15 anniversary wanda muka yi a ɗakin Ka'aba mai tsarki. Shi ne wanda ya kawo tsarin kuma muka tafi baki ɗayanmu muka yi ibada tare da yin addu'o'i...wallahy ji nake tamkar yanzu ne yake furta waɗannan zantukan a gare ni cewa.
" Bibi...ko a haka na mutu Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! Na samu mata ta gari, na samu 'ƴa'ƴa na gari, na samu dangi masu so na waɗanda suka tsaya dani a kowane irin yanayi. Rayuwa ta yi mini komai..."
Jinjina kaina na yi ina share hawayena tare da kawar da tunanin ina mai jin wani irin ɗaci na ce.
" Allah ya gafarta maka yasa ka a Aljanna maɗaukakiya, Allah ya bamu haƙuri da juriyar rashin ka, Allah ya shiryar maka da zuriyarka ya sa su zamto masu jinƙai da addu'a a gareka. Na yi alƙawari ba zan ƙara kuka ba, amma ka sani zuciyata za ta mutu da kewarka da kuma ci gaba da begenka har zuwa numfashina na ƙarshe..."
Hannunta ta kai a hankali tana bubbuga bayana tare da ƙara bani kalaman lallami da kwantar da hankali.
Da haka ta samu ta lallaɓani na ɗan ci abinci na yi sallah sannan muka fito inda na tarar Zarah tana kwance jikin Sis Nourah wai jikinta ya yi zafi tana jin zazzaɓi.
Wuri na samu na zauna ina mai saukar da kaina a ƙasa tare da share hawayena ganin yanda Hairiyyah ta yi wani iri duk ta zabge ta fi ce hayyacinta.
Mutane ne ta kowane ɓangare suke zuwa mana gaisuwa wadanda mafi yawa da cikinsu ni ban ma san su ba.
Shi ma Aliyu yana nan maƙale dani a duk inda nake, Su Aryaan ne ke can waje inda iyayen na su maza suke har aka kambala zaman makokin a hankali kowa ya shiga watsewa.
********
Bayan watanni shi da sun shuɗe, haka na ci gaba da ganin mutuwar mijina wasa. Ji nake kamar zai dawo, ji nake kamar komai wasa ne, amma kuma idan har ina son gaskiya...to fa ya tafi har abada ba zai dawo ba. Na yarda duniya ba ta tabbas, babu abin da yake ɗorewa da ci gaba da wanzuwa sai Allah maɗaukakin sarki, shi ne wanda bai haifa ba kuma ba'a haife sa ba. Da yardarsa da amincewarsa komai na duniya yake tafiya.
Shekaru ashirin sai suka zamo mini tamkar kwana ashirin bayan na tabbatar na rasa shi har abada. Na amince da shi ba tare da na taɓa ganin fuskar sa ba. Na so shi so mai tsanani a lokacin da zuciya da ruhi suka amince da shi a matsayin masoyi wanda ya cancanta kamar yanda shi ma ya ɗauke ni. Mun gina rayuwa mai inganci da tarin albarkoki da alkairai waɗanda ba zan taɓa mantawa da su ba.
Kuɗi ko mulki ko sarauta ko talauci babu wanda zai hana maka mutuwa idan lokacin ka ya yi. Da ciwo da babu ciwo idan lokacin ka ya yi sai ka tafi. Da ace lafiya ko kuɗi ne ko wani jindadi zai hana mutuwa, tabbas da Dayaa na bai mutu ba. Domin yana yawan zuwa check up kuma baya yawan rashin lafiya domin sai ya shekara bai yi ciwon kai ba. Amma da yake mutuwa duk bata duba wannan. Sai gashi ta ɗauke shi ta barni da kewa.
Tun last week Ammie ta zo akan cewa tana so ta ji mi na yanke dangane da rayuwa. Ni dai ban ce mata komai ba, domin akwai abubuwan da nake hangowa da haskowa a cikin rayuwar 'ƴa' ƴana.
