Share this page
ɓari, haka ya shiga sarrafani bai ji bai gani kamar wani mayunwancin Zakin da ya shekara bai ci abinci ba. Ban ƙara shiga cikin tsananin tashin hankali da ruɗani ba sai da na ji ya raba ƙafata biyu a hankali ya kai hannunsa wanda yana yi yana addu'a sannan ya ƙara gangarowa ya haɗe bakinmu wuri ɗaya a haka har ya yi nasarar kaiwa ga abin da yake muradi. Jin wani irin azababben zafi na ratsani na janye bakina inata rusa kuka ina turashi ina faɗin. "Innalillahi!... Wayyo Ammie...Wayyo na shiga uku..wallahi Zafi...Dan Allah Ammie ki zo ki ceceni zan mutu wallahi......Wayyo ka daina dan Allah wallahy bana so...Kai ne fa kace ba za ka iya cutar dani ba... Amma miye haka kake yi.. " Wato wannan daren, shi ake kira daren ihun ka banza. Domin wallahy na gurzu ba ɗan kaɗan ba. Na yi kuka tamkar raina zai fita harda majina tsabar wahala da ficewa hayyacina. Mutumin nan ya mamayeni a lokacin da ban tsamma ta ba. Tun ina ɗari-ɗari ina zuƙewa ina tsoro, bai farmake ni ba sai yanxu da ya gama shashatar da ni yasa na gama sakin jiki da shi yay min wayo. Bayan ya gama shan budurinsa can cikin magagin zafi na ji ya miƙo hannu ya janyoni...hannayena na saka guda biyu na turesa da ɗan sauran ƙarfin da ya rage min ina sheshsheka murya can ƙasa tsabar yanda nasha kuka duk ta dusashe na ce. "Ni wallahi ka ƙyaleni...you broke the Promise you made..and kuma hakan ba daidai bane.." Ko kalma ɗaya ya kasa furtawa, hakan yasa ya ƙara matsowa ya janyoni ina ta wani zillewa ya saka ƙarfinsa ya rungumeni cikin jikinsa a hankali yakai bakinsa saitin kunnena cikin wata irin kasalalliyar murya wacce da ƙyar yayi nasarar ƙaƙalo wasu kalmomi ya furzo su zuwa gare ni,ya ce. "I'm sorry Bibi...I love youu" Laƙwas! Haka na koma cikin jikin nasa na lafe tare da ɗora kaina akan ƙirjinsa ina jin kalmomin da ya furta a gare ni suna yawo a cikin kaina har bacci ya yi nasarar ɗaukemu. Baccin nake amma kuma ba don yana mini daɗi ba, sai wani juye-juye nake wanda daga ƙarshe na farka a hankali na buɗe idona. Jin kamar ina jin alamar zazzaɓi wanda ko ɗaga ƙafata bana jin zan iya yi yasa ni fara zubar da hawaye a hankali ina yi ina kallon fuskarsa cikin ɗan hasken da ya rage. Jin saukar damshin ɗumin ruwan hawayena akan ƙirjinsa yasa a hankali ya buɗe idanunsa ya kalleni tare da kai hannu ya yaye gashin kaina ya mayar da shi baya ya shafo fuskata zuwa idona...ni kuma jin kamar hannunsa ya ɗauki ɗumi yasa nima na kai nawa hannun da sauri akan wuyansa da goshinsa, jin yanda ya yi zafi rau yasa na wani waro ido a gigice na ce. "Na shiga uku...are you sick??...Huh!..ji..ji yanda jikinka ya yi zafi..miye abun da ya same ka.??" ******* Gefen su Daddy kuwa, sai da suka shafe tsawon wata biyu a asibiti bayan ance an yi nasarar yi masa aikin amma kuma kullum babu wani ci gaba, domin har yau babu wanda yayi magana wannan ta fatar baki da shi kullum yana sanƙame da bututun shaƙar numfashi. Suna nan a wannan hali wasu daga cikin ƙawayen Mummy suka bata shawara akan cewa su fitar da shi ƙasar waje kada ya zo ya mutu a banza. Haka suka shiga kicaniya wanda gabaɗaya mummy ta dawo tamkar wata