wajen ba!
Sai da suka kusan shiga gida tukunna aka fara lellek’owa wasu suka firfito da sauri aka biyo bayansu.
Band’aki Ramma ta shiga da ita Gwaggwo ta d’auko k’aton ruwan zafin da ta tara a flask tun d’azu da niyyar yin wanka anjima suka yo toilet d’in.
Ganin suna shirin yi mata wanka ya sanya ta magantu da kyar ta ce musu “um, um”
Tambayar duniya kuma sai ta gagara sake bud’e bakinta ta ce wani abun dan haka Ramma ta yi mata dalla-dalla yadda za ta yi kamar wata mai wankan jego kafin suka rufa mata hijabi a k’ofar suka fito suka barta.
Ruwan kawai ta d’aga ta shek’awa jikinta gaba d’aya ba tare da ta cire ko
Ribbon d’inta ba.
Ta jima a cikin band’akin kafin daga baya ta fito da jik’akk’un kayan tana d’ingishi tana tafiya da kyar.
Group-group ta ga an yi a tsakar gidan nasu kai kana gani ka san munafurci ake yi
amma a haka an fake da jaje aka zo yi.
Tana jin Kaka ta na waya da alamun da Mallan ne……
“To dai a kan gadonsa a ka tsinto ta da kyar!!
Da ma ai ita rayuwa shiyasa ake so ka zama na kirki sannan ka zauna da kowa lafiya.
Matar nan kaff layin nan babu wanda ba ta yin fad’a da shi ita da y’arta sun addabi kowa, sannan wuyarta ta ji maganar shaye-shaye ko cikin shege a gindin wani shikenan ta tusa ka da gori kenan har sai baba ta gani, ranar nan fa cewa Asabe ta yi ‘y’arta ta fi k’arfin k’addarar cikin shege!’
Sai ka ce ubanta ke raba k’addarar.
To dai yau ga d’an daba d’an shaye-shaye ya kwashe duk wata albarkar y’anmatancin da ke a jikinta sai a yi jinya a had’a da gwajin k’anjamau!
Ai shi Allah ba a yi masa gatse.
Shiyasa aka ce maka ka mayar da ita makarantar addini amma ka ce kana koya mata a gida, ai ga irinta nan, bokon ma da ta ke k’aryar ta yi ta iya ai ba iyaka rubutu da karatu baneba har da zamantakewa mutum yake koyo wanda ita sam bata iya ba jahilci ya yi mata k’abe-k’abe, kwata-kwata bata san ilimin zaman duniya ba!
Yanzu ga irinta nan ai bakinta ya janyo muku.”
Ita dai Dije ta ji Kaka ta na magana amma wallahi sam ba ta fahimci kalmar ‘A’ da ta ce a cikin zantukan nata ba.
Diriricewa ta yi ta rasa gane wannene d’akin nasu dan haka ta tsaya tana kallon d’akunan d’aya bayan d’aya kamar mai son k’idaya su.
Yanzun ma Ramma ce ta taso ta zo ta wuce da ita cikin d’akin Inna dan Kaka har ta fara zaginta wai ‘ta b’ace mata daga gani warin Zina take yi, ta shige d’aki kar ta sake fitowa har sai ranar da za ta bar mata gidan d’a! Dan yanzu shigarta cikin al’umma ma haramun ne.
Ita bata tab’a ganin Yarinyar da take iya kallon mutanen k’urr haka a ranar da d’a Namiji ya sanya a matsayin y’a mace ba sai Dije! Haka nan d’azuma tana a kan gadonsa d’are-d’are amma ta yi musu k’urrr kamar sabuwar mayya………..’
A zaune suka tarar da Inna tare da Matar mai unguwa tana yi mata magana da alama nasiha ce, ita Ramma ba ta ma san sun shigo ba dan haka ta k’arasa ta shimfid’a mata darduma da zani dan har yanzu kayan d’akin nasu yana waje an tattara a waje d’aya.
