je ya kama hannun Hassan da Hussaini suka wuce nasa side ɗin, dan tun bayan da na yaye yaran a side ɗinsa suke.
Ba yadda Abba bai yi ba naki faɗa mashi abun dake damuna, dole ya hakura ya yi shirin kwanciya, muka kwanta nai kamar na yi barci har zuwa lokacin da yai barci. Yana yin barci na miƙe na jawo wayansa, da yake nasan password ɗinsa, bamu ɓoyewa juna komai, harta account balace ɗinsa na bank duk nasan komai.
Kai tsaye na buɗe wayan na shiga Whatsapp dan duba maganarsa da Zainab tun da mamansa ta ce kullum in bai yi mata magana ba bata yafe ba. Ina shiga kan number Zainab na chat ɗinsu naga abin da ya yi matukar girgizani, hannuna har rawa yake wajen scrolling chat ɗin na yi sama, nan naga zafafafan................
labarin A'isha zai dinga zuwa maku dama wasu labaran masu gajeran zango dan faɗakarwa da ilmantarwa cikin hikima da basira................ Danne like and share fisabilillahi.
LABARIN AISHA.🥹💔
PART 3
hannuna har rawa yake wajen scrolling chat ɗin na yi sama, nan naga zafafafan kalaman soyayyar da Zainab take turo mashi, da safe misalin ƙarfe 6 tana turo mashi na barka da safiya, da rana around 12 tana turo mashi na barka da rana tare da tambayar ya kasuwa, da yamma karfe 6 tana turo mashi, sai kuma da daddare karfe 9 tana turo masu zafafa masu kwantar da hankali wai yai barci cikin salama sai kace an ce mata dan ubanta da a cikin azaba yake barci, babu abin da ya fi bani takaici kamar yadda a kasan addu'oi da kalaman soyayyan take rubuta ina son ka yi barci cikin salama da natsuwa wanda baka taɓa samun irinsa ba, wannan abin ya fi komai kona mun rai, a raina na ce dan ubanki da cikin azaba ko cikin jahannama yake barci ba salama ba?, sannan ba iya kalaman soyayya bane kawai take tura mashi, harda kalamai masu motsa sha'awa dan bata da kunya, ko ni da nike matarsa bana mashi wasu kalaman wlh.
(Kai Aisha zata kasheni da dariya, wai dan ubanta da cikin azaba yake barci ne, kai wlh matan da ake neman aurensu a wajen nan gani fa suke kamar na gida bata iya kula da miji ba shiyasa ya je neman aurensu, suna ganin kamar zasu fi kowa iya kula da shi, sun ɗauka auren wasan yara ne ko kalaman soyayyar da suke yi a wajen ne auren, sai sun shigo zasu gane wannan hakuri da ake cewa aure ɗan hakuri ne, sai sun shigo zasu gane Annabi Isa ba ɗan ALLAH bane Manzon ALLAH ne, amma dai mu bi Aisha ta cigaba da bamu labari, zamu ga shin da gaske uwayen gida basu iya kula da mazansu bane yake sanyawa a karo masu kishiya ko kuwa dai jarabace irin na mazan kawai!.)
Na duba yanayin reply da yake yi wa Zainab, iyakarsa uhm ko okey, Zainab zata mashi dogon voice note mintuna 5 zuwa 7, amma sai naga wlh bai buɗe voice ɗin ya ji ba sai ya rubuta mata okey a ƙasa, bai fa san me ta ce a voice ɗin ba, amma yake saka okey. Tsabar ƙoƙari irin nawa na zauna na dinga buɗe voices ɗin, na sanya earpiece na dinga jin voice ɗinta. Wani waje in ji tamkar in shaƙeta saboda takaici, na yi godiya ga ALLAH da yasa Abbie bai saurari voice ɗin ba ni na buɗesu.
Ta wani make murya, wani waje har da kukan makirci dan ta ja hankalinsa, wani voice da ta yi na tsawon mintuna 7 gabaɗaya halin kishiyar mamarta take faɗa mashi, wai tin da babansu ya rasu yanzu kishiyar mamansu bata bata abinci ishasshe, wai yanzu kaɗan-kaɗan za'a dinga cin abinci kar ya rinƙa karewa da wuri, a voice ɗin ta dinga rusa mashi kuka da nuna alamar tana cikin tashin hankali, a karshe ta ce kullum tana addu'a aurensu ya zo da wuri ya ɗauketa daga gidan nan dan tasan shi mai tausayi ne zai tausaya mata ya kula da ita.