Yau ma tunda na wayi gari ina kwance a ɗakin sa na kasa tashi ma ko wanka na yi. Ko breakfast ban yi ba.
Hakan yasa Abdallah ya ƙara shigowa ɗakin ya same ni bayan ya nemi izinina ya zauna yana faɗin.
"Grandma ta shigo tana parlourn ki Maami. Yau har yanzu ko breakfast ba ki yi ba. Dan Allah ki daure ki tashi..."
Kallonsa na yi sai kuma na duba agogo ina faɗin.
"Miyasa ka ke gida har yanzu baka fita school ba?"
"Na gayawa driver na cewa ba zan fita school ba tun jiya. Saboda yanayin ki yayi kamar bakya jin daɗi. You are just hiding it Maami....Su Ya Aryaan ma suna duba abinci suka tambayi Miss Mairah ta tabbatar musu cewa baki fito ba kawai suka fice ba tare da sun ci abincin ba...ki na ji ko Maami...yanayin ki is killing us,we are not happy a yanda kike. Ke ce ƙwarin gwiwarmu kuma dogaronmu. Mun rasa Daddy...idan muka rasa ƙarfin gwiwarki zamu susuce rayuwarmu ta samu tangarɗa."
" Zarah fa? Mairah ɗin ta gama shirya mata?"
Na tambaye shi, domin na yi ƙoƙarin kawar da zancen duk da cewa na san gaskiya yake faɗamin.
" Eh, tare suka fita da su Ya Arhaam ɗin, sun ce sune za su ajiye su school ɗin."
Miƙewa na yi na zauna a hankali ina mai share hawayena na jinjina masa kaina ina murmushi na ce.
" Abdallah! Ku yi haƙuri, ni ɗin tabbas na kasance mai tsananin son kai na, damuwata kawai nake dubawa, amma daga yau na yi alƙawari...zan yi iya yina."
Hannuna ya riƙa har bakin toilet yace.
"Ki yi wanka ki shirya kin ji Maami, ni zan je na haɗa miki wani abin karin da kaina. Grand Ma tana jiran ki."
Murmushi na yi tare da jinjina masa kaina ba tare da na yi magana.
Bayan na yi wankan na kambala na fito na shirya sannan na fito inda Ammie ɗin na gaishe ta sannan muka gaisa da Bahrain wanda ya iso ƙasar jiya da dare.
Kallona Ammie ta yi ta kira sunana a hankali ta ce.
"Beenafah!"
Ɗagowa na yi na kalle ta tare da amsa mata sannan ta ce.
"ina ta magana tunda na zo ba ki ce komai ba."
Jinjina kai Bahrain ya yi idonsa a kaina cike da kulawa ya ce.
"Aunty Beena...Life won't continue like this. Dole ki farka ko don goben yaran nan..."
Jinjina kaina na yi ina share hawaye na ce.
"Daman na yanke wata shawara ne. A lokacin da ƙaddara ta haɗamu da Ya Mohaa, a Nigeria rayuwarmu ta fara, sai muka koma Dubai, wanda bamu taɓa kawo ƙaddarar zama a Oumdurman ba. Sai gashi ta kasance gidansa na ƙarshe. Ta dalilin sa ne muka zo nan ɗin, to abunda na yi tunani, idan na ci gaba da zama a nan, zan ci gaba da karyewa ne har abada. Zamu koma UAE tare da su su ci gaba da karatunsu ni kuma na ci gaba da kulawa da su. Akwai abubuwa da dama da yasa na zaɓi na koma can da zama, sannan a tsohon gidanmu zamu zauna inda muka fara rayuwa..."
Murmushi Ammie ta yi tana mai jinjina kanta ta ce.
" Ba komai Beenafah, tunani ne mai kyau, Allah ubangiji ya ci gaba da jiɓantar lamarin rayuwarku damu baki ɗaya. Allah ya ƙara miki haƙuri da juriya ya baki ikon kulawa da Amanar waɗan nan yaran."
"Amin Ammie, na gode sosai."
