nasaba da wanzuwata a ɗakin domin kada in ji mi suke faɗa.
Sun ɗauki tsawon lokacin da yakai hour ɗaya cikin ta biyu suna magana wanda ban san abinda ya tsayar da Hajiya waje ba har yasa bata dawo ba. Fira suke wacce ta gigitani da kuma ɗaiɗaiɗaita tunanina, firar da ta shigar dani cikin tsananin duhu da ruɗanin neman ƙarin bayani dangane da abubuwan da kunnuwana suka jiye mini, zuciyata ce ta tsinke! Tunanina ya juye! Hankalina ya yi tashin gwauron zabin da ban san ma miye ya kamata na yi ba. Miye wannan suke magana akai? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Wai miyasa duniya ta dawo haka ne? Miyasa cin amana da zalunci ya zama kamar shan ruwa a wurin wa su?.
Miƙewa na yi jikina na rawa na sulale na bar ɗakin, domin akan maganar ta yi masu daɗi, dariya suke suna ta kekkewa hankalinsu kwance.
Tafiya nake amma a matuƙar gigice nake, domin bana kallon ma inda nake jefa ƙafata tsabar tashin hankalin da nake ciki, har na kai gida na faɗa ɗaki na kwanta ina mai rushe wa da kuka ban san miye yake damuna ba, jikina sai wata ciccira yake tamkar wata mai sabuwar cutar jijjiga.
Ammie da kambala sallar ta kenan tayo kaina da gudu tana mai janyoni jikinta hankali tashe tana faɗin.
"Lafiya Beenafah! Miye ya faru dake?"
Girgiza kaina na shiga yi ina kuka ina faɗin.
"Ba komai... Ba komai Ammie! zazzaɓi ne kawai nake ji... Zazzaɓi mai zafi sosai... Taɓa jikina ki ji ya yi zafi sosai Ammie.."
Da sauri ta kawo hannunta zuwa wuyana zuwa goshina. Cike da tashin hankali ta ce.
"Wai Beenafah dan Allah ba za ki tausayawa kanki ki ɗau dangana ba? Ke ce fa kike mini nasiha akan kada in damu da komai in yi haƙuri Allah yana sa ne da komai..."
Haka ta ɗauki tsawon lokaci tana lallashina tare da bani baki a hankali har ta samu na natsa da kukan da nake yi ba tare da amsa mata ko da magana ɗaya ba.
Duniya ta bani mamaki, matuƙar mamaki wanda har yanzu ba ta daina ba, domin kullum kwanan duniya akan bani sabon darasi take kamar ko yaushe.
Yanda na ga rana haka na ga dare domin ko kaɗan ban samu na runtsa ba, tunane-tunane kawai na ke da neman mafita. In saƙa in warware in saƙa in warware haka nai ta yi har gari ya waye.
Ina tashi na yi sallah na fito da nufin aiki sai Ammie ta hanani ta ce na koma na kwanta, ko gidan aikina ba zan je ba domin rashin lafiya ya kauda komai, sai da lafiyar ake iya yin wani kataɓus saboda haka na koma na kwanta abina.
A yanzu, ba saurarar maganar ta ce a gabana na ba, domin ni sam ban ga ta zama ba. Hakan yasa ban ko bi takan wanka ba na ce mata dole sai na fita domin akwai ajiyar da Hajiya ta bani kuma nice kaɗai zan iya ɗauko wa daga inda na ajiye, ga shi za ta yi asuba zuwa Kebbi, saboda haka dan Allah ta barni in tafi in bata saƙon daga baya sai in dawo tunda babu wayar da zan kira in shelanta musu uzurina.
Ko makaho ya shafa yanayin da nake ciki yasan bana cikin hayyacina, ta dalilin damuwata da ta gauraya da wata gingimemiyar damuwar da ban san ma ta ina zan fara ba. Gidan Aunty Labiba na nufa ba tare da jin wani ƙiren tsoro ba na ƙwanƙwasa ƙofar gate ɗin.
Kallona Mai gadin na su yayi ba tare da ya gane ni ba ya ce.
"Malama ke wacece kuma wa kike nema?"
