a bakin shi yana soma taunawa
tukunna ya ajiye cokalin
"Kafadu zaka dagamun?"
A kasalance AbdulKadir yace
"Me kake so inyi to? Na riga nazo, komawa zanyi in kiraka ince maka zan taho?"
Kai Yassar ya jinjina, sosai rashin kunyar AbdulKadir ta karu tun shekarar data wuce, wani abu
ya same shi da baisan menene ba, bakomai yake fada mishi ba, amman baya rufe shi har haka,
ko kiranshi yayi a waya da cewar zaije Kaduna ya dubashi sai yace mishi babu lokacin da zai
ganshi, tun yana zuciya yaqi zuwa harya kula AbdulKadir din na boye mishi ne, saiya dinga
share shi baya kiranshi saiya shiga Kaduna tukunna. To har yanzun kuma boye mishi yake,
wannan ba kanin shi bane ba.
Wayarshi da take a hannun shi Yassar ya danna dan yaga ko karfe nawa, hakan yasa
AbdulKadir cewa
"Nasan yarinyar nan..."
Yana dakuna fuska, danna wayar Yassar yayi haskenta ya dauke, da sauri AbdulKadir din yakai
hannu yana fisge wayar Yassar din ya sake dannawa
"Kaban wayata AbdulKadir..."
Sosai yake kallon hoton fuskar wayar Yassar din
"Hawwa ce ko?"
Ya tambaya yana mika ma Yassar din wayar daya karba yana fadin
"Ban sani ba"
Kai AbdulKadir ya jinjina yana ajiye plate din dankalin ya dauki kofin shayin shi daya rike da
hannuwa biyu yana kurba
"Tun yaushe?"
Shiru Yassar yayi ya kyaleshi
"Hamma magana fa nake maka... Tun yaushe? Zaka fara dating baka fadamun ba ashe?"
Kallon shi Yassar din yayi
"Kamar yanda wani abu ya sameka baka fadamun ba kake nufi?"
Numfashi AbdulKadir ya sauke dan bashi da abinda zai fada, wani abu ya same shi da gaske,
amman kuma ya riga ya wuce, fadar bashida amfani tunda ba wani abune zai canza ba idan
yayi hakan.
"Me yasa ba za'a hada dana su Hamma Yazid ba?"
AbdulKadir ya bukata yana son sake akalar zancen. Yassar yagane hakan, bazai takura shi sai
yasan meya same shi ba
"Bamu dade ba, ba mufi wata biyu ba, kar wani abu ya canza a gaba..."
Kallon shi AbdulKadir yayi
"In har kasata a fuskar wayarka kana jinta a ranka Hamma, bana tunanin akwai abinda zai
canza..."
Murmushi Yassar yayi, wata biyu da fadama Hawwa yana sonta, amman ya dan jima yana yin
haka daga nesa-nesa daman, duk sanda zasu zo gidan, kuma suna dan chatting kadan a
WhatsApp. Bayaso abinda ya faru da Yazid akan Waheedah ya faru dashi, shisa bai kwauron
baki ba, kuma da dukkan alamu itama ta jima tana jinshi din, duk da haka bayason yin
gaggawa, duk da zaifi so suyi shagalin bikin nasu tare da Yasir, amman sam Yasir yace mishi
shi bai shirya yin aure dan lokacin ba, da alama zai rigashi.
"Kayi magana kawai ayi bikin nan duk mu huta"
AbdulKadir ya fadi cikin sigar tsokana. Yar dariya Yassar yayi
"Lallai yaron nan, to kaima kayi auren mana"
Girarshi duka biyun AbdulKadir ya daga ma Yassar
"Da wa?"
Ya tambaya yana kurbar shayin daya kware shi dajin amsar Yassar din
"Waheedah..."
Tari yake sosai dan shayin yabi mishi ta hanyar da bai kamata ba, sosai yake kara kurbar
shayin ko zai samu sauki, muryarshi a dishe ta fito daga kasan makoshin shi
"Wanne irin wasa ne wannan?"