mahaukaciya, ta gigice ta susuce ta fice daga hayyacinta. Suna nan suna neman yanda za a yi Hafiz ya bada shawarar siyar da babban shagon da ta yi nasarar buɗewa, domin a yanxu basu da wasu kudi isassu da za su yi amfani da su wurin tafiya nema masa magani har ƙasar waje. Da farko ta so ta yi tirjiya wanda sai daga baya bayan ta rasa yanda za ta yi dole aka soka shi kasuwa aka siyar sannan aka shiga fafutar tafiya. Suna gida da yamma Ita da Hafiz, Aysha da kuma en biyu, daman ita Humaida tana can asibiti sun baro ta wurin Daddyn. Suna nan suna lissafin tafiyar gobe da za'a yi da Mummy da Hafiz sai suka ji ana sallama ƙofar gida. Cikin mamaki Mummy ta kalli Hafiz ta ce. "Waye ne Hafiz?" "mummy ni ina zan sani bayan muna nan tare da ke.." Jinjina kai ta yi sannan tace. "Jeka ka dubo wata ƙila tallafin da muka nema ne muka samu." Yana zuwa ya ga wasu abokanan aikinsa daga kamfaninsu na Wazeermed pharmaceutical tun daga Lagos sun zo tare da wasu mutane guda uku. Cikin wani irin jin sanyin rahama ya miƙa musu hannu da niyyar su yi masabaha amma ga mamakinsa sai ya ga sun ja baya. Wani daga cikin mutum ukun nan da bai sani ba sun miƙo masa envelope da uban stamping ta. Karɓa ya yi hannu na rawa hankalinsa a tashe ya ce. "Ta miye??" "Idan ka karanta za ka gani." Nan gabansu ya buɗe ta ya fara karantawa kamar haka: WAZEERMED PHARMACEUTICAL COMPANY LTD. Headquarter: 22 Wazeer Industrial Estate. Glass House, Lagos, Nigeria. To: Hafiz Mudassir Wazeer Glass House, Lagos State, Nigeria. Takardar tuhuma akan aiki ba tare da bin ƙa'ida yanda ya kamata ba. Ƙarshen bincike da sashen doka da ladabtarwa na kamfanin Wazeermed Pharmaceutical Company Ltd. ya gudanar ya tabbatar da cewa kai, Hafiz Mudassir Wazeer, kana aiki a matsayin Manaja (Manager) a kamfanin dake Lagos ba tare da ingantattun takardun shaidar karatu ko ƙwarewar da ake buƙata ba. Wannan lamari yana ɗauke da babban laifi na karya dokar kamfani da kuma rashin gaskiya a wajen aiki, kamar yadda aka bayyana a sashe na 8 (c) na Wazeermed Employment Regulation Act. Saboda haka, bisa bin ƙa’idojin ladabtarwa na kamfanin, an kama ka tare da umarnin tsare ka ta hannun sashen tsaro na kamfani tare da haɗin gwiwar Corporate Affairs Investigation Board (CAIB) domin ci gaba da bincike. An sanar da cewa ba za a sake ka ba sai bayan an biya tarar doka da kuɗaɗen gudanar da shari’a, waɗanda Alhaji Mudassir Wazeer, wanda ya sanya hannu a matsayin gwarzonka (guarantor) lokacin da aka ɗauke ka aiki. Idan kuma ba a biya waɗannan kuɗaɗen cikin kwanaki bakwai ba daga ranar da ka riski wannan takarda ba, za a miƙa shari’ar ka zuwa ofishin Federal Corporate Crime Unit (FCCU) domin gurfanar da kai a gaban kotu. Ana ba ka shawara da ka bada cikakken haɗin kai ga sashen bincike domin gujewa tsatstsauran hukunci. Sign By: Barr. Kabiru Lawal (LL.B, BL) Shugaban Sashen Doka da Ladabtarwa Wazeermed Pharmaceutical Company Ltd. "Mummyyyy!!!" Ya ambata a gigice jin abin da yafi ƙarfin tunanin sa...... ✍️ *OUM-AMEER* ✍️ *GANIN IDO* 🥀🥀 *ADABI WRITER'S ASSOCIATION* *AMEENA IBRAHIM* *OUM-AMEER* *Wattpad:@Ummu-Ameer* *Arewapen:@Oumameer2671* *FREE-BOOK* Kuyi