Kai tsaye na ce.
"Wurin Aunty Labiba na zo, dan Allah kira ta kace ta yi baƙuwa..."
Agogon ƙaramar wayarshi ya duba yaga cewa bakwaice yanzu na safe da mintuna tara. Cike da zallar mamaki ya ce.
"Ina fata dai lafiya?"
"Lafiya lau, ka kirata ka ce mata Beenafah ce."
Wani irin kallon ne ya jefa mini, kamar zai yi magana sai kuma bai yi ba ya ɗauki wayar ya kira ta kusan sau huɗu amma bata ɗaga ba, mita ya fara akan bata tashi ba kuma ƙarshe ma in ja masa ayi masa faɗa.
Ni dai ina tsaye na yi shiru duk abin duniya yabi ya ishe ni. Ina nan ba tsammani daga ƙarshe na ji ya ce in shiga tana ciki ta ce in shigo.
Ina tura ƙofar parlourn na sameta tsaye sanye da kayan baccin ta dogaye har ƙasa ta ƙura mini ido cikin tashin hankali ta ce.
"Lafiya Beenafah?"
Hawayen da suka silalo mini ne na share sannan na jinjina kaina na ce.
"Shin zamu iya zaunawa muyi magana ta fahimta Aunty Labiba?"
Da sauri ta jinjina kanta tana faɗin.
"Of course dear...zo mu shiga wancan parlourn..."
Ta ƙarashe maganar tana jan hannuna da sauri muka shige parlourn ta rufe ruf da key muka zauna a kujera ɗaya gab da gab ta ƙura mini ido tana faɗin.
"Miye ya faru haka Beenafah?"
Still da ruwan hawaye a idona ina kallonta kamar yanda take Kallona na ce.
"Wane ne Muhammad Aunty Labiba???"
Wata irin sassanyar ajiyar zuciya ta sauke a hankali tare da lumshe idanunta ta buɗe sannan ta yi wani murmushi mai gauraye da ruwan hawaye a lokaci ɗaya ta ce mini.
"Yaya MOHAA! Shi ɗin Yayana ne, Shi ne babban Yayanmu..."
Kafin ta iyarda rufe bakinta na gyaɗa kaina na ce.
"To Ina so na aure shi!!!"
Wata irin zabura ta yi ta miƙe tsaye har saida na ɗan tsorata ta kalleni hankalinta a tashe ta ce.
"Kin san mi kike faɗa kuwa Beenafah???"
Gyaɗa kaina na yi ina kallonta na ce.
"Na sani!!..."
Girgixa kai ta shiga yi tana faɗin.
"A'a, baki sani ba Beenafah....gaskiya baki sani ba.."
"Aunty Labiba ina sane da komai, a hayyacina nake, kuma shi nake so shi zan aura..."
Wani irin kuka ne ta fashe da shi wanda ya sarƙafe zuciyata da matsanancin ruɗani da tsoro.
Shiru ɗakin ya ɗauka na tsawon lokaci wanda daga ni har ita babu wanda ya yi magana sannan daga ƙarshe ta ɗago idanunta waɗanda suka jiƙe da ruwan hawaye ta kalleni tana mai girgiza kanta ta ce.
"Na sani, you are doing all this things don Kawai ki faranta mini kamar yanda na taimake ki ko? Hmm! Kada ki sakawa ranki abin da ba zai taɓa yiyuwa ba Beenafah. Ko ma a ina kika jiyo tarihin Daddyn Raudah, wannan bai dame ni ba, domin ba abun ɓoyo ba ne,amma kuma ki sani, ba za ki taɓa iya yin nasara ba..."
Wani kallon na yi mata na ce.
" Miyasa kika ce haka Aunty Labiba...Miyasa kike ganin kamar ba zan iya ba? A rashin tayi fa ake barin arha banza...ki barni na jaraba sa'a ta mana.!!!"
Wani irin murmushi ta yi mai sauti sannan ta girgiza kanta ta ce.