Ya bukata yana sa Yassar din hararshi
"Karka rainamun hankali AbdulKadir, shekara nawa kana yawo da hotonta a wallet? Dan banyi
magana ba baya nufin ban kula ba, itama kuma ina kallonta, bata kula kowa, ban tana ganin ta
fita zance da wani ba..."
Kallon Yassar yake da dukkan alamu Hausa yake mishi, amman da wani yare daban yakejin
maganganun Yassar din na dira kunnuwanshi saboda yanda ya kasa fahimtarsu, yanayin fuskar
AbdulKadir din Yassar yake kallo, mamaki na bayyana akan tashi fuskar
"Tsaya... Me kake son ce mun?"
Ya tambaya yana kasa gasgata abinda yake gani a fuskar AbdulKadir din, kai Yassar yake
girgizawa
"AbdulKadir..."
Ya kira yana cigaba da girgiza kai, AbdulKadir din bai magana ba har lokacin, kallon Yassar din
kawai yake kamar qaho ya fito mishi a tsakiyar kai
"AbdulKadir..."
Yassar ya sake kira a karo na babu adadi, yana jinjina abinda yake gani a fuskar kanin nashi,
har ranshi, duk tsayin shekarun nan ya dauka soyayya suke da Waheedah din, yana kuma da
tabbacin bashi kadai bane yake zaton hakan. Wani zafi yaji kirjinshi nayi, ya hana Yazid furta
mata yana sonta saboda a tunanin shi AbdulKadir din nasonta, yana kuma da tabbacin idan shi
baya sonta ita tana son shi, dan yanda take tambayarshi akan AbdulKadir din kawai ya tabbatar
mishi da haka daga nata bangaren.
"Me yasa?"
Yassar ya tambaya, sai lokacin AbdulKadir yace
"Me yasa me?"
Kai Yassar ya jinjina
"Tana sonka AbdulKadir..."
Yassar yai maganar can kasan makoshin shi, tausayin yarinyar na cika zuciyarshi, plate din
dankalin shi AbdulKadir ya dauka yana diba ya cika bakin shi dashi taf yana cigaba da taunawa,
maganar Yassar din na mishi yawo a duk ilahirin jikin shi
'Tana sonka AbdulKadir'
Ko a mafarki mai nisa bai taba hango soyayya da Waheedah ba, ko kadan, soyayya fa, da
Waheedah, tana da muhimmancin dashi kanshi baisan iyakarshi ba a rayuwarshi, amman
soyayya da ita, shine karshen abinda yake hangowa. Sai dai soyayya da kowama a yanzun ba
abu bane da yake tunanin zai faru, bayajin yana da wannan lokacin.
"AbdulKadir..."
Yassar ya kira ganin yanda yake cin abincin
"Karka kware..."
Bai kulashi ba, dankalin kawai yake zubawa a bakin shi yana taunawa. Hakan yasa Yassar
mikewa ya fice daga dakin da tunani kala-kala a ranshi. Tari AbdulKadir ya somayi yana fita,
babu shiri ya dauki shayi yana kora dankalin bakin shi dashi, hadiyewa yayi yana sauke
numfashi. Kafafuwan shi ya ja yana dorasu kan gadon hadi da kwanciya yaja bargo ya rufe jikin
shi. Pillow din daya dora kan shi yaji ya soma isar shi, dan ba haka yake kwanciya da pillow ba,
dagawa yayi yana dora pillow din akan hannun shi tukunna ya dora kan shi a sama, yadanji
dai-daito a kwanciyar.
Yassar yasa kashi abinda bayason yi, idan akwai abu na biyu da bayason bayan raini, tunani
ne, ko kadan bayason ya zauna yana tunani, taya Yassar zaice Waheedah na son shi, ita
Waheedah din bata da bakin da zata fada mishi kome yake faruwa, kanshi ya bala'in daurewa
cikin yanayin da bai taba tsintar kanshi a ciki ba, komai yake ji ya cakude mishi haka kawai. Tun
ran daurin auren Nuriyya rabon dayai tunanin wani aure, yanzun kuwa gabaki daya tunanin ne a
ranshi.