Ɗan ƙara tattaunawa muka yi sannan daga ƙarshe ta kirasu Uncle Mu'aƙƙib ta sanar musu wanda ta ce ita ce ta kawo wannan shawarar da take tunanin kamar za ta kawo sauyi a cikin rayuwata. Cikin ikon Allah dai gashi kowa ya goyi baya hakan yasa muka shirya cikin wata ɗaya muka koma UAE inda tarihin rayuwarmu ya soma.
Alhamdulillah! Komawarmu sai in ce ta ƙara haske sosai a cikin rayuwata. Domin na ɗan saki raina duk da a gidan komai yana mini watarana kamar zan ga Dayaa na a ciki. Abubuwa da dama idan na tuna sai dai in shige ɗaki na kulle kai na na yi kukana ba tare da sun sani ba. Yarana sun kasance abun alfaharina, domin sun tsaya sosai wurin bani haɗin kai wurin gudanar da rayuwar tamu bisa tsari. Musamman su Aryaan da suka tsaya akan ƙannensu da basu kulawa yanda ya kamata. Sannan Emraan da Suhaib ma sun tsaya sosai a kansu musamman Emraan wanda ya tsaya kai da fata tamkar 'ƴa'ƴansa na cikinsa. Hakan sai ya ƙara kwantar mini da hankalina sosai Alhamdulillah.
Haka rayuwa ta ci gaba da tafiyar damu a kwana a tashi har su Aryaan ɗin suka kambala Degree ɗin su yayin da Abdallah ya wuce Jami'ar Madina domin karantar fannin larabci kamar yanda ya yi buri da shi da mahaifinsa. Daman shi ɗin rayuwarsa tun tashin sa ya taso ne da son gefen addini wanda a nan rayuwarsa tafi karkata. Tun a shekaru goma ya sauke alƙur'ani sannan yana da sha biyar muka yi masa walimar haddacewa wanda har abada ba zan manta wannan ranar ba, domin Daddynsu yayi matuƙar farin ciki har da kukansa akan yanda abun ya faranta masa rai. Shiyasa bamu hana sa akan abinda yake so ba. Kuma In sha Allahu, a hankali wannan kudurin nasa zai cika.
A shekarar da suka kambala karatunsu, a shekarar na samu Ammie muka tattauna tare da su Emraan akan zancen auren su Aryaan kamar yanda muka tsara. Bayan mun kai ƙarshe ne aka saka rana da lokaci inda Aryaan aka tabbatar da maganar sa da Siyama er Hairiyyah kamar yanda ya zaɓa sannan Arhaam da kuma 'ƴar gidan Raihab da Aunty Husaina wato Amal.
*******
Shiri muka shi ga yi na musamman wanda ta kowane ɓangaren sun ɗauki bukin da muhimmanci, kuma a nan muka yanke za'a yi domin a Oumdurman ma Jadda ta shekara biyu da rasuwa, hakan yasa muka yanke kawai a yi sa a nan ɗin.
Ana saura wata ɗaya Aunty Labiba suka iso da Aunty Nadeeyah domin kawai su kasance a tare dani wanda ba ƙaramin farin ciki ya bani ba.
Ina Zaune ina Gyarawa Zarah kanta wacce a yanzu itama ta fara zamowa Budurwa Aunty Labiba ta shigo.
Kallonta na yi ina murmushi na ce.
"Aunty Labiba kun ji ni shiru ko? Zarah ce ta sakani a gaba..."
"Ba komai ai, daman wata magana ce ke tafe dani."
Kallon Zarahr na yi na ce mata ta bamu wuri sannan na mayarda hankalina ina kallonta sosai na ce.
"Mummy Na'Imatu kuwa za ta zo?"
"Eh, Sun ce sai zuwa nan da sati biyu za su zo."
"Okay! Allah ya kaimu."