"Uhm! Beenafah kenan! neman aure sau ashirin da bakwai...goma sha uku daga ciki har ranar ɗaura aure sai an kai amma kuma a fasa, uku daga ciki hour ɗaya ce zuwa biyu yake ragewa a ɗaura amma kuma a fasa. Manyan mata, manyan 'ya' yan attajirai, har 'ya' yan sarakuna ma an nema, amma kuma ba a yi nasara ba. Ƙarshe kunya ce da baƙin ciki da kuma nadama suke mamaye farin ciki da ɗaukin da muke ciki a maimakon murnar auren. Mun haƙura, mun janye, idan har wannan ita ce ƙaddararsa muna fata Allah yasa jindaɗinsa da farin cikinsa su riskesa a aljanna firdaus idan yana da rabo.... Dan Allah kada ki sa ciwon da ya wuce a wurinmu na tsawon lokaci ki ce za ki sake fama mana shi.... "
Hannunta na riƙo cike da ƙwarin gwiwa na ce.
" Aunty Labiba ki yarda dani, in sha Allahu rabbi da izinin ubangiji wannan karon zamuyi nasara...dan Allah ina roƙon ki da ki amince kuma ki bani goyon baya dan Allah... "
" Beenaf... "
" Trust me.... In Sha Allah we are going to succeed.."
"But how??"
"Gobe za'a ɗaura mana aure. Amma kuma da sharaɗi?"
Wani irin kallo ne ta bini da shi mai cike da tsananin ruɗani da neman ƙarin haske ta ce.
"Sharaɗi Beenafah? Wane irin sharaɗi ne wannan?"
✍️ *OUM-AMEER* ✍️
*GANIN IDO* 🥀🥀
*ADABI WRITER'S ASSOCIATION*
*AMEENA IBRAHIM*
*OUM-AMEER*
*Wattpad:@Ummu-Ameer* *Arewapen:@Oumameer2671*
*FREE-BOOK*
Kuyi sharing, ku yi comment fisabilillahi! Channel ɗinmu na tafe in sha Allahu zamu riƙa yi muku posting gaba ɗaya free books ɗinmu waɗanda babu algus....
*PAGE 28*
"Sharaɗin shi ne; Daga ɓangarenku, daga KE sai SHI ɗin sai kuma waɗanda za su nema masa aurena ne kaɗai na amince kusan da wannan har sai an riga an ɗaura auren. Ina nufin ko Hajiya ban amince da ta sani ba....."
Wani kalar murmushi ne ta saki wanda iyakacin sa kan leɓenta sannan ta girgiza kai ta ce.
"Uhm!Beenafah kenan! In dai akwai biyan buƙata, ai rai ba a bakin komai yake ba. Ina ma ace wannan maganar da kike akan Daddyn Raudah ta tabbata Beenafah! Ina ma ace ba zan farka daga wannan daddaɗan mafarkin farin cikin dana riski kai na a ciki ba..."
"Wannan ba mafarki kike ba Aunty Labiba, ki yarda dani ki amince da maganata. In Sha Allahu gobe mafarkin ki zai cika.....you have done so much to me..Saboda haka ban ga wani dalilin da zai sa in kasa tsamo ɗan uwanki daga cikin rayuwar da yake ciki ba..."
"Shin kin san wane ne Yaya Mohaa kuwa? Shi ɗin ya rayu tamkar wani sarki a cikin babbar masarauta. Sai dai kuma ya fara bankwana da farin ciki ne daga lokacinda ya fara neman aure kusan sau huɗu amma kuma baya nasara. Da farko mun ɗauka cewa maƙiya ne ke yi masa zaƙon ƙasa, wasa-wasa har muka gano cewa ashe baƙar Aljana ce ta aure shi,wanda tun daga lokacin ne abubuwa suka ƙara lalacewa, Hajiya ta baza nema masa aure ba ji ba gani wanda ta kasa yin nasara a kai. Magani kuwa, babu ƙasar da ba'a je ba wurin nema masa magani ba..."
Jinjina kaina na yi ina mai bata tabbaci na ce.
" Tabbas a wannan karon zai yi nasara... "
Hannayenta ta haɗe wuri ɗaya alamar roƙo, cike da magiya ta shiga girgiza kai ta ce.