sharing, ku yi comment fisabilillahi! Channel ɗinmu na tafe in sha Allahu zamu riƙa yi muku posting gaba ɗaya free books ɗinmu waɗanda babu algus.... Na gode sosai da yanda kuka karɓi book ɗin nan. masu tambayata other books ɗina kuma, pls ku duba Wattpad da Arewapen. Tun da na yi loosing wayata har yanzu ban samu time ɗinda na mayar da documents ba tukun, but In Sha Allahu I will try my possible best inga na mayar. Amma akwai documents na paidbooks lols! Don't mindme pls...! Kun san dai sha'ani na kuɗi shi dai daban yake. Kada ku ce nace ba Free-book documents. Dan Allah idan kun shiga Apps ɗin ku daure kuyi following namu. Na gode. *PAGE 40* Da Mummy da Aysha da twins, lokaci ɗaya suka yi rigengen fitowa ƙofar gidan jin wani irin mugun tarasi da Hafiz ɗin ya buga tamkar wanda aka  ƙwaƙwalewa idanuwansa. "Hafiz lafiya??" Da Mummy da Ayshar suka ambata a tare cike da tashin hankali suna masu tsatstsareshi da ido. Jiki na masa mazari ya miƙa musu takarda yana faɗin. "Mum... Mummy wai an kamani da laifin aiki a kamfanin Wazeermed ba tare da shaidar takardun ƙwarai ba...." A tare suka shiga furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Sannan daga ƙarshe Hafiz ɗin ya fashe da kuka yana wani girgiza kansa ya ce. "Mummy wallahi ni ba laifina ba ne ko? Da..Daddy ne ya nema min aikin ni ba ruwana..." Ɗaya daga cikin mutanen ne ya ƙara tsuke fuska ya kalle su ya ce. "Mu ɗin nan fa ba wasa muka zo yi ba a nan kun gane....don't try to joke with us...Saboda haka ka wuce mu tafi.." Mummy na wani irin kuka ta kalli mutumin ta ce. "Amma dai bawan Allah ka na tsayawa a bi ba'asi ko?..." Hannu wani ya sake ɗaga mata yace. "Dan Allah Hajiya dakata! Idan muka je koma miye sai ku zo ku ji daga baya..Amma dai yanzu bamu da wani lokacin ɓatawa a nan." Cikin tsantsar mamaki ta girgiza kai tana kallon mutumin ta ce. "Yanzu kai Adam ni zaka kalli tsabar idona kana faɗamin wannan magana? Ni ce fa Zaliha matar Alhaji Mudassir Wazeer...wannan kuma ɗan sa ne Hafiz ko ka manta?" Ba tare da nuna wani alamun maganarta ta yi tasiri ba ya ce. "I'm sorry Hajiya, but I'm not after that. Ni kawai aikina nake yi." Daga haka suka tasa ƙeyarsa suka hau mota gaban idanunsu suka wuce da shi. Wata irin gigitacciyar ƙara ce Hassana ta buga tare da sulalewa ta zube ƙasa tare da dafe ƙasan cikinta tana faɗin. " Na shiga Uku cikina...Wash Allah na! Dan Allah ku taimaka mini..." Da gudu suka yo kanta yayinda Mummy ta janyota jikinta tana wani irin kuka ta ce. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Na shiga uku na lalace ni Zaliha...wannan wace iriyar baƙar ƙaddara ce ta zo mana a wannan lokacin...mine ne? Miye ya same ki?" Idon Aunty Aysha na sauka akan jinin da ta gani ya wanke ma Hassanar zanin jikinta ta fasa wata irin ƙara tana faɗin. " Wayyo Allah! Cikin da yake jikinta ne ya fara zuba. Jini Mummy... Kalli Jini..!" " Jini kuma Aysha?" Cewar Mummy tana mai ƙara zaro ido waje tamkar za su zazzago su fito waje tsabar kaɗuwa da gigicewa. "Momm... Mota... Bari na janyo mota.." Cewar Husaina a gigice tana mai juyawa da gudu ta koma gida ta ɗauko