Ta ina zai fara? Wacce yarinya zai fara tunkara? Yaushe ma zai ganta? Duk da yasan indai
yana da rai da lafiya aure abune da ya zame mishi dole, ko dan gujin fadawa halaka, tare da
Waheedah yana da tabbacin ba zata taba raina shi ba. Asalima raini na daya daga cikin abinda
yasan bazai taba shiga tsakanin su ba. Kuma a yanda yakeji bazai iya kallon idanuwan
kowacce yarinya da sunan soyayya ba a yanzun, bashida ma da wannan lokacin, da anyi
posting dinshi zuwa inda zai fara aiki kuma zai kara samun karancin lokacin duk wannan
abubuwan.
Tashi yayi zaune, karo na farko a tsayin lokaci da yaji zuciyarshi na dokawa da abinda yake
shirinyi. Wayarshi ya dauko yana kunna data din, WhatsApp dinshi ya bude, sunan Waheedah
ne farko da saqonninta da suketa shigowa, sosai bugun zuciyarshi yake karuwa, bude sakkonin
yayi:
'Me kaci?'
'Karka kwanta da yunwa Hamma'
'In dafa maka indomie? Ko zaka sha Tea?'
'Shine baka fadamun zaka zo ba ko?'
Dubawa yayi yaga tana online, rubutu ma takeyi, jikinshi yakeji har kyarma yake mishi, a hankali
ya soma rubutu yana tura mata:
'Waheedah...'
Rubutun da take yaga ta tsayar, hakan yasa shi cigaba:
'Waheedah...'
Runtsa idanuwan shi yayi yana sake budesu kan screen din wayar
'Hamma'
Ta amsa, ya karanta sunan nashi da muryarta, bayason yin abinda zai dana sani, sanin ba zata
taba raina shi bane abinda yabashi kwarin gwiwar rubuta
'Kina so na?'
Karanta tambayar tashi yayi, ganin bata fara ko typing ba, ba lallai ma tagane kan tambayar
tashi ba
'Ba so na yan uwa ba Waheedah... So na aure. Kina so na?'
Tana online har lokacin, amman bata ko fara rubutu ba, kuma yaga ta karanta, zuciyarshi yakeji
har cikin makoshin shi saboda dokawar da take mishi.
'Ki amsani, zan kirga daya zuwa goma. Karki amsa sai kina da tabbaci, idan bakida shi karki
amsa, nida ke zamuyi kamar ban tambaya ba, maganar ba zata sake hadamu ba har abada'
Ya fadi yanajin yanda maganganun nashi suka zauna mishi, ita dashi suna da daqiqan da zasu
dauke shi ya kirga daya zuwa goma, amman zai karya idan yace baya tsoron shirunta.
'Daya...'
'Biyu...'
'Uku..."
Rubutu yaga ta soma, hakan yasa shi barin kirgar da yake, can kuma yaga ta daina
'Hudu...'
'Biyar...'
'Shidda...'
Rubutun ta sake cigaba dashi, tana sake dakatawa bayan wani lokaci
"Ki kasheni kawai Waheedah"
AbdulKadir ya furta a fili, yana jin alamar zufa a goshin shi da bayan wuyan shi
'Bakwai...'
Zuwa lokacin hannuwan shi kansu zufa suke fitarwa, shi baima taba tunanin soyayya da ita ba,
yanzun hakan baisan rashin hankalin daya kaishi yin abinda yayi ba, baisani ba, gashi yazo
yanajin bugun zuciyar da bai taba tunanin zai iyaji bama akan jiran amsarta, Yassar bai tabbatar
ba, hasashe yakeyi, bai tabbatar da Waheedah nason shi ba, kilama tana da wanda take so, yai
tunanin yanajin wani tuquqi na tokare mishi makoshi.
'Takwas...'
Ya tura, yana jin yanda zaibar garin Kano da sassafe, yanajin yanda yaima kanshi karya da
tunanin amsarta ko rashin amsarta bazai canza komai ba, da gaske baya tunanin zai iya hada
idanuwa da ita idan bata amsashi ba. Duk da bayajin yana dana sanin tambayarta din, Yassar
yasa shi son sanin ko tana son shi ko bata son shi.