"Amin. Daman Beenafah, zance ne dangane da rayuwarki...babu wanda zai tilasta miki, amma zama a haka kamar ya yi wani iri Beenafah. Dole kowa yasan cewa kin yi rashi, amma rayuwa ba za ta ci gaba da a haka ba....ina neman afuwarki idan har maganata ta ɓata miki. Amma Emraan yace yana neman alfarma idan har zai yi yu, yana so zai aure ki...muma haka ɗin idan har ya kasance, to tabbas zamu fi kowa farin ciki, domin mun riga mun zamto ɗaya, idan har kina da buƙatar wani a rayuwarki, to tabbas Emraan ne yafi cancanta. Ya kamata ki ɗaura aure Beenafah ko don yaran nan.."
Wasu irin hawaye ne suka wanke mini fuska masu matuƙar ƙuna da zafi. Tabbas ba ita ce ta farko wacce ta fara mini wannan maganar ba. Ammie ta yi ta bina da zancen wanda har ta ga ji ta zuba mini ido.
Kallonta na yi ina mai jinjina kaina na ce.
" Na gode sosai da kulawa Aunty Labiba. Amma ki yi hak'uri ko Ince ki ce masa ya yi haƙuri. Na riga na gama aure a duniya. Babu wani namijin da yake burgeni, babu wani namijin da zai iya bani farin ciki kamar yanda mijina yake yi. Sai yanxu na fahimci ciwo da tsananin ƙuncinda ya kasance a cikin rayuwar Noura a wancan lokaci. Rasa miji babban ƙalubale ne a rayuwa..."
Cike da tausasawa ta ce.
"But at the end ta ɗauki shawara tayi haƙuri tayi auren, kuma ta yi farin ciki Beenafah..."
Girgiza kaina na yi tare da lumshe idanuna wasu irin zafafan hawaye suka sake sulalo mini na ce.
"I'm sorry Aunty Labiba...amma na riga na gama aure a duniyar nan. Har abada ba zan iya auren Emraan ba."
Ita da ta kawo shawarar...ƙarshe ita ce ta ɓige wurin lallashi da bani haƙuri har sai da na ji ƙuncin da ke zuciyata ya ɗan ragu.
Na san cewa Emraan tsayayye ne ga komai namu, duk wani abun da uwa da Uba za su yi wa 'ƴa'ƴansu, to tare da shi muke gabatar da shi, ko Walimar saukar Zarah wacce ita kaɗai ce Mahaifinsu Allah bai nufe shi da ganin wannan ranar ba, tare da shi muka halarta. Ko Abdallah da zai je Madinah, tare muka tafi gabaɗayanmu har Emraan ɗin wanda idan ba ka tambaya ba ba za ka ce ba shi ne mahaifinsu ba da gaske. Duk da cewa matsayin Uba daban ne a rayuwa, ba su taɓa neman wani abu da sunan mahaifi sun rasa ba, saboda ya tsaya a kansu bisa gaskiya da adalci wanda ba ya iya bambanta su da su Abeer.
******
Wannan hidimar ta tara mini mutanen da ban za ta ba ban kuma yi tsammani ba. Ko gefen Dr. Basheer kaɗai Su Mama Asma'u da su Mummy Sameera sun nuna mini karamcin da ba zan taɓa mantawa da shi ba.
Su Yaya Hafiz suma sun zo gabaɗayansu har Yaya Ahlan mijin Aunty Aysha.
Su ma Maman Fakiha da Baba sun zo har da Barrister Jafar wanda ni tun da suka iso har yanzu ban sanya shi a ido na ba.
Hidima muka shiga yi sosai, inda a nan muke shagalin Su Aryaan ɗin, da kuma gidan Suhaib sai kuma Qatar gidan Raihab wanda a can su Annie suka tsaya har sai da aka kammala ɗaura aure sannan suka iso da Amarya.