Zaunar da ita ta yi ta fita ta je cikin kayansu ta d’auko
mata kayanta ta bata ta ce ‘ta tashi ta chanja.’
Zuwa yanzu yanayin Dijen ya fara tsoratata dan ko da ta tashi d’in a kan kayan jikinta ta fara k’ok’arin saka waenchan d’in dan haka ta yi saurin rik’o hannunta ta girgiza mata kai dan ta ga kamar ta fi fahimtar wannan yaren yanzu.
K’ok’arin kwance mata zanin ta yi amma ta k’i yarda..sun fi minti d’aya suna fama a haka k’arshe ta fashe mata da kuka dan haka matar mai anguwa ta ce ta barta da kayan jikinta kawai maybe fargaba ba ta gama barinta ba.
Tunda Ramma ta ke a rayuwarta za ta iya cewa ba ta tab’a ganin abunda ya bata tausayi bayan y’ay’anta a lokacin da Mijinta ya rasu sai Inna da Dije a halin yanzu.
Ga Kaka a waje ta k’i yin shiru kusan duk wanda ya shigo sai ta sanar masa da halinda ake ciki dalla-dalla Asabe ta na tayata, ka na gani ka san murna suke yi.
Mallan kuwa ta kirasa ya fi sau biyar daga shigowarsu zuwa yanzu, ta na ji yana ce mata hanya babu kyau amma ta ce ‘ya taho a haka ya tabbata ya zo Kano a yau a yi ta ta k’are’
Girgiza kai kawai Ramma ta yi ta fito jikinta a sanyaye ta bar d’akin dan sosai tausayinsu zai iya sakata yin kuka a rasa mai rarrashin wani tsakanin ta da Inna. Ga Ya Muhammad a gefe a zaune shi ba mai bacci ba shi ba ido biyu ba. Abun tausayi.
Ko da Ramma ta fita ta tarar Kaka ta kira Kawu Isa tana zaiyyane masa bayani wannan karon kam har da Allah shi k’ara take ta cewa dan ta kasa ci gaba da b’oye farin cikinta.
Ita dai Ramma ta wuce ta barta nan tana mamakinta.
Kaka kuwa ji take kamar ta janyo Mallan kawai ta gansa a gabanta yanzun dan ba ta so abun ya yi sanyi ta fi so ya zo ta sake rura wutar a san na yi da Dije ta san har da Halima!
Ta tafi ta bar su haka ya Isa! Dan wallahi tsintacciya ba ta Isa ta gaje mata gidan d’a ba ta yi kad’an!!!!.
Ramma ta na shiga d’akinta ta ji kanta ya sara, sai kuma tunaninta ya bata yanzu fa idan ba ta nema musu mafita ba tsaf wani azzalumin zai iya aikata irin hakan ga Rakiya ko Fiddausi kuma a gagara bi musu hakk’insu, har gara ma Dije in da ace ba Ma’a bane ba ta san Mallan zai tsaya mata, ita fa?
Dan haka gara mata kawai ta tura su chan ta tseratar da su daga wahala da zalinci da masifar Unguwar nan, su je su dawo da k’ima da kud’i da mutuncin su, akan dai ta barsu a nan babu gata babu tudun dafawa.…..
Kawar da tunanin ta yi ta nemi guri ta zauna a kusa da Rakiya wadda take zaune tana cin gari, d’ago idanunta ta yi ta kalleta ta ce “Allah ki tsame hannunki daga lamarin su Dije, tam!” Ta yi kwafa ta ci gaba da cin kwad’on garin kwakinta wanda ya ji farin mai da gishiri zallah, shima kuma a haka Kubra ce ta d’idd’iba mata komai.
Ba ta kula ta ba ta yi shiruuu dai dan babu abunda ya fi shiga kanta sannan zuciyarta take azalzalarta akai a halin yanzu kamar ta ga an gama magana ta tura su Ingila ko Saudiyya.
BULAMA ✍️
0806 402 1951
ANA MALIK!!
Book 01.
Page 27.
Humairah Bulama.