'Tara...'
Ya tura yana gyara zaman shi hadi da fitar da wani irin numfashi mai nauyin gaske, idanuwan
shi ya runtsa a hankali ya bude su kan screen din wayar.
'Ina son ka, ina son ka da aure Hamma AbdulKadir'
Sake karantawa yayi yana sauke numfashin da baisan yana rike dashi ba. Wayar ya ajiye gefe
yana dafe kanshi da hannuwanshi duka biyun, wani irin numfashi yake saukewa mai nauyin
gaske, kafin ya mike yana zira takalman Yassar dake bakin kofa ya fice daga dakin yanayin
hanyar wajen bangaren nasu. Takawa yake zuwa bangaren Abba yanajin shi kamar wanda
yake tafiya a gajimare, jinshi yake kamar yana yawo a wata duniya da batashi ba, kamar yana
gefe yana kallon wani mafarki dashi a ciki.
*
Dakin Abba ya shiga da sallama, ya same shi a tsakiyar falon a zaune, Mama nakan kujera
"AbdulKadir..."
Abba ya fadi da fara'a yanajin dadin ganin dan nashi.
"Abba..."
AbdulKadir yace yana karasawa ya zauna gefen shi.
"Abba zanyi magana dakai"
Murmushi Abba yayi
"Soja manyan kasa, ina saurarenka ai"
Daga kai AbdulKadir yayi yana kallon Mama dake zaune, yana saka Abba kara fadada
murmushin shi, mikewa Mama tayi, batason sake shiga hancin AbdulKadir din kafin ya tona
mata asiri wajen Abba.
"Bari in baku waje kuyi sirrinku"
Cewar Mama tana dora murmushi kan fuskarta, lokacin daga fice daga dakin. Kallon Abba
yakeyi a nutse yace
"Aure zanyi Abba... Kafin in koma nake so a daura"
Da mamaki bayyane a fuskar Abba yake kallon AbdulKadir din, kafin ya numfasa da fadin
"Aure AbdulKadir?"
Kai AbdulKadir ya daga mishi, yana jin maganganun na fitowa daga zuciyarshi
"Eh Abba..."
Wannan karin Abba ne ya jinjina kai, maganar na dirar mishi da wani yanayi, yana kuma son
karbarta da budaddiyar zuciya, idan har AbdulKadir din zai bude baki da maganar aure to yana
kokarin ganin ya gujema fadawa halaka ne, kuma yanzun yana da sana'ar da Abban yake da
tabbacin zata riqe mishi mata, sai dai shi bayason yin abu cikin gaggawa, musamman magana
ta aure.
"Yaushe zaka koma?"
Jim AbdulKadir yayi kafin ya amsa
"Sati biyu in na dade"
Numfashi Abba ya sake saukewa
"Maganar aure a sati biyu AbdulKadir, abune da bazance bazai yiwu ba, amman gaggawa ba
abu bane mai kyau. Aure kuma yana bukatar shiri. Nasan kana da aikin dazai rike maka mata,
amman wajen zama fa? Lefe da sauran hidindimun biki"
Dakuna fuska AbdulKadir yayi shi baiyi wannan tunanin ba kwata-kwata. Yama manta ana wani
abu waishi lefe a maganar aure, ya kuma manta ana neman wajen zama. Magana Abba yaci
gaba dayi
"Ana iya maganar auren, idan kana ganin zaka iya shiryawa nan da watanni shidda sai a hada
dana su Yazid duk ayi..."
Kai AbdulKadir ya jinjina, hakan ya mishi, zai tara kudin da zasu ishe shi yin lefe, wajen zama
zasu iya farawa da barikin sojoji tunda yasan za'a bashi muhalli, amman ko kadan ba dadewa
zai ba, kafin ya tara kudin dazai mallaki nashi ne zasu zauna. Baya son yaranshi su tashi cikin
bariki, badan wani dalili ba, ra'ayin shine kawai hakan. Dariya maidan sauti yaji ta kubce mishi,
yadan girgiza kai. Da gaske ya samu matsala, shine da maganar aure harda tunanin rayuwar
yaranshi da yanda yake son ta kasance.
