amma da na tuna ɗan uwana ba zai cutar dani ba, sai na ce mashi to zan je bank sai in saka mashi. Muka yi haka da kwana ɗaya na samu na tura mashi kuɗin dukka.
Ranar dana tura mashi ya kirani, ya ce. "Duk abin da kike so daga yau ki tambayi Sulaiman tun da shi ya ajiyeki, ba ke kika ajiye kanki ba bare ki dinga rike kanki, kuma ki ce idan yai kasuwa ya baki 5M da kika bashi last week, sannan idan ya dawo ki sake jaddada mashi ya auri Zainab, and ki canza account na shagonki zuwa account ɗina na Gtbank, zamu dinga lissafi duk karshen sati".
Na yarda da yayana sosai, dan shi ma ɗan kasuwa ne na gasken-gaske. Na bi umarninsa, da Abbie ya dawo na saci hanya na je wajensa, still na samu yana waya, yana ganina ya katse kiran ba tare da ya sallami wanda suke waya ba, na zauna a kusa da shi, yana ta kallona, na kara jaddada mashi ya auri Zainab ya haɗamu ko dan in huta da wannan fitina da nike ciki na bala'in su Mama.
Da farko ya ce mun. "Habibi bani da kuɗin auren yarinyar nan, kuma bani da karfin iya rike mata biyu, da na aureta ta zo zata fara haihuwa nauyi ya karumin, yanzu haka kayan dake shagona duk bashi na ɗaukosu, ba hakkina bane, ya za'ayi in ɗauki hakkin mutane in yi aure?".
Na ce. "Duk da haka Abbie ka cika umarnin Mama In Sha ALLAH UBANGIJI zai buƙa maka"........ Ya amsa da ALLAH yasa kawai. A wannan rana ban bar ɗakin ba sai da ya amince da safe zai faɗawa Mama ya yarda zai auri Zainab.
Zuciyata tamkar zata fashe na miƙe na nufi waje, ya kira sunana wanda yasa na juyo ba tare da na dawo in da yake ba, a natse ya ce. "Amma Aisha kin tabbata ban cutar dake ba? Ban zalunceki ba?"...... Na kallesa cike da mamaki, sai na ce. "Me ya kawo wannan magana?".
"Ina son tabbatarwa da ban cuceki a zamanmu bane, kun mun halacci wanda gabaɗaya dangina basu taɓa mun ba dake da danginki, a lokacin da na shiga halin babu duk family ɗina babu wanda ya iya bani aron 1k banza, amma kika ɗebi kuɗi ke da danginki kuka bani, kuka ƴanta ni, so bana son in cutar dake ne, bana son hakkinki ya hau kaina, idan kina ganin kamar akwai abin da nike yi yake cutar dake dan ALLAH ki faɗa mun da wuri dan in gyara".
Na ƙaƙalo murmushin dole wacce ta fi kuka ciwo na amsa da. "Babu komai Abbie, baka taɓa cutar dani ba, bari in je in kwanta"...... Ya amsa da sai da safe, na juya na fita da sauri. Na shiga ɗaki na sha kuka na har tsakar dare, Abba ya kawo mun Muhammad kamar yadda ya saba, na shayar da yarona, sannan ya mayar da shi, ya tasani gaba in ci abinci kamar dai yadda ya saba, dole na ci kaɗan, ya ɗauki sauran ya fita yana mun sallama.
Washegari ranar kwanaki na bakwai kenan da zuwan Mama gidanmu, da safe ina ɗaki na ji kira a parlo, na miƙe na fita, gabaɗaya ahalin gidan suna parlo, na wuce na zauna a kusa da Abba, ina kallon Abbie dake ta faman dannar waya yana ɗan murmushi. Mama ta yi hamdala ga ALLAH, sannan ta ce. "Yau kwanaki bakwai kenan muna maganin wannan asiri, ga shi cikin ikon ALLAH asirin ya karye, yau Sulaiman da kansa ya sameni a ɗaki, ya bani hakuri, ya nemi afuwata sannan ya jaddada mun zai auri Zainab, lallai Liman ya yi gaskiya, lallai A'isha kin bani kunya, amma ba komai, albarkacin iyayenki, ba zan ce Sulaiman ya sakeki ba, amma yazama wajibi yarana su sha maganin kariya daga mugun nufinki".