Koda aka shigo da su aka ajiye su a gabana tare da su Aryaan ɗin. Kuka nake sosai ina mamaki da al'ajabi wai ni ce yau nake da yara maza da suka yi aure? Ni Beenafah! Allah mai iko da rahama. Ga shi yau wannan ranar ta zo, amma babu Daddyn Abdallah. Ina ma ace yana duniyar? Ina ma ace yana nan zaune a gefena wannan burun na shi ya cika? Haƙiƙa mun rayu, kuma mun yi farin ciki ga albarkar 'ƴa' ƴa Alhamdulillah! Amma duk haka...har yau na kasa sabawa. Dariyar da yanda ya nuna tsantsar farin cikin da nake ji da gani a kunnuwana da idunawana a lokacin da Arhaam ya ce shi zai yi aure a 25yrs ɗin shi. Kamar zai ga wannan ranar da gaske, har ya fara tunani ya fara tsare-tsare, ko a jirgi lokacin da za mu yi tafiyar ƙarshe zuwa Nigeria babu zancen da yake idan ba na auren na su ba. Ya ce zai zan yi gayyata Bibi...zan gayyaci mutane da yawa, wanda duk kuma bai zo auren Mazaje na ni da shi mun datse alaƙa har abada...dariya muka yi dukkanmu. Har Aryaan ya ce, Daddy wannan kalmar Bibin tun muna jin kunyar ta har mun saba da ita. Tun ba mu san mi take nufi ba, har muka fara wayon sani, ga shi mun girma amma kaƙi ka daina ta. Yana jin Aryaan ya dire ya kamo hannuna ya haɗe a cikin nasa yana kallon su yana murmushi ya ce, Cancancacciyar kalma ce da ta cancanci nagartaciyyar Mace kamar Mahaifiyar su. Ita ɗin ta kasance ta musamman kamar yanda na saba faɗa muku, ban san wata kalma da zan kira ta da ita wacce ke bani farin ciki ba Fiye da wannan Kalmar..idan kuma ka ji an daina ambatonta...to ka ƙaddara bana duniyar.
A hankali Aryaan ya ɗaura kansa akan ƙafata, muryar nan cike da nuna zallar karaya ya ce.
"Maami! Daddy kike tunawa ba? Muma ɗin shi ne muke tunawa da irin ɗokin da ya nuna da zuwan wannan ranar...."
Hawayena na share ina mai yin wani irin murmushi na dafa kansu sannan na ce.
"Haka Allah ya nufa, cewa Daddynku ba zai ga wannan ranar ba. Alhamdulillah! Ina farin ciki, domin na cika masa wannan burin nasa, an ɗaura muku auren a ranar da kuka cika shekaru ashirin da biyar a duniyar. Ina muku fatan alheri da fatan zaman lafiya da farin ciki na har abada. Siyama...Amal..dukkan ku 'ƴa'ƴa na ne kuma jinina. Allah ya zaunar da ku lafiya ya baku zuriya ɗayyaba. "
Nan ɗakin ya ɗauka da Amin sannan aka fita da su zuwa gidanje su wanda muke fata su rayu rayuwa ta har abada.
Ina tsaye jikin windown bedroom ɗinsa ina kallon waje, zuciyata cike da marari da kewa na ji an turo ƙofar an shigo. Waigowa na yi sai naga Aryaan ne da Arhaam. Saurin share hawayena na yi ina mai ƙirƙirar wani murmushin na kalle su da alamun nuna mamaki na ce.
"Lafiya kuka dawo?"
A hankali suka tako a tare kowa ya ɗaura kansa a gefen kafaɗata suna faɗin.
"We love you Mammi....thank you for being a good mother to us. Kin tarbiyyantar damu da ke da Daddy, kun bamu farin cikin rayuwa, kun tsaya mana akan cika duk wasu mafarkai na mu, wanda a yau sun juye sun zama gaskiya. Muna alfahari dake, Allah ubangiji ya ji ƙan Daddy ya gafarta masa, ya ƙara jaddada rahamarsa a gare sa ya ƙara yalwata makwancinsa, Allah yasa ki gama da duniya lafiya yasa ki yi kyakkyawan ƙarshe."
Jinjina kaina na yi na ce.
" Amin ya Allah."
Daga nan na ɗago su tare da kama hannun su na koma jikin Window ina kallon waje na ce.