"Hakan yayi Abba... Zan tara kudin sai in bama Hajja ta siyo abinda ya kamata..."
Murmushi Abba yayi, AbdulKadir din ya kalle shi yana fadin
"Waheedah ce Abba... Waheedah zan aura"
Kallon shi Abba yake da mamaki shimfide akan fuskar shi
"Waheedah? Waheedah ta nan gidan?"
Ya karasa tambayar da alamar rashin yarda a muryarshi da fuskarshi gabaki daya. Akance sai
halayya tazo daya ake zama guri dayama har a qulla alaqa, Abba na ganin karyar zancen a
abinda AbdulKadir yake fada mishi, dan ta kowacce fuska AbdulKadir bai dace da Waheedah
ba, halayyarsu da komai nasu ya banbanta, bai kuma hango ta yanda akai suka fara soyayyar
ba.
"AbdulKadir ka tabbata? Ita Waheedah din ita tace tana sonka?"
Kai AbdulKadir ya dagama Abba, inda batace tana son shi ba, bazai taba zuwa ya furta ma
Abba zancen aurenta ba.
"Allah mai iko... Oh Allah"
Abba yake fadi har lokacin da AbdulKadir din ya mike jinjina maganar yake, dan kai kawai ya
iya daga ma AbdulKadir batare da yaji kome yace ba, harya fice daga dakin. Sosai yake jinjina
al'amarin auren Waheedah da AbdulKadir, shikam zai kira Waheedah ya tabbatar daga wajenta
kafin ya yanke kowanne hukunci, dan jikin shi na mishi wani iri akan auren, sanyin Waheedah
yai yawa, zafin AbdulKadir ko su da suka haifeshi addu'a suke binshi da ita, yana kaunar su
biyun duka, yana jin Waheedah har kasan zuciyarshi, zai komai dan ganin ba'a cutar da
marainiya da sa hannun shi ba...!
*#TeamAbdulKadir*
*#TeamWaheedah*
*#AnaTare*
[7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan
IG: SufyanLubna
Email: Calmlubna@gmail.com
Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43
*ABDDULKADIR*
*LubnaSufyan*
16
Tun da ta kwanta tunanin abinda yaci takeyi, ko kadan zuciyarta taki samun nutsuwa, ita kanta
Amatullah ce ta dafa musu taliya, da bata zuba musu tare ba, tana da tabbacin babu abinda
zata saka a cikinta. Dan ta nemi yunwar data kwaso tun daga makaranta ta rasa, duk da tasan
ba lallai ya amsata ba, bai hanata daukar waya ta bude manhajar sada zumuntarta na
whatsapp ba. Sunan shine a sama dan shine mutum na karshe da tayi magana dashi.
'Me kaci?'
Ta tambaya, tana dorawa da
'In dafa maka indomie? Ko zaka sha Tea?'
Amatullah dake kusa da ita ta gyara kwanciyar ta tana fadin
"Adda Wahee... Ki rage hasken wayarki mana"
Hannu takai tana rage hasken wayar hadi da fadin
"Yi hakuri..."
Bargo kawai Amatullah taja tana rufe jikinta har kai batare da tace komai ba. Hakan ya ba
Waheedah damar mayar da hankalinta gabaki daya kan wayar, dan ba surutun take so ba
daman.
'Shine baka fadamun zaka zo ba ko?'
Ta sake rubutawa tana tura mishi, da tasan zaizo din da ta dafa mishi wani abu, lumshe
idanuwanta tayi tanajin da dare bai farayi ba ita kam ko indomie ce data dafa takai mishi, a
kasan zuciyarta take addu'ar karya zauna da yunwa. Alamar shigowar saqo da taji yasata ware
idanuwanta kan screen din wayar da wani irin bugun zuciyar da bazai misaltu ba
'Waheedah...'
Lumshe idanuwanta tayi data karanta sunan nata da muryarshi, tana bude idanuwan da
murmushi a fuskarta
'Waheedah...'