A raina na ce shegiya makira, da can ba tare da kishiyar mamar taki kuke zaune ba, a lokacin duk baki san tana gana maki azaba ba sai yanzu kenan, kuma abin da ya kara bani takaici Zainab ta fini shekaru, dan a lokacin ina da shekaru 20 a duniya, na yi aure ina da shekaru 15, na haihu na fari ina da shekaru 16, na sake samun cikin na biyu ina da shekaru 18, Hassan da Hussaini suna da shekaru 2 kenan, na haifi Muhammad ina da shekaru 19, yanzu Muhammad ya kusa shekara ɗaya, kunga ina da shekaru 20, ita kuma Zainab ta girmi Abba kanin Abbie ma a shekaru, dan Abba yana da 25 years yanzu, ita kuma tana da 27, to shi ne abin da ya fi bani takaici, kallon yarinya karama take mun, dan a cikin chat ɗinsu na ga in da take ce mashi ai Aisha kanwata ce, da auren kauye nema da na haifeta, wannan abu ya bakanta mun rai matuƙa.
Amma danaga irin reply da yake mata, na gane he didn't pay attention to her, na samu peace of mind sosai, na goge duka voice da ta mashi waɗan da dama bai jisu ba, sannan na mayar mashi da wayansa na yi kwanciya.
Washegari da safe muka sake tashi da wani tashin hankalin kuma, Abba ya yi wa su Hassan wanka ya kaisu school ya biya kasuwa yai mana cefenen provision yana dawowa kawai sister ɗinsu ta kirasa wai gata ta shigo Kano ya zo ya ɗauketa. Muna zaune a kan gado ni da yayansa ina tuhumansa a kan me yake magana da yarinyar, ina faɗa mashi na ji duk abin da yake faruwa, meyasa bai faɗa mun ba ya bari na ji a gari, muna tsaka da wannan magana sai ga kiran Abba.
Abbie ya ɗauka Abba ya faɗa mashi ai Aunty Babba ta ce ta shigo Kano ya zo ya ɗauketa yanzu, Abbie ya ji takaici sosai, amma ya ce babu komai ya ɗaukota ɗin, bai nunawa Abba kamar akwai damuwa ba, amma hakika ya shiga damuwa saboda yasan ba alkhairi ne zai kawota ba, ashe basu yi rabuwar daɗi da ita ba lokacin da muka je Kano.
Abbie ya kalleni ya ce. "Saboda nasan ba auren Zainab zan yi ba shiyasa ban faɗa maki ba, amma ba wani abin bane"..... Na ce. "Na ji kamar Aunty Farida ce aka ce ta zo ko?"........ Abbie ya jinjina kai game da cewa. "Ita ce, ni zan fita kasuwa, ki mun addu'a, ki mance da wannan zance, ki ciresa a ranki, ni Zainab bata mun ba, bana sonta, idan buƙatar karin auren takamani da kaina zan nemo mai hankali da zata girmamaki ba sai an nemomin ba".
Na ɗan ji sanyi a raina, amma ba sosai ba, ya tashi ya yi wanka ya shirya fita kasuwa, a gurguje ya yi komai dan baya son haɗuwa da Aunty Farida. Kafin Abba ya daukota Abbie ya fice daga gidan. Na tashi nai wanka nima, ko breakfast dama ban girka ba, su Hassan ma ragowar abincin jiya uncle ɗin nasu yai masu warming ɗinsa suka ci ya ɗauka masu snacks da drink ya sanya masu a lunch box suka tafi da sunan mammynsu bata da lafiya kada a tasheni shiyasa yai masu hakan.
Ina ƙoƙarin shiryawa na fito daga wanka kenan na ji shigowarsu parlo, gabana ne yai wani mummunar faɗuwa. A hanzarce na shirya na fito. Ina fitowa sai da na ji kaina ya wani buga da karfi saboda ganinta da na yi da babban ɗanta da mai binsa. Dama wannan babban ɗan nata a farkon aurenmu da Abbie mun zauna da shi, ya zauna wa Abbie a shago kafin ya yi wa Abbie sata Abbie ya koresa, zaman shekara ɗaya muka yi da shi a baya, na rike yaron nan tamkar kanina, ina bashi duk abin da yake so amma shi bai rikeni haka ba, da Abbie ya koresa ne sai ya ɗauko kaninsa Abba ya ajiye a ɗayan shagonsa ɗin kafin ya haɗu da jarabawa ya rufe shagon Abba kuma na mayar da shi makaranta saboda jininmu ya haɗu, yanzu yana 4 hundred level, computer engineering yake karanta.