" Kun san ta ya muka fara da mahaifinku? We were met as a strangers, a hankali sai muka fara sabawa da juna, yakan mayar da damuwa ta ta zamto ta shi a kowane irin yanayi, yakan ɗauki farin cikina a matsayin na shi da dukkan al'amura na. Bai taɓa sa na ji cewa na yi taɓa nadamar auren sa ba, kamar yanda shi ma bai taɓa riskar nan wannan lokacin ba a rayuwarsa. Haƙiƙa mun so juna so na domin Allah ba don wani kyawu ko ƙyalƙyalin duniya ba. Mun so juna, mun kuma girmama juna, ya girmama Iyayena da en uwana kamar ya basu muhimmanci sosai kamar yanda ni ma na girmama na sa. Saboda haka, ina muku nasiha da ku ji tsoron Allah, ku daraja auren ku, ku yi rayuwar aure bisa gaskiya da adalci. Ku kula da wannan amanar, kun yi aure a cikin ƙurciya sosai, ina fata da addu'a da kuma roƙon ku akan cewa kada ku zamto masu hange-hange, rayuwar aure duk wanda ya gina ta fata yake ta ɗore har mutuwa. Kada ƙurciya ta ɗebeku ku riƙa tunanin aure-aure. Don Allah ku riƙe amanar en uwanku ku zauna da su tsakaninku da Allah. "
" In Sha Allahu Maami,mun ji duk abin da kika faɗa mana kuma zamu yi aiki da shi gwargwadon iko...."
Jinjina kaina na yi na ce.
"Allah yasa...Kuje, sai da safe. Allah ya bamu alheri."
*******
Wata ɗaya da auren na su aka shirya bukin ƙaddamar da su a matsayin sababbin shugaban nin Golden Pathways kamar yanda Emraan ya tsara, domin sun kawo girman da ya ga cancantar hakan, sannan daman mafarkin Daddynsu kenan da abun da ya tsara matuƙar abubuwa sun tafi daidai.
Bayan sun zamto jagorori muka shirya bayan watanni shi da muka tafi Sokoto wurin auren Kausar wacce zata auri wani matashin likita wanda ke zaune a nan cikin sokoto.
Koda muka isa an gama shirya komai har an shiga hidimar bukin. Muna ɗaki muna tattauna zancen kuɗaɗen da za'a sa yi kayan gara dasu na kalli Ammie na ce.
"Wai dai Ammie shi ke nan kika hanawa Armaan Kausar da gaske?"
Dariya tayi ta ce.
"Bana so ne ta yi nisa dani Beenafah. Sannan Abbun ku ma haka, shi ma ya nuna rashin amincewarsa ya ce ya fi so tana a kusa da shi."
"To Allah yasa albarka yasa ace gwamma da akayi."
"To amin."
Daga haka ta samu wuri ta zauna sannan ta nuna mini gefenta ta ce na zauna. Ina jin ta kira a tausashe na san cewa maganar dai ce kamar kullum.
"Beenafah, kamar yanda na saba faɗa miki, zaman ki a haka sam baya mini daɗi. Beenafah idan kina zaune ke ɗaya, damuwa da tunanina ba za su taɓa barin ki ki zauna lafiya ba. Beenafah aure shi ne cikon kamalar Mace. Ki yi haƙuri ki yi auren nan ko don yaran ki musamman Zarah. Beenafah kada ki manta, na auri Dr. Basheer ne don kawai saboda ke a lokacin. Ke ce dalili domin kawai na ga cewa na cika miki burin ki na son auren mutumin da kika zaɓa. To miyasa ke ma ba za ki jaraba hakan ki gani ba? Na san cewa zuciyarki mijinki kawai take tunani,to amma ki hasko goben yaran ki, har kin aurar da su Aryaan, amma su kan su sun same ni akan cewa suna so ki yi aure, domin zaman ki ke ɗaya yana ƙara miki damuwa..."
Hawayena na share ina kallonta na ce.