Na sunkuyar da kai ina jin kuka na zuwan mun, zuciyata na barazanar tarwatsewa, saboda ni nasan gidanmu ahalin sunnah ne, wlh ban da karatun Alqur'ani bamu dogara da komai ba, bama zuwa wajen kowa neman komai face ALLAH da ya haliccemu, amma ana mana muguwar kazafi, ba komai rayuwace.
Abbie bai ce komai ba, sai Abba ne ma ya ce. "Mama dan ALLAH ki bar wannan magana haka, tun da yanzu Yaya ya yarda zai yi wannan auren komai ya wuce"..... Khalifa dake zaune kusa da uwarsa ne ya ce. "Kai kam Abba anya asirin nan ya sake ka kuwa?"........ Mama ta ce. "I wonder ooooo".
"Ban kasa da kai ba Khalifa". A cewar Abba, ya faɗa tare da miƙewa ya ɗauki Muhammad dake kusa da Mama, ya wuce ɗakinsa. Mama ta kalli Abbie ta ce. "Sai ka je wajen sauran kawunenka ka nemi auren Zainab, kada a saka lokaci mai tsawo, ni gobe zan koma Kaduna tun da komai ya warware"....... Abbie ya amsa da okey tare da mikewa ya nufi waje, yana fita na miƙe zan bi bayansa dan ina son yin magana da shi, ina miƙewa Mama ta ce. "Zai fita nema ma ba zaki rabu da shi ba sai kin hana shi fita a kan lokaci ne?"..
Aunty Farida ta ce. "Rashin kunya ne ai, ko kunyar idanunki bata ji"........ Ban ce komai ba na juya da sauri na shige ɗakina ina jin kuka na zuwanmu, ina tuna lokacin da mijin Aunty Farida yake hanasu abinci ni nike ciyar da gidan, ina tuna lokacin da yaranta suka gantalin basa zuwa makaranta saboda ubansu baya ɗaukar nauyinsu ni nike masu komai, amma yau Aunty Farida ni take zagi saboda mijinta baya yi mata abin da kaninta yake mana na kulawa, rayuwa kenan, dama duk macen da ka gani tana jin haushin zaman aurenka lafiya to wlh bata samun rabin kwatan abin da kake samu ne, da tana samun irinsa ko ta fika ko kallon in da kake ba zata yi ba bare ta takura maka, amma tun da ita bata samu ne bari ta hana ayi maka kai, mutum mugub icce.
Ina shiga ɗaki ƙanina ya kirani a waya. Ina ɗauka ya ɗaga mun gaisuwa, bayan mun gaisa sai ya ce. "Aunty jiya ƙarshen sati baki zo mun yi lissafi ba, dama jiya na ce in mun tashi zan zo gidanki in ga meyasa kwanaki biyun nan baki leƙomu a shago".
"Ahmad babu komai, zan zo anjuma mu yi lissafin, abubuwa ne suka mun yawa". Ahmad ya amsa da okey, muka yi sallama, na zauna ina tunanin rayuwa, saboda gudun fitinar dangin miji fa yasa na kamawa Ahmad haya a wani unguwa daban, dan ma kada su ce na kawo ƙanina gidan muna cinyewa ɗansu arziki mun ɗaura mashi nauyi da wahala, amma duk da haka ban tsira ba, ALLAH dai ya kyauta.
Yau da yake an gama maganin makarin asiri in ji Mama, sai ta barni na sake a gidana, an dawo mun da Muhammad, dan haka da yammma na shirya muka je shago da Muhammad, Abba ya tafi wajen kwallonsa, Hassan and Hussaini suna islamiya.