Key suka cicciɓata a tare suka saka a mota ta kunna a tsiyace suka kama hanyar asibiti. Suna cin tafiya kawai suka ji motar ta fara jacking kafin kace mi ƙarfen nasara marar tabbas taja ta tsaya. Cikin tashin hankali Mummy ta leƙo mazaunin drivern ta ce. "Husaina dan Allah ki taimaka ki ja mu tafi....kalli yanda take zubar da jini.." Husainar na wani irin daddaga motar tana iya yinta ta ce. "Mummy ba laifina ba ne... I don't know what's wrong with the car.." Wani abu ne taji ya wuce mata muƙut a throat ɗinta ganin ashe Mai ne babu ta wani daki starring motar da ƙarfi ta ce. "shit! Mummy wallahi fuel ne babu.." Ai a 360 Aunty Aysha ta ɓalle murfin motar ta fito ta tsaya gefen hanya tana neman abun hawa. Ta kusa minti talatin sannan da ƙyar ta samu wani bawan Allah ya tsaya yayi da sunan yi musu lift. Tamkar matacciya haka suka cicciɓo Hassana suka shiga motar da Ita yayin da suka bar Husaina nan tare da bata ATM card suka ce duk yanda za ta yi ta yi ta saka mai ta cim musu asibitin. Tsaye tayi a bakin hanyar tare da jingina bayanta jikin motar ta fashe da kuka tamkar wata ƙaramar yarinya tana magana da ƙarfi tana sabbatu. "Dan Allah yanzu ina amfanin hakan? Mummy ina ta nuna muku ina muku Nasiha amma haka kuka ɗaukeni yarinya ƙarama wacce bata san mi take ba...yanzu ga shi ko'ina ba'a je ba sai masifu ke ta abko mana iri-iri.." "Malama ya dai? Ko kin zare ne?" Lokaci ɗaya ta haɗiye kukan ta tare da ɗan ware idonta ta kalli mutumin da ke gaban ta cike da saka rai ta shiga goge hawayen da bayan hannunta murya a karye ta ce. "Ba zarewa na yi ba, mo... Mota ta ce Mai ya ƙare..." Dariya ce ta suɓuce masa yana girgiza kai ya shagwaɓe murya kamar yanda ta yi ya ce. "To kuma shi ne don kawai Mai ya ƙare a mota dan Allah sai ki tsaya kina kuka? Tsabar dai ku yaran masu kuɗin nan daɗi yayi muku yawa ba ku da wata damuwa..." Shiru tayi masa kawai tare da yin addu'a a ranta Allah yasa ya tsaya ya taimaketa. Wayar shi ya ciro ƙarama daga gaban aljihun rigar sa ya kira waya, cikin mintunan da ba su gaza biyar ba, sai ga wani ya fito daga motar sa ya karɓi mukulli sannan ya kalleta ya ce. "Yarinyar Daddy kawo Mukullin a saka miki fuel ɗin." Hannu na rawa ta miƙa Key ɗin sannan ya yo gaba ta bishi. Motar sa ya buɗe ya shiga ya Buɗe mata ya ce ta shiga. Bayan ta shiga ya rufe motar ya kalleta ya ce. "Sai ina?" Wayar ta ta ciro tana faɗin. "Bara na tambayi Aunty Aysha asibitin da suke in ji..." "Wani ne ba lafiya?" Gyaɗa kanta ta yi ba tare da ta kalle sa ba ta ce. "Twin sister na ce ba lafiya, shi ne muka fito zamuje asibiti sai motan ya tsaya.." "Eyyah! Sorry! Allah ya bata lafiya." Bayan ta faɗa mata address ɗin ba jimawa sai gasu asibitin. Da gudu ta fito ta wuce ba tare da ta tsaya ma jin ina labarin motar Mummy ba. Tana shiga ta fashe da kuka ganin yanda duk suke kukan babu wanda ke iya rarrashin wani. " Aunty Aysha ya jikin na ta?" Girgiza kai Aunty Aysha tayi cike da damuwa tace. "She lost it..." "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Allah ubangiji ya bata lafiya ya bata wani mai albarka." "Amin." "Salman fa Aunty Aysha?" "Yana hanya..." "Wayyo