Taga ya sake rubutowa, saida ta goge hannunta jikin wandon kayan baccin da take sanye dasu
saboda zufar da taji ya mata, tukunna ta iya amsa shi da
'Hamma'
Rubutu taga yayi, babu shiri ta tashi zaune, da ita kadaice a dakin tsaf zata yi dan ihun murna
ko ya yake, yanzun ma gudun tashin Amatullah daga barcine kawai ya hanata yin hakan,
amman kanta har wani lilo yake, kamar tana saman gajimare haka take jinta, kafin ta karanta
saqon shi daya shigo da wani yare daban da ya saka komai yi mata tsaye cik
'Kina so na?'
Karantawa takeyi tana kara maimaitawa cike da son fahimtar kalmamomin da take jin kamar
ba'a yaren da take fahimta yayi su ba, bai bari ta gama fahimtar su ba ya kara mata da
'Ba so na yan uwa ba Waheedah... So na aure. Kina so na?'
Wayar ta ajiye jin kamar ta dauki wani irin dumi da yake barazar qona mata hannuwa, sauka
tayi daga kan gadon, fankar dake cikin dakin takejin ta mata kadan, zafi takeji bana zazzabi ba,
zafi take ji daya girmi ta dora shi akan tsantar girgiza da mamaki. Littafin Amatullah da tayi
assignment tagani a ajiye, da sauri ta dauka tana fifita fuskarta da duk wani waje a jikinta da
zata iya. Zuciyarta kanta ta nutsu wani waje a cikin kirjinta dan taji abinda basu taba mafarkin ji
ba su dukansu. Sakon da taji ya sake shigowa ya sata dauki wayar saidai ta kasa zama sam
'Ki amsani, zan kirga daya zuwa goma. Karki amsa sai kina da tabbaci, idan bakida shi karki
amsa, nida ke zamuyi kamar ban tambaya ba, maganar ba zata sake hadamu ba har abada'
Gefen gadon ta zauna tana mayar da numfashi a hankali, ta runtsa idanuwanta ta budesu kan
saqonnin nashi yafi sau ashirin, so take ta tabbatar ba mafarki takeyi ba. Ba kuma tunaninta
yake hasaso mata abinda zuciyarta take burin ji ba, amman duk sanda zata bude sakon
AbdulKadir din yake sake mata sallama.
'Daya...'
'Biyu...'
'Uku...'
Ta karanta kafin zuciyarta ta fara mata ihu tana sanar da ita yanda take musu wasa da dama
kwara daya tal da suka samu a wajen AbdulKadir din. Tasan shi, kamar yanda ya fada ne, idan
harya gama kirga goman da yace maganar ba zata sake hadasu ba har abada. Sai dai yanzun
ma batasan yanda akai maganar ta hadasun ba, ko a mafarki bata taba tunanin hakan zata faru
da ita ba
'Hamma... Hamma kace wani abu, ka gayamun ba mafarki nake ba, kabani wani tabbacin
banda wannan...'
Ta rubuta, sai ta tsinci kanta da gogewa
'Hudu...'
'Biyar...'
'Shidda...'
Kai take girgiza mishi tana soma rubuta
"Ina sonka, bansan ko tun yaushe nake sonka ba, ina sonka fiye da yanda zan taba fada maka
Hamma AbdulKadir, tare dakai zuciyata ta fara bude idanuwa, kai zuciyata ta fara dokawa...'
Batasan meyasa ta sake gogewa ba, kalamai take nema, amman ta rasa, har lokacin jin komai
take kamar a mafarki, kamar tana tura mishi amsar zata farka
'Bakwai'
Kai ta sake girgiza wannan karin a fili tace
"Ka tsaya Hamma, dan Allah ka tsaya..."
Idanuwanta ta lumshe tana sake budesu kan wayar tata
'Takwas..."
Wani irin yanayi ne ya bayyana kan fuskarta, muryarta a karye tace
"Hamma mana, dan Allah ka tsaya..."
Nutsuwarta take son tattarowa ko da abinda yake faruwa zai kasance mafarki, bataso ta manta
komai, sakkonin nashi ta sake karantawa tana lumshe idanuwanta ta adana su wajen da tasan
ba zasu taba bace mata ba koda ta farka tukunna ta bude idanuwan nata.