Ina zuwa shago muka yi lissafi da Ahmad, a wannan sati kasuwa ta yi kyau, Alhamdllh mun samu ribar almost 550k, sannan mun yi ciki sosai, dan a kallah tsabar kuɗi a ƙasa akwai 8M, na kira yayana dan in faɗa mashi, yana ɗauka ya ce. "Ke zan kira yanzu dama".
Na ce. "Sai kuma ga shi na kiraka".... Ya ce. "To fara faɗa mun naki dalilin na kira kafin in faɗa maki nawa"........ Ina murmushin yaƙe na ce. "Mun yi lissafi ne a shago, ga abin da aka samu, ga kuma tsabar kuɗin dake ƙasa".
Da buɗar bakin yayana sai ya ce. "Ki tura mun kuɗin dukka, da ribar da uwar kuɗin, ina son shagonkin nan sai ya zamana jarin 5M ne kawai a ciki zaki barsa"....... "Yaya meyasa?". Na tambaya a raunace.
"Kada ki sake tamnayata, kawai ki yi abin da na ce, idan lokaci ya yi da kaina zan faɗa maki abin da yasa". Ya faɗa, a cikin zuciyansa kuwa, yana tunanin yadda zai sakani in zame dukiyata dake hannun Sulaiman, idan har wannan shagon nawa akwai kaya, to lallai Sulaiman ba zai daina karɓar arzikina yana abin da yake so ba.
Na amsa mashi da okey tom, sai ya ce. "Ki nemi izinin mijinki ki zo Kaduna a satin nan, ina buƙatar ganinki"...... Nan ma na amsa mashi da to, muka yi sallama, na bawa Ahmad kuɗina dukka na ce ya je ya sakawa Yaya a account ɗinsa a banki. Ya ce okey, sannan ya ce yana son kuɗi akwai abubuwan da zai saya, na ce ya tambayi yaya, yadda suka yi dukka ni yanzu shago ya bar hannuna.
Daga nan na miƙe na dawo gida. Ina dawowa na ɗaura girkin dare, na dafa amma Mama bata ci ba, wai kada na saka asiri a ciki tun da na fita da yamman nan. Na ci abincina ni da yarana, ko Abbie bai ci ba Mama ta hana shi, tun kafin Mama ta hana shi ma ya ce ya ƙoshi.
Abba kuwa ya saci hanya ya ci girkina, domin idan akwai abin da za'a fi yabani da shi to shi ne iya girki bayan yawan ibada, na iya girki sosai, Abba ya ce girki idan ba nawa ba duk lami ne, shiyasa baya taɓa cin abinci wajen kowa sai wajena, idan yai tafiya zuwa Kaduna ya dinga damuwa kan abincin can babu daɗi, shiyasa bai cika yin tafiya bama.
Duk da an gama maganin makarin asiri ban kwana tare da Abbie ba, saboda ina shiga ɗakinsa na same shi yana barci, sai na dawo ɗakina kawai na kwanta, da yake ma bana jin daɗin jikina. Washegari da safe Hajiya Mama ta mana sallama ta koma Kaduna, amma kafin nan sai da ta mana nasiha sosai, ta dinga mun faɗa wai inji tsoron ALLAH in daina bin malamai, ni kan na ce mata to kawai.
Aunty Farida ma da guntun nata nasihar wai miji da makirci ake mallakesa bada asirai ba, a raina na ce shiyasa naga naki mijin ya gagara rikeki ai, duk makircin naki ga shi kina gantali a titi na neman abin da zaku ci, a fili kuwa na ce Nagode.
Mama ta jawa Abba kunne sosai, sannan ta ce ga su Khalifa amana, Abbie ya ce babu komai, suka mana sallama suka tafi, Abba ya kaisu tasha suka shiga mota. Suna tafiya na kalli Abbie dake zaune a kan kujera, na ƙaƙalo murmushi dole kamar yadda yayana ya ce kada in nuna mashi ɓacin raina, na ce. "Abbie ba zaka je kasuwa bane yau?".