Mikiya writers Association.
***************
Zuwa wannan lokacin rashin lafiyar mai martaba sarki
ZainulAbiddeen ta zagaye masarautar gaba d’aya har ma da wajenta da waensu garuruwan na k’asar ta Khak’il. Sai dai kuma Gimbiya Mariya ta fito ta k’aryata hakan ta inda ta ce “zamewa ya yi kawai ya fad’i ya d’an gurd’e k’afarsa, ba wani abu serious bane ba kuma yanzu haka ma yana a kan treatment dan haka kowa ya kwantar da hankalinsa.”
Alhalin a asalin gaskiya yanzu haka Sarkin abinci ma ta robar hanci ake bashi. Kwararrun Likitoci bakwai ne a kansa waenda sai ka dage ka ci sa’a tukunna ake iya samun appointment da su. Malamai wajen biyar har da wani boka da d’an bori, sannan Oga kwata-kwata shima yana akan nasa binciken dan halin da take ciki bai sanyaa ta mance ta saka a binciko mata su waye masu wannan d’anyen aikin ba.
Kowa ya zuba ido ya ga ko ya ji wani leakage a kan jikin nasa amma ta yi bakam-bakam ba ta bawa kowa dama ba sai y’ar ta Zakiyya da amininta Nuraddeen ne kawai suka san komai amma hatta y’ay’anta na gidan aure ba ta gaya musu ba.
Su Wambai da Galadima suma k’ok’ari take yi ta goge musu hadda, dan takanas ta kirawo su ta ce musu ‘ranar gurd’ewar da ya yi ce ta janyo suka ganshi hakan amma ba komai bane ba, yanzun jinyar k’afarsa kawai yake yi kuma da zarar ya warke zai fito ras in sha Allahu.
Dan haka kar ma su je suna ta yayata fake news d’in da ba shi ba, kuma su sani muddin ta ji wani zance to ta san daga garesu ne dan haka su kuka da kansu.”
Daga haka ta fice ta barsu a wajen suna ta kallon-kallo.
Su dai sun san gaskiya kuma sun fahimci me take son yi tunda ba Yara bane ba dan haka suka rabu da ita kawai suka bishi da addu’a, suka rik’e abun a zuciyoyinsu gashi dama
sun ga ma duk a rikice take kwana biyun hakan ya sanya kawai suka rabu da ita suma suka kama sabgogin gabansu.
Nuraddeen shine a tsaye a kan komai, shi yake ta nemo mata Likitoci da Malamai duk da kuwa ya san aikin gama ya riga ya gama dan daga gani asirin mai tauri ne ba shi da makari.
Gashi hatta Malaman da suke aiki a kansa tuk’uru ba su rik’e Allah shi kad’ai ba ballantana a saka ran dacewa………
Sarakuna na garuruwan k’asar kuwa k’iri-k’iri ta hanasu duba jikin nasa a ranar da suka yo cincirindon zuwa gaida shi, ta ce musu ya sha magani ya kwanta haka nan suka juya kowa ya kama gabansa shi da tawagarsa, bayan sun yi mata ya mai jikin tare da neman alfarmar ta mik’a musu gaisuwa idan ya farka daga barcin…..
Tun jiya da suka zo suka tafi gaba d’aya ta gaza zaune ta gaza tsugunne, yau ma da sassafe gari ko gama haskawa bai yi ba ta tafi wajensa, bayan ta je ta ga yanayin jikin nasa sai hankalinta ya sake tashi!
Kasa ci gaba da zama ta yi tare da shi dan haka ta fito ta dawo
sashenta, ta wuce bedroom d’inta.
Tunda ta dawo kuwa ba ta ko zauna ba, take ta faman kai kawo dan hankalinta ya kai k’ololuwa wajen tashi. Duk dakiyar ta yau kam ta sare dan ba ta san lokacin da ta durk’ushe a wajen ta fashe da wani Irin kuka ba.. Babban tashin hankalinta idan Allah rufa asiri wani abun ya sami Sarkin shine ‘wani ya hau karagar mulkin nan’ Ta san bayin garin sai sun fita freedom muddin aka ce ba d’anta ne a kan mulki ba duba da yadda ta dinga treating d’in jama’a.