Na ji faɗuwar gaba ganinta da yaran nata, dukkansu manyan samari ne, babban ya kai 26 years dan ya girmi Abba, mai bi mashi 21 years yake da shi, shi ne mate ɗina ko in ce ya fini da kaɗan.
Na ce mata. "Sannu da zuwa Aunty Farida". Tana mun wani gani-gani, bata amsa ba sai da ta zauna a kan kujera tana wani shan kamshi, sannan ta amsa game da cewa. "Ina Sulaiman ɗin yake? Ya fito ga yaran nan na dawo mashi da su, dan ba zai yiwu yana da ƴan uwa ya bar bare suna shiga cikin arzikinsa ba"........ Na gane dani take yi, tana tunanin shagon abayars da nike da shi na Abbie ne, and ƙanina mai bi mun na saka a shagon da sauran ma'aikata, ƙanina Manager ne, yana zuwa school tare da Abba, idan ya dawo zai je shago ya duba me ya shigo me ya fita, sho kuma Abba burin kwallon kafa yasa a gaba sai ya tafi buga ball, to shi ne wai ta kawo yaranta su suka cancanci su rike wannan shago ba wasu bare ba tun da shagon ɗan uwansu ne a tunaninsu.
Na yi kamar ban jita ba, na wuce kitchen na ɗauko masu ruwa, ina ajiyewa ta ce. "Abinci zaki kawo mun ba ruwa ba, saboda kwanaki na zo yi ba wai na zo yau zan koma yau ba ne".......... Na ɗago na kalleta kafin in ce. "Aunty Farida ban taɓa tunanin jin irin waɗan nan kalamai daga gareki ba, a tunanina ko su Amina zasu canza mun ke ba zaki canza mun ba tun da ke babba ce a kansu, kuma kin yi aure kin san me auren yake nufi, ban san laifin da nai maku ba, and baki taɓa zuwa gidan nan in ce maki tashi ki koma ba, hasalima ni nike gayyatarku da ku zo mu yi hutu tare, meyasa kike jefana da kalaman dake nuna bana son ku raɓi ɗan uwanku?".
Ta kawo salati ta zabga, cike da faɗa ta ce na faɗa mata maganar banza, wai na zageta, kenan ita bata da hankali, tana matsayin yayar mijina zan zageta. Babban ɗanta ya miƙe yana wani bubbuɗewa wai a kan mahaifiyarsa babu abin da ba zai iya ba, babu wanda ba zai daka ba, ba'a haifi wacce zata zagi mahaifiyarsa ya kyaleta ba, yai kaina kamar zai kai mu duka, ga shi da kirar bujumaye. Da sauri na ja da baya ina kallonsa da mamaki.
Abba ya ce. "Khalifa kana da hankali kuwa? Giya ka sha ne kafin ku zo da kake ƙoƙarin kai mata duka?". Ya faɗa yana miƙewa tsaye. Da sauri na juya na shiga kitchen na bar masu wajen, ina jiyo muryoyinsu suna musayan yawu da Abba, Khalifa ɗin ya ce zai dagi Abba, amma kuma Abba ya fisa karfi da jiki mai kyau, coz Abba ɗan kwallo ne sosai, kullum yana cikin buga ball, dalilin haka yasa yake motsa jiki, yana da burin zama shahararren ɗan kwallo a duniya, shi kuma Khalifa kaman wani ɗan daba haka yake, ba arabi ba boko sai shiga faɗan mata a gida, in short ɗan daban unguwa ne kawai Khalifa, amma baya shaye-shaye. Kanin Kalifa mai suna Fahad yaro ne mai hankali da natsuwa, ya yi karatu sosai musamman ɓangaren addini, so ya banbanta da Khalifa, sai ya koma gefe yana jinsu bai saka baki a rigimar ba.
Ban san ya suka kare ba daga baya na ji parlon shiru. A daddafe na yi girki na kawo masu parlo, sai na samu basa nan, Aunty Farida ta shiga ɗakinsu da suke sauƙa idan sun zo, Abba da Fahad sun fita, Abba yana da class karfe 11 dama, ya je shiryawa, shi kuma Khalifa kato da shi ya kwanta mun a saman kujera ya baje yana barci. Takaici tamkar in mutu, amma na daure.