Ya ce. "Yau ranarki ce uwar gida ran gida, yau zan zauna tare dake"........ Zuciya bata da ƙashi, na ɗan ji daɗin kalamansa, har da ajiyar zuciya na sauke, sannan na ce. "Abbie, amma komai iri ɗaya zaka yi mana da amarya ko?"........ Ya kalleni yana murmushi kafin ya ce. "Haka kike so? Ai kin san duk abin da kike so shi zan yi, kinga auren ma sai da kika nuna kina so zan yi".
Na kara faɗaɗa murmushina kafin in ce. "Kai Abbie, kai Abbie"...... Ya ce. "Wlh da gaske, a wannan hidima duk abin da kike so shi kawai za'ayi"....... Ba ƙaramin daɗi na ji ba, sai na ce. "To shikenan komai iri ɗaya zaka mana ni da amarya, sannan ni zan je in sayo mana".
Ya amsa da. "An gama uwar gida". Yana magana yana murmushi, mun wuni tare yau cikin farincikin da na jima ban shiga ba, sai around 3 ya ce zai je da kansa yau ya ɗauko su Hassan dan suma su shaida Abbie ɗinsu ya dawo garesu. Na ce adawo lafiya. Yana fita na ɗauki waya na kira yayana.
Na kyankyasa mashi duk abin da ya faru. Ya ce. "Yauwa ƴar albarka, tun da ya ce duk abin da kike so za'ayi bari in faɗa maki yadda zaki yi, kinga yanzu ba zai so rigima dake ba, dan hankalinsa na kan auren, lallaɓaki zai dinga yi, yanzu ne kike da dama, dan haka abin da nike so dake daga yau.........
labarin A'isha zai dinga zuwa maku dama wasu labaran masu gajeran zango dan faɗakarwa da ilmantarwa cikin hikima da basira................ Danne like and share fisabilillahi.
LABARIN AISHA.🥹💔
PART 7
"Yauwa ƴar albarka, tun da ya ce duk abin da kike so za'ayi bari in faɗa maki yadda zaki yi, kinga yanzu ba zai so rigima dake ba, dan hankalinsa na kan auren, lallaɓaki zai dinga yi, yanzu ne kike da dama, dan haka abin da nike so dake daga yau ki koyi zame dukiyarki daga cikin nasa a hankali cikin hikima da basira, kada ki bari ya farga, kafin ya farga kin kwace dukiyarki, ba faɗa ba gaba, kada ki kuskura a ƴan tsakanin nan ki yi gaba ko faɗa da shi, ki nuna mashi kina tsananin farinciki da wannan aure, da fatan kin gane?".
Watau yaya ya gama gano cewa tun asali Abbie yana son yarinyar nan Zainab, kawai ya ɓoye mun ne, kun san maza sun san duk wani makirci na ɗan uwansu namiji, ba wani zancen baya sonta a nan, wayau kawai yake mun, ni kuma na yarda da Abbie, gani nike kawai ba zai taɓa cin amanata ba.
Na ce da yaya na karɓi shawaransa kuma zan yi yadda yake so In Sha ALLAH. Muka yi sallama na ajiye waya ina tunanin rayuwa, daga karshe na kwanta na yi barcina. Bani na farka ba sai 12 na rana, na tashi na shirya shiga kitchen, na haɗa mana lunch mai rai da lafiyar da na jima ban yi irinsa ba.
Ina tsaka da girki Abba ya shigo kitchen ɗin, ban ma san yana gidan ba, ashe da na yi barci ya dawo, da ya shigo yaga ina barci sai ya wuce room ɗinsa. Ban ji shigowansa kitchen ba sai ji na yi abu ya taɓani a bayan wuya. Razana nai game da sake ƴar kara saboda ina da tsoro sosai, na juyo da karfi.