" Beenafah dan Allah! Dan Allah ki daina...wallahi ko a iya nan kika tsaya ba zan daina gode miki ba..."
Miƙewa na yi a zafafe ina ɗaga murya na ce.
" To amma miyasa? Miyasa kike neman hanani taimakawa mutumin da ya fito daga ɓangaren ki yana mai matsanancin neman taimako? Shin ba ki yarda da cewa al'amarin Allah mai juyawa ba ne a duk lokacin da ya so? Shi ɗin fa mai iya juya al'amarin bawan sa ne daga farin ciki zuwa baƙin ciki ko kuma daga baƙin ciki zuwa farin ciki a duk lokacin da yaso....Kada ki ce za ki tsaurara Aunty Labiba please na roƙeki! Ki barni na gwada taimakawa ko Allah zai sa a dace... "
Jikinta ne ya yi sanyi jin irin kalaman da na ɗaure ta da su wanda daga ƙarshe bayan na dire ta sauke ajiyar zuciya a hankali sannan ta share hawayenta a tausashe ta ce.
" Ba wai bana so ki taimaka ba ne Beenafah...akwai gagarumar matsala ne idan har hakan akayi yunƙurin gudanar da hakan...domin a neman auren sa na ƙarshe ne, Aljanar ta yi alƙawarin ganin bayan duk wacce ta sake yunƙurin amincewa da auren sa....Dan Allah Beenafah ki fahimce ni."
Cike da gardama na girgiza mata kai na na ce.
" Na ji na gani na kuma amince. Dan Allah ki ƙarfafa wannan abun ya tabbata daga yau zuwa gobe."
" To ai Beenafah shi karan kansa nasan ba zai amince ba.... "
" Zai amince Aunty Labiba, ke dai kawai ki kira shi ki masa bayani.."
Miƙewa ta yi sukuku ta fice ɗaga parlourn tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki ta barni nan ina ci gaba da nazarin plan na gaba.
Na jima tsawon lokaci ina jiran ta wanda har ta kai ga na cire rai kwatsam sai ga ta ta dawo riƙe da waya a hannunta,ban san ya suka ƙare da ita ba, tana shigowa ba tare da ta zauna ba ta kalleni fuska cike da alamun fargaba ta ce.
"Baba Ustaz zai ta so daga Abuja yanzu, In Sha Allahu zuwa 4pm na san duk daɗewar sa zai iso. Sai dai kuma, wannan sharaɗin naki ba Yaya Mohaa ba, hatta ni karan kaina na girgiza Beenafah....ta ya ya kike tunanin Yaya Muhammad zai yi aure ba tare da sanin Hajiya ba.... "
Murmushi na yi mata sannan na ce.
" Ba wannan sharaɗin ne buƙatar Hajiya ba Aunty Labiba... Iya farin cikin ɗan ta kawai ya ishe ta."
Jinjina kanta ta yi ta ce.
" Haka ne kuma, to amma yanzu miye abin yi?"
" Gida zan tafi yanzu, ke kuma ki zo gidanmu zuwa an juma idan rana ta yi sanyi."
Fitowa na yi na baro ta kai tsaye ba tare da ta yi wani yunƙuri ba, da alama gabadaya gaɓoɓin jikinta sun sanyaya.
*******
Gidan Daddy kuwa, in banda ƙarar sautin kukan Mummy dake tashi a gigice, babu abin da ka ke ji.
Tun da Daddy ya dawo ya sanar mata wannan mummunar maganar take kuka. Juyin duniya an yi, amma taƙi ta yi magana da kowa musamman Hafiz ɗin, ko kallon in da yake zaune ta ƙi ta yi, ga shi har da Uncle Isma'ila shi ma ya zo tun jiya yana wurin.
Suna zaune a cikin yanayin shiru kowa abin da ya damesa ya damesa, sai ga wayar Daddy security sun kira, cewa ya yi baƙo daga jihar Zamfara.
Cike da zaƙuwa suka ba shi umarnin shigowa har ciki domin suna saka rai da tsammanin cewa, duk wanda zai zo to babu abin da zai kawo shi idan ba zancen Hassana ba.