Na bi Aunty Farida da abincin cikin ɗaki, tana ta wani bina da mugun kallo har na ajiye abincin na fita bata yi magana ba. Nima ban mata magana ba. Ina fitowa na shiga side na Abba. A bakin kofa na tsaya na yi knocking, ba jimawa ya buɗe, yana shirye cikin dakakkiyar shaddarsa fara tas, ya kammala shirin zuwa school.
Yana ganina ya yi murmushi har dimple ɗinsa suka lotsa game da cewa. "ALLAH ya ja da ranki hajjajo matar babban yaya, ALLAH ya kara maki hakuri, ya aka yi?"......... "Zo ka ci abinci". Na faɗa game da juyawa ina jin kaina na wani irin sara mun.
Da sauri Abba ya riko hannuna wanda yasa na juyo, ya ce. "Please Aunty don't mind what they're saying, kina da ilimi da hangen nesa, ki cigaba da hakuri watarana komai mai wucewa ne, and please keep smile like the way you are"......... Na ɗan yi one sided smile tare da cewa. "Yaushe nawan ya koma yin wa'azi?". Na faɗa ina ɗaga mashi gera guda....... Ya saki hannuna yana murmushi ya amsa da. "Ba dole in iya wa'azi ba ko dan saboda ke, and waye ya ce maki dama ban iya ba?".
"Ina ka yi to? Ban da harkar kwallo ai kai babu abin da ka saka a gaba, ko makarantar nan ma da ban tsaya tsayin daka ba ba yi zaka yi ba, ni dai fito ka ci abinci ka wuce kada lokaci ya kure maka". Na kai karshe tare da wucewa ina harararsa cikin zolaya. Yana murmushi ya koma ciki.
Na zo na fito masu da abincinsu parlo sannan na koma ɗaki, na gagara cin abinci saboda wannan musifa data kunno kai. Ina zaune a ɗaki Abba ya shigo yi mun sallama zai tafi, na mashi fatan alkhairi ya ce mun yana son kuɗi, na ɗauki dubu goma na bashi muka yi sallama, ya fice ni kuma na tashi Muhammad nai mashi wanka, na shiryasa muka sake kwanciya.
Ina tsaka da kwanciya sai ji nai Aunty Farida na kwala kiran sunana har ta shigo cikin ɗaki. Da sauri na miƙe zaune ina amsawa. A bakin kofa ta tsaya tare da cewa...........
labarin A'isha zai dinga zuwa maku dama wasu labaran masu gajeran zango dan faɗakarwa da ilmantarwa cikin hikima da basira................ Danne like and share fisabilillahi.
LABARIN AISHA.🥹💔
PART 4
Ina tsaka da kwanciya sai ji nai Aunty Farida na kwala kiran sunana har ta shigo cikin ɗaki. Da sauri na miƙe zaune ina amsawa. A bakin kofa ta tsaya tare da cewa. "Sarauniya sarkin kwanciya, ina abincin Khalifa?".
Na miƙe ina kallonta, cikin raunin murya da takaici na ce. "Abincinsa na cikin kitchen"........ Ta wani harareni kafin ta juya ta fita, na rasa me yake mun daɗi, ban saba da irin wannan tashin hankali ba, wayana na jawo na kira mamana, na gagara faɗa mata halin da nike ciki, bayan mun gaisa ta tambayi lafiyar yarana, na ce suna nan lou. Muka ɗan taɓa hira, ta so ta fahimci ina cikin damuwa, amma da ta tambayeni sai na ce mata babu komai. Muka yi sallama na kira sisterta wacce take bina. Bugu ɗaya ta ɗauka tana cewa. "Masoyiya tun jiya ban jiki ba". Kawai sai na ji kuka ya kwace mun.
Katse kiran na yi ban amsa mata ba, ina jinta tana ta rattaɓa mun kira amma naƙi ɗagawa, daga karshe dole ta hakura ta barni. Haka na wuni a cikin wannan gida zuciya babu daɗi, na takura a ɗaki zuwa karfe 1 na fito na ɗaura lunch, Aunty Farida na ɗaki.
Na kammala abinci around 2:30, na ɗauki na Aunty Farida zan kai mata, dab zan shiga ɗakinta na ji tana cewa. "Wlh Mama komai a gidan nan akwaisa enough, sai wadakarsu suke yi, kawai umarninki ne Sulaiman ba zai bi ba, gara kawai ki tattara kayanki ki zo ki zauna har sai bayan auren, idan an yi auren ma ki tsaya tsayin daka dan kada wannan Aishar ta cutar mana da ƴan uwa Zainab".