Four eyes muka yi yana tsaye yana kallona, ya yi folding hands ɗinsa a saman kirji. Na dallah mashi mugun kallo ina sauke numfashi, duk tunanina wani abin ne ya taɓani, ashe shi ya saka mun wani ganyen flower a wuya...... Ya ɗan yi dariya game da cewa. "Sarkin tsoro kawai, ke Aunty ban san yaushe zaki girma ba, tsoronkin nan ya yi yawa, dole in karo mata jarumar da zata dinga tsare mun gida, haba, wannan ai da kin ji ɓarayi zaki shige ƙasan gado ne na sani".
Ina harararsa na ce. "Nawan! Nawan! Nawan! Sau nawa na kira sunanka?"..... Ya ɗan sunkuyo ta gabana kaɗan kafin ya ce. "Sau uku Auntyn tawan ta kirani......." Ban bari ya karisar da maganar ba na ɗebo ruwan bowl ɗin bayana na watsa mashi a fuska tare da cewa. "Dole in maka iyaka da wasu sassa a cikin gidan nan, dan yanzu ka girma ba kamar da bane, kada ka sake shigo mun kitchen!". Na faɗa ina ɗaure fuska.
Yana ɗan murmushi ya amsa da. "Eyyye, ni da gidan nawa? To ki shafawa kanki lafiya tun ma kafin raina ya ɓaci na baki suspension"........ Na juya na cigaba da aikina tare da cewa. "Nawan, ka daina yi mana yawo da gajeran wando a gidan nan, dan kana ɗan kwallo sai ka ishemu da sportswear, kuma wlh aure zaka zo ka yi in huta, dan ka isheni haka".
Ya matso kusa dani, ya ɗan jingina da jikin drawers na kitchen ɗin tare da cewa. "Ni da aure, tab, sai na girma, yanzu kam ban kai ba, kuma ni da gidana dole in yi yawo da sportswear". A ɗan shagwaɓe yai maganar, wani lokaci Abba ya iya shiririta saboda ɗan Auta ne, Mama ta shagwaɓa shi sosai, shi nan gani yake bai girma ba, kuma har cikin zuciyansa wlh yake ganin kamar bai girma ba, yaro yake ɗaukan kansa, shiyasa ma yake shagwaɓa sosai har yanzu.
"Zaka ga baka kai aure bane, sai na je na faɗawa Mammyna kana son sister Safiyya, daga nan manya su shiga lamarin, ni dama already na mallaka maka ita, sai aure kawai".
Da sauri ya ce. "Aunty wannan sister ɗin taki mai kama dake?"....... Na gyaɗa mashi kai game da cewa. "Ita fa, kaga yanzu tana da 14 years, kai kuma 25, zaku dace, sannan kaga tana SSS1, sai ayi magana, a saka rana, kafin ta kammala secondary school kai ma ka kammala karatunka ka fara aiki, sai ayi auren kawai".
Da sauri ya tari numfashina da cewa. "A'a Aunty, wani aiki kuma? Ni fa ɗan kwallo ne, meyasa baki son yin fatan alkhairi a kan burina?"....... Ina yanka ganyen ogu na amsa da. "To Malam ɗan kwallo, ni dai yanzu ka samu Safiyya ku fara gaisawa".
Ya sake matsowa kusa dani, ya fara tayani tsinke ganyen, saboda ya iya sosai, coz cikin mata ya taso, shiyasa wani lokaci yake da shiririta ga shagwaɓa, duk wani aiki na mata ya iya. Yana tayani tsinke ganye ya ce. "Amma Aunty anya zata yarda dani kuwa?".
"Meyasa ka ce haka?"...... "Naga ƴan gidanku basa saurin yarda da mutane, and suna da kamewa sosai, bugu da ƙari ba ƙaramin abu bane yake jan ra'ayinsu"..... Na ɗan kallesa kafin in ce. "Waye ya ce maka hakan? Ba ga shi ni na yarda da yayanka ba, na aminta da shi, dan haka ƴan gidanmu suna da yarda da mutane, kawai saurin sabo ne bamu da shi, kai ma da ka zo gidan nan ai kafin mu saba an kai watanni shidda, da muka saba kuma ba shikenan ba".