Kallon shi suke tamkar idanuwansu za su zazzago ƙasa, bama kamar Mummy wacce ta ke jin tamkar ta miƙe ta buɗe zuciyarsa taga miye abun da ke tafe da shi.
Uncle Isma'il yana ganin shi ya wani zaro ido waje alamar mamaki ya ce.
"Kai ne ko? Wato dai duk jan kunnen da na yi maka baka ji ba sai da ka zo?"
Direwa ya yi akan ƙafafunsa ya durƙasa a hankali yana mai jinjina kai ya ce.
"Ni jan kunnen da ka yi mini bai dameni ba, buƙata ta ɗaya ce dan Allah ku amince min ku tausaya mini ku bani Beenafah, wallahi tallahi ina sonta..."
Cikin wani irin takaici Daddy ya kalle shi cike da hargagi ya ce.
"Ashe kai ɗan iska ne!!! Wawa sakarai daƙiƙi...ban yi maka kashedi tun a waya ba na ce kada ka zo nan??"
Cike da magiya ya ce.
"Dan Allah Daddy ka taimaka mini wallahi..."
Wata irin zabura Daddyn ya yi yana wani ihun kiran Security tamkar zai fasa musu dodon kunne yana faɗin.
"Security!! Security!!!..."
Wani irin shu'umin murmushi ne ya suɓucewa Uncle Isma'ila bayan nasarar samowa Mummy mafita da ya yi yanzu-yanzu cikin ƙanƙanin lokaci ya kalli Daddy ya ce.
"Alhaji!! Barshi tukun, ina da wata shawara...."
Tsit sukayi suna kallon shi domin su ji wace irin shawara ce wannan.
"Ba sai ka haɗa shi da security ba,ina so ka bashi sound warning, sannan daga nan ya tattara ya fece kada kuma ya sake nuna maka fuskarsa a nan har abada. Idan ba haka ba kuma, duk irin hukuncin da ka ɗaukar masa shi ya janyowa kansa."
Wani kallon ƙasƙanci Daddy ya jefawa Ashirun sannan ya ce.
" Ai ka riga ka gama faɗa masa komai da ya kamata. Saboda haka, idan kunne ya ji to gangar jiki ta tsira, ka manta da Beenafah....Ka manta da ita har abada, idan ba haka ba wallahi sai na ɓatar da kai..."
Miƙewa Ashiru ya yi jiki a saɓule amma kuma ba don ya haƙura da Beenafah ba ya fice ya bar gidan gabaɗaya. Shi yasan cewa ko zai rasa ransa ba zai iya haƙura da Beenafah ba sai dai idan kuma ya zo a ƙaddararsa cewa ita ɗin ba matar sa ba ce, to sai ya ɗauki dangana.
Kallon Isma'il ɗin Mummy ta yi tamkar idanun ta za su zazzago waje ta ce.
"Isma'il miye shawarar??"
Wuri ya samu gefen da Hafiz yake zaune tun ɗazu wanda ya kasance tamkar mutum mutumi ya zauna ya fara magana da cewa.
"Uhm to! Shawarar tawa ita ce;ai na san dai har yanzu baku sanarwa shi Ameer ɗin da iyayensa cewa Hassana ta tsere ba??"
Da sauri duk suka jinjina kai alamar eh sannan Mummy ta ce.
"Ban cire rai ba har yanzu da cewa za ta dawo kafin bikin nan in sha Allahu. Shiyasa bamu ma yi mafarki gaya musu ba."
Jinjina kansa ya yi ya ce.
"That's very good! Idan har ta dawo ɗin, Alhamdulillah! Hakan aka fi so, idan ma kuma ba ta dawo ba, maimakon rasa waɗannan kadarorin kai tsaye, tun da har ba su san halin da ake ciki ba, to a kira shi Ameer ɗin cikin ɗaki a lallaɓa shi a bashi Beenafah..."
Wata irin uwar zabura Mummy ta yi ta miƙe tsaye tana wani irin girgiza kai ta ce.
" Wane irin zancen banza ne wannan Isma'il??"