" Ammie ba zan iya auren Emraan ba...dalilai da yawa sun sa ba zan iya auren Emraan ba Ammie...and su ma sauran mutanen da suke nuna suna so na ba zan iya ba Ammie ba.."
Hannunta ta ɗora akan kafadata ta ce.
" Beenafah kina ji na? Jafaru yana nan, Jafaru ya kasa aure saboda rasa ki da ya yi, ba komai bane yasa ya aikata duk abin da ya aikata kawai tsabar son da yake miki ne. Ki tausaye shi Beenafah ki ba shi dama dan Allah ko zai samu farin ciki kafin mutuwar sa ta riske shi. Wani lokacin halin da zuciya ke shiga ne yake sa tana aikata ayyukan da ba su kamata ba, amma shi ɗin kin fi kowa sanin cewa mutumin kirki ne. Dan Allah Beenafah ki daure ki ba zuciyar ki magana. Beenafah yanda Jafaru ya ƙare babu wata uwa ko uba mai burin ganin ɗansa a wannan halin, ki daure ko don darajar iyayensa da zumuncin da ke tsakaninmu ki amince ki aure sa."
Jinjina kai na nayi ina mai jin wani irin nauyi a ƙirjina na ce.
" Shi kenan Ammie...idan har hakan shi zai sa ki yi farin ciki zan yi.."
Murmushine ya suɓuce mata jin amsar da ba ta yi tsammaninta ba daga bakina. Hakan yasa ta miƙe cike da farin ciki ta ce.
"Na gode Beenafah. Allah ya yi miki albarka ya ƙara miki kwanciyar hankali da farin ciki mai ɗorewa. In Sha Allahu ana gama ɗaura auren Kausar gobe sai mu tattauna ke ma sai ku tattauna da shi domin ku tsayar da abun da ya dace."
Daga haka ta fice ta barni nan ina mai kwanciya akan gadon na fashe da kuka.
*******
Barrister Jafar kuwa, tun auren su Aryaan bai ƙara yin ido biyu da Ashiru ba sai yau da ta kasance ranar ɗaura auren Kausar wanda suka jima suna tattaunawa.
Jiki sanyaye ya kalli Ashirun ya ce.
"Ko a lokacin auren 'ƴa' ƴanta...na kasa haɗa ido da ita. Ina jin kunyar ta na abin da na aikata mata a lokacin. Amma har yanzu ina son ta..."
Wani murmushin Alhaji Ashirun ya yi sannan ya kalle shi ya ce.
"You made a big mistake Barrister. Tabbas ka aikata kuskure. Wato kasan wani abu? Idan mace ta nuna so akan wani wanda ba kai ba, matuƙar dai kana sonta da gaske kuma kana son farin cikin ta, to lallai ka nuna kana son wanda take so ɗin nan fiye da yanda ma take son shi, sai Kaga an zauna lafiya. A lokacin da na ga hotunansu na a lokacin da aka haifi su Aryaan,...sai a lokacin na gane, na kuma tabbatar da cewa shi ne wanda ya kaɗe mahaifiyarta ya kuma yi tafiyarsa. Sun riga sun yi aure har sun haihu,babu amfanin kawo abin da ba shi da amfani a wannan lokacin. Ta yi kuka, ta yi baƙin ciki ta kuma ci alwashi akan duk wanda ya kaɗe mata Ammienta. Sai daga baya na gan shi ya zo asibitin yana tambaya wanda ita a daren tana can wurin likitan da yake duba Ammienta. Ban san taƙamammen abin da yake tambaya ba domin ɓoyewa ma na yi don kada ya ganni, duk da cewa a rikice yake, na san cewa akwai wani abun da ke damunsa na daban a wannan lokacin, ina nan ina kallon sa ba jimawa ya juya ya wuce. Na gane motar kuma na gane shi, amma tun da har ta aure shi babu buƙatar sanar mata domin haɗa husuma tsakanin miji da mata abu ne wanda Allah
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 65 Chapter of 67