Allah! Na san yana can duk hankalinsa ya tashi. Kullum maganar sa ɗaya ce dai, Hassynah ki kula da kanki.." "To ya za'a yi! Ba wanda ya isa ya gujewa ƙaddararsa. Sai hak'uri. Allah dai ya bata Lafiya." "Amin." Kallon Mummy ta yi wacce ta buga uban tagumi tana mai jin duniyar ta game mata sama da ƙasa akan wannan rikitaccen al'amari. "Mummy! Yanzu miye abin yi akan al'amarin Ya Hafiz?" Tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki, haka ta mazayo ta juyo kaɗan tana kallon su idanu cike da kuka tace. "Wallahy ban san ya zan yi ba Husaina..." "To mu kira Alhaji Baba mana.." ******* Hannu ya kai a hankali ya toshe min bakina tare da ɗan mirginowa kaɗan murya a ƙasa sosai ya ce. "I will be fine,.." Shiru na yi na kwanta wanda ina jin zafin jikin sa a nawa amma dole na ƙyale tunda ya hanani. Yanda na kasa baccin shima haka ne a wurinsa domin ko kaɗan bai sassauta riƙon da ya yi mini ba tamkar wanda zai haɗiyeni haka muka kasance tsawon lokaci wanda sai misalin 4am ya mirginani kaɗan tare da jamin duvet a daddafe ya sauka daga kan gadon ya shige toilet tsawon lokaci sannan daga ƙarshe bayan ya ɗumama Jikinsa ya fito ɗaure da towel yaje ya shirya Sannan yazo a hankali ya tallafoni har duvet ɗin ya kaini toilet. Kallon fuskata ya yi wacce ta yi suntum tsabar yanda na sha kuka, ya ce. "I'm so sorry...Do you need mah help?" Saukar da idona na yi ƙasa a hankali ina mai share wasu sabbin hawayen da suka silalomin na girgiza masa kaina alamar a'a ba tare da na yi magana ba. A hankali ya taka ya fice waje zuciyarsa cike da tsantsar tausayina, tsoro yake ya tsaya nace masa ya yi laifi, gudun hakan yasa ya fice ya bar ni ni ɗaya. Na daɗe a toilet ɗin wanda sai da na ji na ɗan dawo hayyacina bayan na gama gasa kaina sannan na yi wanka na fito. Sosai abin da ya faru a tsakaninmu ya tsaya mini a raina...Wai Yaya Muhammad ne ya tara dani! Tarayyar aure tsakanin mata da miji...Dama wannan shi ne First night ɗin da yake ta yawo da yamaɗiɗi a bakin mutanen duniya? Tabbas na tabbatar kuma na gasgata domin ya bar min tarihin da har abada ba zai goge a ƙwaƙwalwata ba. Lumshe idanuna na yi tare da kai hannu ina shafa jikina ina jin komai kamar yanzu ne yake faruwa tsakanina da datijjon Mijina. Ajiyar zuciya na sauke daga ƙarshe sannan a hankali na matsa na ja towel na ɗaura na fito. Bakin ƙofar na tarar da shi ya jingina jikin sa tare da tallafe hannayensa a ƙirjinsa. Ɗan ja baya na yi kaɗan tare da noƙe kaina domin ban tsammace sa a wurin ba. Yana ganin na fito ya matsoni tare da riƙo hannuna cike da nuna kulawa, ya ce. "How are you feeling now?" Shiru na yi tare da ɗora kaina a ƙirjinsa jin wata irin kunyar sa da ta dawo mini sabuwa. "ki yi haƙuri kinji...ko kaɗan ban da nufin cutarwa a gare ki....." Murmushi da kuka ne suka zo min lokaci ɗaya jin yanda ya ruɗe yana ta wani lallashina kamar wanda ya aikata min wani babban laifi. Ɗago kaina na yi da koɗaɗɗun idanuna a hankali na kalle sa a natse muryata a ƙasa sosaina ce. " Jikinka fa har yanzu da zafi..." Share maganata ya yi tare da kai hannu ƙarƙashin cinyata a hankali yana mai zame towel ɗin zai tura