Hankalina ya yi bala'in tashi, jikina yana rawa, ina ta addu'ar ALLAH yasa dukkan wannan abin mafarki ne. Daga in da nike tsaye ina jiyo muryan Mama a cikin wayar tana cewa. "Tabbas na sani dama, nasan Sulaiman yana da komai a wadace, kawai umarnina ne ba zai bi ba, amma barni da shi, nan da kwanaki uku dole in zo da kaina ba saƙo ba, amma sai na fara zuwa gidan Liman ya bani rubutun karya asirin nan dan in zo da karfina".
Aunty Farida ta amsa da. "Yauwa Mama, ki faɗawa Kawu Liman har da Abba ta yi wa asiri, ta mallake ba iya Sulaiman ba, dan wlh baki ga ɗazun Abba wai zai dagi Khalifa saboda ta zageni Khalifa ya ce zai daketa ba"......... Mama ta ce. "Ta zageki? Aishar ce ta zageki?"......... "Wlh mama zagina ta uwa ta uba ta yi mun, wai mun zo zamu cinyewa mijinta abincin gida, ni da farko ma fushi na yi na ce zan dawo, amma da na tuna abin da ya kawoni, na tuna ceto ɗan uwanmu zamu yi sai na hakura na shanye, amma baki ji irin zagin da ta mun ba, har da ce mun matsiyata ƴan yunwa". Ta kai karshen maganar tana matso kukan munafurci.
Na ji tsoron ALLAH na ji tsoron mutum, ban san lokacin da hawaye suka fara zubo mun tamkar an buɗe tap ba, haƙiƙa ban taɓa sanin ya makirci da munafurci yake ba sai yau, Aunty Farida ta gwada mun na gani, ban iya ɗauka ba a lokacin, sai nike jin tamkar zuciyata zata fashe, kafafuna suka gaza ɗaukana, na durkushe a wajen ina kuka, na ajiye abincinta a ƙasa.
Ban san lokacin da ta kammala waya da Mama ba saboda tashin hankali da na shiga, sai da na ji ringing ɗin wayata a ɗaki ne na farga, da sauri na miƙe, na bubbuga mata kofa, ta ce in shigo, na goge hawayena, kaina a ƙasa na yi sallama game da tura kofa na shiga.
Ban kalleta ba na wuce na ajiye abinci na fito, da sauri na dawo ɗaki na ɗauki wayana. Abbie ne yake kirana, da sauri na bi kiran, ya katse ya kirani, ina ɗagawa ya hau mun jajen wuni da Aunty Farida, dan yasan masifarta. Ban nuna mashi komai ba saboda yana kasuwa, na ce lafiya lou, amma ya fahimci babu wani lafiya lou kawai ina ɓoye mashi ne, sai ya kara bani hakuri yana dannata, mun jima muna waya har na manta da kuncin da nike ciki, ya dinga lallaɓani da kalamai masu kwantar da hankali.
Sai karfe 2:30 muka yi sallama, ina ajiye waya sai ga kiran Abba, na ɗauka, cikin zolaya ya ce. "Kada ki wani ja mun aji already na mallakeki na ajiye a gida, dan haka da na kira ki ɗauka da wuri"........ Na ɗan yi murmushin karfin hali kafin in amsa da. "Ai mu mata ko a ina muke jan aji dole ne".
"Duk ba wannan ba, ya kika wuni da Aunty Farida?". Ya faɗa yana driving a hankali............. "Uhmmm, ya baka dawo da wuri ba?". Na faɗa a ƙoƙarina na kawar da zancen Aunty Farida. Ya ganoni sai ya ce. "Canza topic zaki yi saboda baku wuni ta daɗi ba ko?"....... "Canza mun magana zaka yi? Ni na ce maka bamu wuni ta daɗi ba?". Na faɗa ina sauke ajiyar zuciya, coz hankalina ya kwanta, Abbie da Abba sun sakani farinciki.
"Nasan halin Aunty Farida ne ai, gani nan zuwa gidan ma, na gagara hakura ne kawai na ce bari in kiraki tun kafin na iso in ji ya kuka wuni, coz yanzu muka fito daga class zan je ɗauko su Hassan"........ "To ka mai da hankali ga driving ALLAH ya tsare sai ka dawo zamu yi magana, ni ina cikin ƙoshin lafiya". Ban jira amsansa ba na katse kiran, na buga uban tagumi ina tunanin rayuwa.