Yai ɗan dariya game da cewa. "Wahala dey for who is dating one of your family Aunty, yanzu sai na yi 6 months ina bin Safiyya kenan kafin in samu yarda?"......... Na hararesa kafin in ce. "Ni kam yayanka ya yi 6 months kafin in sauraresa ne?"......... Ya ɗan nisa game da ɗan canza mood, ya ɗan haɗe fuska kafin ya amsa da. "Yayana yana da saa sosai ne, amma kuma Aunty ai shima ya sha bakar wahala, sama da shekara kuna rigima a kan baki son shi, shiyasa yanzu nike tsananin fargabar ya ci amanarki, ku ƴan gidanku basu da saurin sabo, amma in kuka saba da mutum, to kun gama bashi yarda ne, ina tsoron yaya ya rasa wannan yardar da kika bashi, ina maku addu'a kullum, sannan ina maku fatan ALLAH yasa wannan abin ya zo da sauƙi".
"Kai nawan, waye ya ce maka yayanka zai ci amanata? Na san shi sosai, na yarda da shi, yana da hankali da ilimi, ya san me yake yi, ba zai taɓa cin amanata ba Abba, i trusted him more than your expectations".
Abba ya girgiza kai cike da tausayina, ya ji tsoron ALLAH ya ji tsoron yardan da na baiwa yayansa. Sai ya canza topic na hiran da cewa. "Aunty duk bama wannan ba, manta da batun yaya, please Aunty maganin can zaki sake saya mun, sannan ki bani number Safiyya ɗin".
Na juyo da kyau na kallesa kafin in ce. "Nawan, ban fa yarda da kai ba, wai wani irin magani ne kake saya duk wata, yaushe na bada kuɗin maganin nan 10k? Ka faɗa mun cutar dake damunka kaki, baka yarda dani bane?"......... Ya ɗan ja dogon hancina ƙaɗan game da cewa. "Idan akwai wanda zan yarda da shi to ya biyo bayanki Aunty, kawai wlh ba zan iya faɗa maki abin dake damuna bane, kuma wajibi ne in dinga shan wannan magani idan ina son zaman lafiya, maganin da na saya last week faɗuwa yai a school ban gansa ba, shiyasa zan sayi wani".
"Nawan, watau har yawo ma kake yi da maganin? Wani irin ciwo ne yake damunka haka? Please in har ka yarda dani ka faɗa mun damuwarka, ka sani ma ko nasan maganin da ya fi wanda kake sha kyau da amfani?".
Ya ɗan ɗauke kallonsa daga kaina, yana wani son dojewa kada ya faɗa mun, sai ya ɗauko zancen Safiyya tare da cewa. "Aunty bani number Safiyya ɗin". Ya faɗa game da ɗaukar wuka zai yanka ogu da ya gama tsinkewa........... "Nawan, in dai ba zaka faɗa mun abin dake damunka ba kada ka sake mun magana, ban taɓa tunanin akwai rana da zata zo wani abu na damun ɗayanmu mu gagara yin sharing problems ɗin da juna dan neman mafita a tare ba". Da iya gaskiyata na faɗa, coz ya kai shekara biyu kullum Abba sai ya sayi magani, kuma yaki faɗa mun me yake damunsa, baya son in sani, and kullum yana yawo da maganin a jikinsa, alamar cutar tana da karfi kenan, kuma tana da haɗari a garesa.