'Tara...'
Ta karanta
"Bansan yazan ci gaba da rayuwa bayan abin nan ba Hamma, idan mafarkine ka tabani ta
fannin da banajin zan koma dai-dai wannan karin... Ka fifitamun wutar burina ka dawomun da
komai baya..."
Ta karasa maganar da wani irin sanyin murya, sosai take jin in har mafarki take a gefen
soyayyarshi da take wahalar da ita, burin samun shi zai zauna, zata dinga kallon shi tana jiran
ya sama mata wajen zama a rayuwarshi ko da bata samu a zuciyarshi ba.
'Ina son ka, ina son ka da aure Hamma AbdulKadir'
Ta tura mishi tana jiran taji ta farka daga baccin da take, alama tagani na cewar ya karanta
sakon, kafin taga ya sauka daga kan WhatsApp din, wani irin numfashi da batasan tana rike
dashi ba ta saki, itama kashe data din tayi ta ajiye wayar hadi da mikewa. Bandaki ta shiga ta
tara ruwa tana wanke fuskarta, har lokacin numfashi take mayarwa kamar wadda tayi gudu.
Zuwa yanzun bata da kalaman da zata fassara abinda takeji. Takai mintina goma tsaye a
bandakin ta dafe sink, amman idan ka tambayeta ba zatace ga asalin abinda take ji ko take
tunani ba.
Alwala ta daura ta fito daga bandakin, doguwar hijab din da take sallah da ita ta dauko ta saka
jikinta. Dardumar da tayi sallar isha'i tana shimfide bata nade ba, kai tahau ta fara jero salloli
tana rokon tabbatar alkhairi a koma menene yake shirin faruwa tsakaninta da AbdulKadir din,
dan tun daga yanda take son shi tasan abin yafi karfinta, yanzun ma ba zata iya ba, ba kuma
zata bata darenta tana tunanin abinda baya karkashin ikonta ba, gara ta bude ma Allah
zuciyarta, sosai kuma ta samu nutsuwar da take jin ta kwace mata, akan dardumar bacci mai
nutsuwa ya dauketa.
*
Tana da darasin safe, gashi ta tashi da wani irin sanyin jiki, har iskar da take shaqa daban take
jinta yau din, bata sake shiga wani yanayi ba saida taci karo da sakon Abba
'Aslm. Waheedah ki sameni kafin ki wuce makaranta'
Haka kawai taji zuciyarta na mata rawa, duk da ba yau bane ranar farko da Abban yakan mata
irin sakon ko idan zasuyi magana ko kuma zai bata wani abin. Yau dinne dai takejin kiran kamar
zai zamana daban. Sanda tagama shiryawa saida ta biya dakin Mami tai mata sallama tukunna
ta fita zuwa bangaren Abba. A bakin kofa ta tsaya ta kwankwasa, saida taji yai magana tukunna
ta tura dakin da sallama tana shiga. Waje ta samu kan kafet din ta zauna dan shima anan yake
zaune ya miqe kafafuwan shi.
"Ina kwana Abba..."
Ta gaishe dashi cikin sanyin muryarta
"Waheedah..."
Ya kira yana dorawa da
"Kin tashi lafiya? Ya makarantar?"
Hijab dinta da taji ta danne ta dan daga tana gyara zamanta sosai
"Alhamdulillah..."
Wani numfashi Abba yaja yana kallon yanda take komai nata cikin sanyi. Da tunaninta ya
kwana a ranshi, har zuwa safiyar ranar yana jinjina ma kaddarar data hadata da AbdulKadir,
dan ko a tunaninshi ya kasa dai-daita dacewarsu. Idan zabi za'a bashi na ya aurar da ita cikin
yaranshi, yanajin Yazid kadai zai iya aura ma ita hankalin shi a kwance, yana da tabbaci akan
Yazid zai riketa da amana, dan bazaice ga rana daya da yaji anyi wata hayaniya dashi ba tun
yarintar shi. Muryarshi dauke da nauyin da yake jin dukkan jikin shi yai mishi ya soma magana
"AbdulKadir ya sameni jiya. Nasan halin shi, nasan bazai sameni batare da amincewarki ba,
amman ina so in tabbatar daga bakinki Waheedah, amana ceke a wajena kamar yanda suma
suke amana, banma kowa maganar ba tukunna, ki fadamun idan kin amince da auren shi..."