Abba ya wuce makarantarsu Hassan ya ɗaukosu suka dawo gida. Tun da suka dawo ban fita ba, a ɗaki Abba ya zo ya sameni, ya yi ta jana da hira mai kwantar da hankali dan in samu farinciki, sai lokacin sallar la'asar ya mun sallama ya fita. Na fito na kama Hassan da Hussaini yau da kaina na masu wanka, na saka masu uniform na islamiya, na basu abinci suka hau ci kafin Abba ya zo, na shiga ɗaki na yi alwala na yi sallah nima.
Ina idar da sallah sai ga Abba ya shigo, hannunsa rike da wani bakin leda, ya miƙa mun yana faɗin. "Kayan lambu sun fara shigowa, na sanki da son garden egg shi ne na gani ana tallah na saya maki". Na karɓa ina godiya, yau tun safe ban ci komai ba sai wannan yalon da ya saya mun, na karɓa na wanke, na yankasa, na zuba a plate na dawo parlo.
Ya kama hannunsu Hassan zasu fita kenan ya ganni a parlo da garden egg ɗin ina ci, ya zo ya ɗauki yanka ɗaya, ya ɗauki biyu ya baiwa Hassan ɗaya Hussaini ɗaya, ya wuce ɗakinsa ya shirya cikin kayan kwallon, suka fito tare da Fahad ɗin Aunty Farida dake ta faman barci tun ɗazun. Fahad ya gaidani a mutunce, na amsa, sannan suka mun sallama suka fita.
Haka na kwashe kwanaki uku da Aunty Farida a cikin gidan nan, daga ni har Abbie lamarin babu daɗi kullum muna cikin damuwa, a ranar kwanaki na ukun ne Mama ta diro garin Kano, daga nan tashin hankalinmu ya kara ninkuwa, a daren da ta zo babu wanda ya yai barci, ta dinga faɗa, ta zagi Abbie tas, ya zauna ya dinga bata hakuri, ni kam nawa zagin ko kuda ba zai tauna kalarsa ba, na ji tamkar in gudu a wannan dare in koma gidan iyayena.
Amma na daure, tun karfe 10 da mama ta iso bayan ta gama zaginmu tasa aka kunna mata wuta a bunner, ta hau banka mana hayaki a gida wai makarin asiri, ban isa in yi tari ba ta ce asirin ya fara komawa kaina kenan, ta zaunar damu a parlo wai dole hayakin ya shiga jikin kowa, maganin bashi da daɗin shaƙa sai warin ruɓaɓen nama, amma haka muka zauna, ta dinga zuba kala-kalan ganyayyakin har 2 na dare, da wannan ya kare zata saka wani.
Tun ina danne kukan dake raina har na kifa kaina da gwiwa na hau kuka ciki-ciki, kowa ya sunkuyar da kai ba halin ya yi magana. Mama ta ce ina kuka ne saboda asirin yana dawowa jikina, ban ce komai ba, na cigaba da addu'a a cikin raina har lokacin da ta gama abin da zata yi ta ce mu je mu kwanta.
Muna miƙewa Mama ta ce. "Kai Sulaiman dawo, ai ba zaka kwana da ita ba, dan kada ta sake maka wani asirin, ka shiga ɗakinka ka kwanta, ni ina nan parlo zan ga kome da zai wakana a gidan nan"....... Ban tsaya sauraren Mama ba, na wuce ɗaki da sauri ina rungume da Muhammad dake barci.
Abbie ya shiga ɗakinsa bisa umarnin Mama, haka ina ji ina gani muka kwana waje daban-daban. Ba shi ne babban tashin hankali ba, ashe tashin hankalina na gaba. Washegari Mama ta hana Abbie leƙa ɗakina, wai ta mashi iyaka dani har sai ta karisa karya asirin nan, na kwana bakwai za'ayi. Haka ya tafi kasuwa bamu gana ba, girki Mama ta hanani yi wai kada in barbaɗa masu maganin mallaka in mallake har da ita, Aunty Farida take girki, ni kam na zama tamkar hoto a cikin gidana, su girka son ransu, sai abin da suka bani zan ci.
Abbie yana zuwa kasuwa ya kirani a waya, ina ɗauka ya fara bani hakuri, na ce mashi babu komai watarana komai mai wucewa ne, Abbie yai ta saka mun albarka, muka ɗan taɓa hira yana kwantar mun da hankali, amma yana katse kiran na rushe da kuka mai ban tausayi.
Ina cikin wannan kuka Abba ya shigo ɗakina. Ya zauna a gefen drawer yana bani baki, na gagara danne kukan, sai na kifa kaina a jikin pillow, na
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 38