Share this page
hidima. Duk da matsala dayace take fama da ita yanzun, itace rashin haihuwa, banda wannan rayuwa take data sa tagane farin ciki bako yaushe yake zuwa da kudi ba, farin ciki kanzo idan ka samu wadatar zuciya da iya inda Allah ya zaunar dakai. Tayi nasarar ganin Anas sau daya tun bayan rabuwar su, ta kuma roki daya yafe mata, duk da har yanzun takanyi juyi da amsar daya bata 'Na jima da yafe miki Nuriyya saboda bana son wani abu ya sake hadani dake, ciki kuwa harda tsayuwa gaban Ubangiji a filin tashin kiyama, wallahi na jima da yafe miki karki damu' Sosai takanyi tunani akan kalar rayuwar da tayi a baya, da mutane biyun da suka nuna mata kauna fiye da kowa a rayuwarta da yanda tayi amfani da wannan kaunar ta cutar dasu "Nuriyya" Waheedah ta fadi tana katse mata tunanin da takeyi "Ki yafemun dan Allah, na cutar dake da yawa, wanda kika sani da wanda baki sani ba, ki yafemun Waheedah..." Numfashi Waheedah ta sauke "Babu komai, Allah ya yafe mana" Wannan karin ajiyar zuciya Nuriyya ta sauke tana dorawa da "Ki rokar mun AbdulKadir da ya yafemun shima" Kai Waheedah ta daga mata tana hango motar AbdulKadir din "Sai anjima..." Tace ma Nuriyyar tana kama hannun Ikram din "Ina Fajr?" Nuriyya ta tsinci kanta da tambaya tana saka Waheedah juyowa ta kalleta cikin idanuwanta "Na yafe miki Nuriyya, tun kafin ki tambaya, amman hakan baya nufin ina son sake kasancewa dake a rayuwata, babu wani abu da zai sake hadani kawance dake" Kai Nuriyya ta jinjina ma Waheedah din, bata koji zafin maganganunta ba, ko itace a matsayinta abinda zatayi kenan. "Nagode..." Nuriyya ta fadi da wani irin yanayi a fuskarta "Ina miki fatan alkhairi a duk inda rayuwa zata kaiki" Waheedah ta fadi tana jan Ikram suka tsallaka inda AbdulKadir yayi parking din motar, Nuriyya kuma ta shiga gida. Bayan motar ta budema Ikram ta sakata a ciki, tukunna ta bude gaban ta shiga "Kinsan sarai gobe zan tafi, shine zaki zo ki barni ni kadai" Murmushi kawai tayi "Nuriyya nagani yanzun ta shiga gida, tace ince ka yafe mata" Shiru AbdulKadir din yayi badan baiji me tace ba, sai dan a shekaru uku yaune rana ta farko da maganar Nuriyya ta gifta a tsakanin su. Motar shi ya tayar yana wucewa dasu gida, bashida abin cewa yanzun ma, shisa ya zabi yin shiru, wanda duk zaiji labarin shi da Nuriyya zai san kaddarar zaman aure ce kawai ta gifta a tsakanin su, yanzun ta zama bayan shi, bayan da baya dubawa idan harya wuce, ya gama yafe mata duk wani kuskure da tayi mishi a dan gajeran zaman da sukayi. Shima fatan shi idan ya kuskure mata ya zamana ta yafe mishi. Dan da Abbba ya kira shi yai sake mishi nasiha kan abinda ya faru din daya kira mishi ko da gaba zai tunanin kara aure saida hanjin cikin shi ya murda, yana addu'ar Allah yasa kaddarar shi ta zama da mata biyu ta kare daga kan Nuriyya, Waheedah ta ishe shi rayuwar duniya yana kuma fatan ta zama matar farko da zai nema idan ya tsallake duk wani mataki yayi nasarar shiga aljanna. Suna karasawa gida an kawo wuta, Ikram nata tsalle ganin tv a kunne da tashar cartoon network da suka saka shun the sheep. Nan falon suka barta suna shigewa dakin su. Waheedah na cire hijabin dake jikinta, AbdulKadir ya taka ya hade space din dake tsakanin su, sai nishi take kamar tayi wani aikin karfin. Hannun shi daya ya dora kan cikinta kamar abinda yake ciki hakan yake jira yayi motsin da taji har bayanta ya amsa tana runtsa idanuwanta ta bude su akan AbdulKadir da yake mata dariya "Ke kam kamar ba matar soja ba" Harar shi tayi "Da zan iya dana cire cikin nan ka dauke shi kona kwana biyune" Tsinin cikin bazai barshi ya rungumeta yanda yake so ba, hakan yasaka shi sakin hannunta ya zagaya yana rungumeta ta baya hadi da rada mata maganganun da sirrine a tsakanin su, hannu tasa tana dan ture shi hadi dayin dariya kafin ta dora hannunta saman nashi da ya ke kan cikinta tana lumshe idanuwan shi. ABDULKADIR din ta, sojan ta, Sadaukin ta. Bata same shi da sauki ba, kaddarar zaman su bata kawosu inda suke da sauki ba, bata da wani tabbaci akan yanda rayuwa zata kare musu, amman tana da yakinin indai suna tare da juna koya rayuwa zata hankade su koda sun fadi dayansu zai daga daya...! DUKKAN GODIYA TA TABBATA GA ALLAH. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 37 of 37