" Ai dai kina bari in mutu Hajiya Zaliha kafin ki yi ƙoƙarin binne ni...ina so ki fahimci zancena, a rashin Uwa akan yi Uwar ɗaki! Kuma sai idan dama ta ƙiya ne ake komawa hagu. Ku sani fa; sai idan yaran Alhaji Mansur sun auri waɗannan 'ƴa'ƴan na ku ne sannam za ku iya samun cikar mafarkin ku, idan har kuma daman hakan ta suɓuce muku, to kuwa shikenan kun rasa wannan damar har abada. A madadin yin wannan katoɓarar; a aura masa Beenafahr mana. Ita ɗin mace ce da duk wanda namijin da ya same ta ya cancanci ayi mishi barka,kuma ku sani, dole dai a ƙarƙashin ikon ku take, sai abin da kuka ce za ta yi, muradin shi ne ya aure ta kuma ta haihu a gidan...Namiji ɗaya! Idan ta haife shi a gidan shikenan kwalliya ta biya kuɗin sabulu. Kinga daga zaran anyi auren,Hafiz ko bai da takardu a matsayin sa na Yayan Su dole za a bashi gurbi wanda sai ma ya tsaya yangar zaɓar inda yake so ya yi aiki,sannan kuma duk wani buri da mafarkin ku zai cika, daga zaran ta haihu kuma, za ki iya yin duk yanda za ki yi kisa a sako ta shikenan."
Wani irin kukan farin ciki ne Mummy ta fashe da shi tare da ɗaga hannu sama tana ta zunduma masa addu'a da godiya akan wannan kyakkyawan tunani na sa.
Kallon shi Daddy ya yi cike da ɗan shakku ya ce.
" To amma fa, ba a nan gizo yake saƙar ba Isma'ila. Kasan an yi ta tallata musu yara iri-iri amma suka ce lallai sai sun samu en biyu kamar yanda suke...baka tunanin ya ƙi amincewa?"
"Na yarda da maganar ka Alhaji, amma kuma ai kowa ya shaida ya kuma tabbatar cewa shi Alhaji Mansur ɗin yana matuƙar ƙaunar yaran nasa, idan har yaron ya amince banga dalilin da zai sa ya ƙi amincewa ba, sannan ga hidimar nan ta matso, tabbas zai zama abin kunya ga irin wannan babban familyn aji labarin cewa wai amarya ta tsere saboda bata son ɗan su da aure. Ko don wannan dalilin, ba za su ƙi amincewa ba."
Miƙewa Aunty Aysha ta yi tsam! Ta fice daga ɗakin wanda ba jimawa Husaina ta bi bayanta suka bar su Mummyn nan zaune suna tattauna yanda za su yi abin ba tare da an samu matsala ba.
Hafiz dai zaune yake a wurin tamkar hoto, domin ya kasa sakin jikin sa dalilin Mummy taƙi ta yi masa magana tun da ya dawo.
********
Ni kuwa, cike da ruɗani Ammie ta shiga girgiza kanta alamar bata amince ba dalilin zancen da na zo mata da shi cike da tashin hankali ta ce.
"Ban amince ba Beenafah....wannan ma wace kalar tatsuniya ce mai abin mamaki? Taya don kawai kinji labarin cewa an ce mutum ya kasa auruwa, mutumin da baki taɓa ganin sa ba, baki san asalinsa ba, baki san ya yake ba wai ki ce kin amince ki aure sa....ai gwanda ma Alhaji Mudassir ya aura miki Ilyas ɗin hankalina sai yafi kwanciya da wannan mummunan abun da kike shirin aikatawa... "
Cikin matsanancin kukan da ban san ma ina yinsa ba na girgiza kaina ina faɗin.
"Ammie! Kika ce gwanda Ilyas akan Mohaa? Wallahi tallahi har abada ba za su zama ɗaya ba. Ai idan na auri Ilyas Daddy zai yi farin ciki akan ya sake yin nasara akanmu, wanda hakan baya nuna komai garemu sai faɗuwa da hasara! Amma Mohaa...ko ba komai, zan samu lada domin na kautar masa da baƙin cikin duniya wanda Allah ya yi alƙawari akan hakan cewa, duk wanda ya kautar wa da ɗan uwansa musulmi wani baƙin ciki to shima Allah zai kautar masa da na sa ranar gobe alƙiyama....Ammie dole rayuwarsa akwai tausai, gabaɗaya Familyn suna cikin baƙin ciki da rashin walwala na tsawon lokaci, hakan da zan yi shine zai zama silar farin cikin su Ammie..."