hannun nasa a HQ ɗina yana faɗin. "Da zafi ne har yanzu?" Tashin service!...ai a mugun gigice na kai hannu jiki na rawa na riƙe hannun sa tare da girgiza masa kaina idona a rufe na ce. "Wayyo ni! wallahy...ni dai dan Allah ka daina.." Ganin yanda duk na rikice yasa ya janye hannun sa yana murmushi ya ce. "I'm sorry....Ya jikin to?" Idona a rufe sosai still ina riƙe da hannun nasa na girgiza kaina na ce. "Ni dai lafiya ƙalau...." "Au! Da gaske...! To bari mu kom...." Ba shiri na ƙanƙamesa tamkar zan shiɗe ina faɗin. "Dan Allah kayi haƙuri...wallahy wurin zafin sosai..." Ɗagani ya yi kai tsaye ya bar ɗakin dani. Tafiyar kusan 3mnt sai gamu a wata duniyar wacce tsawon zamana a gidan ban taɓa sani da zaman ta ba. Wuri ne na musamman wanda zan ce duk kyaun gidan nan nan ɗin yafi ko'ina tsaruwa da kuma jin kayayyakin komai na more rayuwa. A bakin wani tamfatsetsen gadon ya ajiyeni sannan ya ɗauko wani ƙaramin towel ya tsane mini gashin kaina kamar yanda yaga ina yi sai dai kuma bai zo da hand dryer ba, bayan ya gama tsane ruwan a haka ya bar sa sannan ya ɗauko cream ya shafa mini yana murmushi ya juya ya fice. Duk tsawon lokacin nan da muka shafe babu wanda yayi wa wani magana ta fatar baki amma kuma saƙon da yake Isar min yana isa yanda ya kamata domin wata irin soyayyarsa ce sabuwa nake Jinta tana ƙara huda sassa da ruhin jikina,sam na kasa daina gani da jin abinda ya wakana a tsakaninmu a ido da ƙwaƙwalwata amma kuma gabaɗaya haushinsa da naji ina ji na nemesa na rasa. Kitchen ɗinda ke cikin keɓantaccen wurin ya shiga ya haɗo min Tea da kansa ya kawo min nasha sannan ya bani magani, bayan na shanye ya ja ni zuwa jikin sa muka kwanta akan gadon wanda bai fi 10mnt ba ya sauka ya shirya ya fice masallaci. Koda ya dawo ni har na yi sallah na koma na kwanta bacci ya kwashe ni. Ganina sanye da Hijabi shi ya tabbatar masa da cewa na yi sallah. Hauro wa ya yi a hankali cikin sanɗa ya janyoni jikinsa gudun kada na tashi yaja mana duvet. Kallon fuskata yake yana jin wani abu na ƙara fisgarsa a zuciya game dani...ji yake tamkar ya tsaga ƙirjinsa gida biyu ya ɗauke ni ya jefa a ciki tsabar yanda yake jina a yau. Ƙara matso da fuskarsa yayi a hankali yayi kissing saman goshina sannan ya ɗora hannunsa akan gashin kaina a hankali yana shafawa yana addu'a a ransa yana faɗin. 'wannan matar tawa...Allah ya bulbula miki albarka..Allah ya barni dake har mutuwa...Allah ya dauwamar da farin ciki a zuciyarki har abada...Allah ya bani ikon kulawa da ke da dukkan ƙarfina da dukiyata. Haƙiƙa kin bani farin ciki...farin cikin da har na koma ga Allah ba zan daina gode miki da kuma yaba miki ba. A yau na roƙi Allah alkairai masu yawa a tsakaninmu Bibi...Allah ya tabbatar mana da su ya bamu zuria ɗayyaba.' Haka ya shafe tsawon lokaci yana aikin yaba mini da gode mini a zuciyarsa wanda Sam bacci bai yi nasarar kawo masa farmaki ba. Muna nan a haka har misalin takwas na safe wanda har yanzu baccina nake hankali kwance ya ji ƙarar saƙo ya shigo wayarsa. Hannu ya miƙa ya ɗauko ya karanta sannan ya zamar dani gefe a hankali tare da ƙara gyara mini lulluɓi ya sauko ya zura jalabiya