Shiru ya ɗan yi, gabaɗaya mood ɗinsa ya canza, har cikin zuciyansa baya son faɗa mun abin dake damunsa, amma baya son ɓacin raina, jikinsa duk ya yi sanyi. Ban sake bi ta kansa ba na cigaba da aikina bayan na bashi number Safiyya. Ganin hakan yasa ya tayani komai bai sake yin magana ba shi ma, har muka kammala around 1:30 ba rana, muka fito, ya wuce ɗakinsa nima na wuce nawa ba wanda ya sake yi wa juna magana. Wanka na yi na ɗauro alwala, na zo na yi sallar azahar, ina idarwa na yi zaman askar.
1:40 daidai Abba ya shigo ɗakina bakinsa ɗauke da sallama, ciki-ciki na amsa mashi, ya zauna a ƙasa kusa da daddumar da nike kai, yana kallona ya ce. "Auntyn tawa, yanzu da gaske fushi kike yi dani kenan?". Na yi shiru ban amsa mashi ba.
"Shikenan zan faɗa maki abin dake damuna, amma fa ki sani ko Mama ban taɓa faɗa mata ba, daga ni sai ALLAH kuma ban yi niyyar faɗawa kowa ba, kema saboda kin ɓata rai ne, kuma bana son ɓacin ranki shiyasa zan faɗa maki, amma please ki rike mun amana, ko yaya kada ki faɗawa dan ALLAH"....... Na hararesa ban yi magana ba, ya ɗan sunkuyar da kai saboda tsananin kunyar maganar da yake ji, ya kara natsuwa kan wanda yake da shi, dan gaskiya Abba akwai natsuwa sosai kaman yayansa haka yake.
Yai ƙasa da murya can kafin ya ce. "Nasan kin san gabaɗaya yaran Mama muna da wannan matsala ta karfin sha'awa, daga matanmu har mazanmu haka muke, halitta ce, to wannan ne yake damuwa sosai, gudun afkawa wata ɓarnar yasa nike shan wannan maganin dan kwantar da shi, sau uku nike haɗiyar maganin a rana shiyasa nike yawo da maganin a jikina, dalilin da yasa wani lokaci zaki ga bana sallah a jam'i sosai har yaya yai ta faɗa, ina yawan zubar da sperm sosai, amma Dr ɗin yake bani maganin nan ya ce in dinga kallon fina-finan batsa zasu dinga taimaka mun, sai dai ba zan iya ba, saboda haramcin hakan, shiyasa nike wahala sosai duk da ina shan maganin". Tun da ya fara magana bai ɗago ya kalleni ba har ya kai karshe.
Gabaɗaya sai na ji na yi nadamar saka shi dole ya faɗa mun abin da ya fi shekaru biyu yana ɓoyewa, duk na ji wani irin kunya mai tsanani ya kamani, na gagara ɗagowa in kallesa nima, tabbas nasan gabaɗaya yaran Mamansu haka suke, harta matansu, dan wlh duk matan idanunsu jajir yake, suna da muguwar karfin sha'awa bare kuma mazan, haka Abbie yake, kuma dalilin mutuwar auren Khadija da Amina sister ɗin Abba kenan, wannan karfin sha'awar tasu ya kashe masu aure, saboda sun aurin mazan da ba zasu iya yi masu yadda suke so ba, duk gidan kanwar Abbien mai suna Homaira takwarata ce kawai nata da sauki, amma har Aunty Farida wannan abu yake addabama shiyasa kullum suke faɗa da mijinta ga yawan haihuwar da take yi, mijin ya ce baya son yara ita kuma jarababbiya, ya ce wlh idan ta sake haihuwa ba zai ɗauki nauyin yaran ba dan ba zai iya ba, so jaraba a cikin jininsu yake, and duk nasan da hakan, sai dai ban yi tunanin na Abba yai tsamari haka ba.
Ganin na gagara yin magana kuma ba zai iya ɗagowa ya kalleni bane yasa ya miƙe ya fice waje da sauri, ai yana fita na ɗauko wayata na tura mashi kuɗin maganin, ina dalili, haka kawai ya je ya kawo mana yaro daga waje, ai gara ya dinga shan maganinsa ya fi mana sauƙi,
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 4 Chapter of 38