A zafafe ta jinjina kanta ta ce.
"Ki kautar musu nasu baƙin ciki ke kuma ki fara ƙirga kwanakin mutuwar ki ko??"
"Ba zan mutu ba Ammie, In Sha Allahu ba zan mutu ba sai idan kwana na ne suka ƙare! Ammie, Aunty Labiba ta yi mana riga ta yi mana wando, duk alherin da muke ciki a yanzu ita ce sila, Ammie kin ga irin kwantaccen baƙin cikin da yake fuskarta kuwa? Ammie kin ce wurin ceto rayuwar masoyinka sai inda ƙarfin ka ya ƙare...kenan wannan duk ba haka ba ne?"
" Beenafah! Aure fa aka ce miki! Kin san mi kalmar aure take nufi kuwa? Idan fa an shiga fata ake yi sai mutuwa idan ta raba, cike kuma da soyayya da farin ciki da kwanciyar hankali da 'ƴa'ƴa masu albarka! Wannan shi ne mafarki da burin kowace Uwa ta gari akan 'ƴar ta...To kuwa idan haka ne, kika ce kin zaɓi wannan yaron akan wani dalili kina ganin kin yi mini adalci kuwa?"
Hannayenta na kama na jimƙe sosai a nawa, sannan na yi amfani da su na goge hawayen fuskata still ba don sun tsaigata kwarara ba sake ɗagowa na kalle ta a tausashe na ce.
"Ban san ya zan ce miki ba a yanzu,amma kuma duk abinda nake ƙoƙarin aikatawa, kece sila domin ban san komai ba sai irin tarbiyyarda kika ɗorani a kanta wacce tausayi shi ne mafi rinjaye a cikinta. Ba zan miki alƙawari ba Ammie, domin ni ɗin ba ma'asumiya ba ce ballantana in ce miki na san mi zai faru gobe,ina roƙonki da neman alfarma dan Allah Ammie ki karɓi wannan ƙudurin nawa ki kuma tsaya mini akan hakan sannan ki yi mini addu'a. Da in auri Ilyas gwanda na auri Mohaa da ban taɓa gani ko jinsa ba, domin da shi da Ilyas ɗin duk kanwar Ja ce sai dai shi ko ba komai zan faranta ran 'ƴan uwansa waɗanda suka zame mana bangon jingina."
Rungumeni ta yi sosai tana mai fashewa da kuka tace.
" Shi ke nan Beenafah! Na amince tun da har kin kafe akan hakan, to amma ta ya ya kike tunanin wannan auren zai yi nasara daga nan zuwa gobe? Alhaji Mudassir ba zai taɓa aura miki shi ba kinsa. Sannan Malam Habibu (Babansu su Jafaru) ma ba zai tsaya mana ba Beenafah kin dai gani tun zancen Ashiru da akayi a farko ballantana wannan.. "
Janyewa na yi ina kallonta na ce.
" Mu sake jarabawa wurin Baban mu gani mana, ba dole sai munje wurin Daddy ba domin nasan har abada ba zai taɓa amincewa ba. Dan Allah ki tashi kije wurin Baba ki roƙesa dan Allah."
Da rarrashi da komai na samu ta saka hijabin ta ta fice zuwa gidan Maman Fakiha. Na jima a zaune ina dakon jiran ta sannan sai ga ta ta dawo. Jiki a sanyaye ta kalleni tare da girgiza kanta ta ce.
" Wallahi Beenafah na yi iya yanda zan iya, amma yaƙi ya amince mana. Ni nasan tabbas wannan abun da Wuya, saboda haka ki haƙura da wannan al'amari....."
Cike da ƙwarin gwiwa na ce.
"To Ammie ga
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 24 Chapter of 67