ya fita. Yana shigowa main parlourn gidan suka yi ido biyu da Labiba,waigawa ya yi ya kalli Emraan, Nadeeyah, Hairiyyah da kuma Baba Ustaz. Wani irin harbawa ya ji ƙirjinsa ya yi lokaci guda. Kafin yayi wani yunƙuri da gudu Labiba ta zo ta Rungumesa sosai ta fashe da kuka ta ce. "DADDY!!!" Cikin wani irin jin azabar kewar ƙannen nasa ya ƙanƙemata tare da jin wasu irin zafafan hawaye ya ce. "I'm sorry my PEACE.....I'm so sorry..Abubuwa sun juye mana yanda bamu tsamma ta ba....dole ce tasa na yi nisa da ku...amma dan Allah ku yafe min..." Tana kukan ta Ɗago kanta ta kalle shi ta ce. "Ka yi haƙuri Yaya..mun azabtu da rashinka, wallahi bana iya baccin kirki tun daga ranar da kasa ƙafa ka barmu har zuwa yau, wayarka bata shiga, ka hana kowa na kusa da kai ya mu'amalancemu. Hajiya tabbas ita ce wacce ta haifemu,.... Amma Sam babu adalci idan har ka saka mu a tsakiyar wannan abun da ya faru domin yanda ka tsinci abin muma haka muka tsince sa daga sama... Yaya ba kuɗin ka muke da buƙata KAI....kai ne ubanmu wanda yake tsaya mana a dukkan komai....nisantarmu da ka yi yasa mun zamto marayun ƙarfi da yaji Yaya...kuɗi ba su ne farin ciki ba wani lokacin, kyakkyawar alaƙar zumunci tafi komai muhimmanci..." Hannayensa ya ware yana kallon su Hairi alamar suma su zo wurin Yayansu. Da gudu suka shige jikinsa tare da haɗe kai suka yi ta rusa kuka son ran su shi kuma yana ta aikin lallashi da amsa laifinsa yana ta basu hak'uri, musamman irin kukan da ya ji Hairi nayi ya ɗaga masa hankali. Bayan sun natsa da koke-koken ne suka wuce part ɗin Hajiyarsu inda take sauka idan ta zo ƙasar suka zauna. Emraan sai wani noƙewa yake alamar jin kunya wanda shi Mohaan sam bai kawo hakan ba. Sosai yanzu yake jin rashin kyautawa akan ba su baya da yay na tsawon lokaci. Allah ne fa gatan su shi ne gatan su...amma miyasa zai biyewa zuciya haka har ta kai shi ga saka Masoyan ƙannensa a damuwa. Matsayin Hajiyarsu daban suma matsayinsu daban. "Emraan....are you still mad at me?" Ya faɗa yana mai jifar Emraan ɗin da wani irin marayan kallo. Da sauri Emraan ya Girgiza Kansa cike da jin nauyi ya ce. "Ba haka bane Yaya..." "Please kada ka damu kaji ko... Komai ya wuce in sha Allah. Daman ko tsakanin harshe da haƙori da suka fi kowa kusanci da zumunci ana samun saɓani ballantana mu 'ƴan Adam..." Daga haka ya mayar da kallonsa gun Baba Ustaz a natse ya ce. "Baba...A farko na ɗauki abin da ya faru dani da zafi sosai wanda har na ji a raina cewa bana buƙatar kowa daga cikinku wanda a ganina tare kuka haɗai kai kuke nema kuga bayana...to amma bayan na zauna na yi nazari, a yanzu na riga na fahimta cewa yana daga cikin ƙaddara ta wanda ban isa na gogewa kaina ba. Saboda haka ni komai ya wuce a gare ni musamman da Allah ya bani Mata ta gari wacce ta zamto haske a cikin rayuwa ta..... A yanzu ni tambayata ɗaya ce a wurin ka...Wace ce mahaifiyata? A ina take? Ina kuma Ahlinta suke?" Ajiyar zuciya Baba Ustaz ya sauke a hankali yana mai jinjina kansa ya ce. " Sunanta RANIA MUSDHAPA SAMI...a zuwa tafiyar kasuwanci mahaifin ka ya haɗu da ita a OUMDURMAN da ke ƙasar SUDAN......" ✍️

Chapter 37 of 67