Da gudu wata Hadimarta ta shigo ta na cewa “ki gafarceni ya uwar gijiyata dole ce ta shigo da ni….”
Maganarta ce ta mak’ale da ta hango ta dan haka ta k’arasa da gudu sakamokon ganinta a durk’ushe ta na kuka.
Durk’ushewa ta yi itama ta fashe da kuka ta na cewa “Allah ya huci zuciyar mai k’asar KHAK’IL gaba d’ayanta! Idan ke kika koka mu kuma sai dai mu binne kawunanmu kenan dan ba za ta yo mana kyau ba!
Allah ya tashi kafad’un Sarki Allah ya bashi tsawon rai! In sha Allah babu abunda zai same shi….”
Cikin share hawayenta ta kalleta da jajayen idanuwanta ta ce “ce miki na yi gurd’ewar da ya yi ce ta saka ni kuka?”
Da sauri ta shanye kukan nata dama na munafurci ne ta durk’usar da kanta sosai ta na fad’in “Allah ya huci zuciyarki idan maganata ta b’ata miki rai ki gafarceni ya uwargijiyata.”
Nannauyar ajiyar zuciya ta sauk’e ta mik’e tsaya ta kakkab’e jikinta sannan ta ce “idan kin fitar da halinda kika same ni a ciki yanzu, na san kin san zan sani ko?”
Za ta yi magana ta katseta ta hanyar cewa “me ke tafe da ke!”
A d’an zabure ta fara magana “an samu gawarwakin bayi guda ashirin, sha uku mata bakwai maza.
Matan an yanke musu nonuwa tare da horo me tsanani mazan kuma an yanke musu gabansu suma tare da horo mai tsanani kafin a kashe su amma akwai guda d’aya yana motsi, Gimbiya Zakiyya tana a chan tare da su tana jera musu tambayoyi, da alama sune bayin da…”
Sai kuma ta yi shiruu ta had’iye maganarta da mugun sauri dan Gimbiya Mariyar ba ta san sun san asiri aka yiwa Sarkin ba.
“K’arasa maganarki”
Ta fad’i hakan a dake!
Diriricewa ta yi da farko chaan kuma ta ce “….suka yi sata a bangaren Gimbiya Zakiyya”
Tsaki ta yi ta juya ta fita fuuuuuu kamar za ta tashi sama kamar ba Gimbiya ba.
Unfortunately kafin ta k’arasa shima wannan Bawan da ya rage ya cika! Dan haka bak’in ciki da tashin hankali suka had’e mata goma da ashirin, atleast inda ace za a san mai laifi ta hukunta shi to da zata ji d’an sauk’i da dama-dama….
Sallamar kowa suka yi, hatta Dogarai da amintattun Hadimansu a chan nesa da su suka tsatstsaya, kallon bayin suke yi suna sakewa kamar masu son gano asalin gaskiyar wanda ya saka su aika-aikar a kan fuskokinsu…….
Suna nan tsaye kuwa aiken Oga kwatakwata ya iske su!
‘Tabbas guda goma a cikinsu sune bayin da aka haya suka taimakawa d’ayansu ya hura iskar asirin da ya nakasta Sarki a k’asan dardumar gaban kujerarsa yayin share-share da goge-goge a Fada, guda biyar kuma ganin mai hurawar suka yi by mistake, sai ragowar biyar d’in su kuma leakage suka samu.’
Kuka kawai Gimbiya Mariya ta saka tsabar bak’in ciki da tashin hankali a gaban d’an aiken.
Da sauri Gimbiya Zakiyya ta janyota ta rungume ta shiga bubbuga bayanta, kafin ta sallami d’an aiken itama hankalinta chaaaa a tashe. Ita a yadda ta tsara shine idan suka bi diddigi suka gane
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 23