Kanta a kasa yake tunda ya fara magana, bata taba tsintar kanta cikin kunya irin wadda takeji
ba, wasu zasuce kamar kasa ta tsage su shige, a irin kunyar da take ciki ba tajin zata iya jiran
kasar ta tsage, ita take so ta narke ta sulale tabi kasar ta shige cikinta. Ga zuciyarta da take
wata irin dokawa kamar zata fito daga kirjinta
"Kimun magana Waheedah, karkiji nauyina, idan har baki amince dashi ba yazo ya sameni ki
fadamun, wallahi indai ina numfashi babu wanda zai miki dole akan komai na rayuwa..."
Shirun ta sakeyi tana kara sadda kanta kasa, numfashi Abba ya sauke
"Aure ba abu bane da akanyi dan kowa nayi, ba kuma abu bane da ake fatan idan anyi a fito,
aure abune da ake fatan idan har anyi ya zamana har muddin rai, shisa ba'a son gaggawa a
cikin duk wani abu daya shafe shi, ba'a kuma son tursasawa, da fahimtar juna ma dole sai an
hada da hakuri a zamantakewar da za'a tashi a kwana karkashin inuwa daya. Kimun magana
Waheedah, bazan samu nutsuwa akan maganar nan ba..."
Kanta da takejin yaima siririn wuyanta nauyi naban mamaki yau ta samu ta motsa tana dagashi
a hankali, da ace nutsuwar Abba bata kanta da bazai ga daga kan ba
"Kin amince da auren shi?"
Abba ya tambaya yana son tabbatar wa, kan ta sake daga mishi a hankali. Wani numfashin ya
sauke, yana jinjina ma karfin kaddara da take zuwa karkashin ikon Allah. Kai ya jinjina
"To Alhamdulillah, Allah ya tabbatar mana da alkhairi..."
Kafafuwanta Waheedah ta tattara, har lokacin ta kasa dago fuskarta, jikinta gabaki daya ya
dauki dumi da kunyar Abba da takeji, mikewa tayi dakyar tana juyawa cikin sauri da nufin barin
dakin
"Kizo ki karbi kudin makaranta..."
Abba ya fadi yana saka hannu a aljihun shi, amman kamar maganarshi ta kara tunzurata, da
gudu ta fice daga dakin tana ja mishi kofar. Murmushi Abba yake
"Oh Allah mai iko..."
Ya fadi, ya jima wani abu bai bashi mamaki ba irin na daren jiya zuwa safiyar yau. Da gaske
AbdulKadir da Waheedah sukeyi, yanda yake jinshi zai kwana biyu yana jinjina al'amarin.
Wayarshi ya dauka ya kira Mami dan ya sanar da ita kafin ya samu dangin Baban Waheedah
din da maganar, duk da sun jima da nuna mishi yana da damar yanke hukunci akan rayuwar
Waheedah din bazai hanashi nuna musu godiya da halaccin da sukai mishi ba, zai samesu da
maganar duk da yasan ba zasuki kowa yake son hadata dashi ba, balle kuma idan sunji jinin shi
ne.
*
"Ina zaki je?"
Muryarshi ta sauka cikin kunnuwanta, tana sakata gyara zaman jakar dake kafadarta tukunna ta
juya tana sauke idanuwanta akan shi. Jikin shi sanye da riga fara kal, sai wandon sojoji gajere
da silipas din wanka a Kafafuwan shi.
"Hamma..."
Ta kira da wani yanayi a muryarta, wani irin son shi taji ya taso mata har yana ma numfashinta
barazana. Tasan ya kamata ta sauke idanuwanta daga kanshi, ta daina kallon shi, amman
zuciyarta ce da iko kan idanuwanta wannan karin, ta kuma nuna mata bata gaji da kallon shi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 37