da manzonsa ba sa so kuma suka yi hani da shi. To ni na faɗa maka wannan ne domin in baka misali in kuma nuna maka cewa ka aikata kuskure na bibiyarta da kuma furta kalmomin cin zarafi akan Mijinta..."
Jinjina kansa ya yi sannan ya ce.
" Ai komai ya wuce Alhaji Ashiru, domin ko ni yanzu idan na tuna wallahy kunyar kai na nake ji. Allah yasa dai ta amince min."
"To amin."
Daga nan suka wuce wurin ɗaurin auren wanda aka ɗaura ƙarfe biyu na rana.
Ana nan ana ta hidima, Ina tsaye a ɗaki ina magana da Abdallah da ke shaidamin cewa gobe zai koma school na ji wayata ta yi ƙara, ina dubawa naga cewa Ammie ce ke kirana.
Ina ɗagawa ta ce na zo Parlourn Abbu na sama ina da baƙo Jafaru yana jirana a can.
Wani irin yawu ne ya wuce mini da ƙyar sannan na kalli Abdallahn na ce.
"Sai ka shirya ba damuwa, shi ma Aliyu zai bi su Arhaam su koma gida domin exams ɗinsa wannan satin ne, duk da na san cewa ya sanar maka.."
"Eh Maami, ya faɗamin ɗazu da safe."
"To kana da buƙatar kuɗi?"
Girgiza kansa ya yi yana mai mayarda kallon sa akan wayarsa ya ce.
"Nop! Ina da kuɗina, ko last week Daddy Emraan ya tura mini da 500k. And Ya Arhaam ma ya ce idan na sauka zai tura mini wasu."
"Ok to, ka je ka ci abinci dan Allah kafin na zo. Zan je naga wani baƙo a Parlourn Abbu, ka nemo Zarah ka ce ta jirani ina zuwa yanzu, tun ɗazu nake kiranta a waya ba ta ɗagawa."
Yana fita na ɗauko mayafina na lulluɓa na shiga ratsa mutane har na yi nasarar shige wa cikin Parlourn.
Zaune na cim masa ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya yana sanye cikin shiga ta manyan Kaya na alfarma.
Yanzu tsawon shekaru Ashirin da biyar kenan rabo na da nayi ido biyu da shi. Sosai ya canja a idona amma sam ban ji komai da ganinsa ba. Gyara zamansa ya yi yana mai yi mini murmushi ya ce.
"Hajiya Beenafah! Barka da wannan lokacin?"
Wani kallon na yi masa ina mai jin wani iri a raina na ce.
"Tsawon shekaru ashirin da biyar kenan..amma ko kaɗan ban ji tsana da ƙiyayyar da nake maka sun ragu a zuciyata ba. Komai da nake tunawa ina ganin ka yanzu sai yake min kamar yanzu ne yake faruwa. Kalaman ɓatancin da ka yi akan mijina sun kasa barin zuciyata. Tsananin fushi da ƙiyayyarka ne na gani kwance akan fuskarsa a ranar da ya kama ka a ƙofar gidansa. Jafaru har abada ba zan iya auren ka ba, saboda dalilai da dama..."
"Beenafah na kwashe tsayin shekarun rayuwa ta ba tare da na kula wata macen ba duk don saboda son ki da nake yi..."
"Kai ne ka ɗorawa kan ka, domin Allah bai ɗora maka ba. Wato kasan wani abu....rashin tawakallinka duk shi ne ya kai ka ga wannan Jafaru. Da ace ka yi haƙuri ka karɓi zaɓin Allah da ya rubuta cewa ni ɗin ba rabonka ba ce, da yanzu kana nan kana farin ciki kamar kowa. Amma dagewa da ka yi kace kai lallai sai ka yi fito na fito da ƙaddarar da Allah ya zaɓa maka, shi ne yasa ka ƙare a haka. Mijina ya nuna rashin jin daɗinsa akan bibiyata da ka dinga yi kana faɗin munanan kalamai akan sa, idan har a GANIN IDOn sa na juya maka baya da gaske, to mi zai sa bayan ƙasa ta rufe masa ido na dawo yin alaƙa da kai? Hakan ya nuna cewa na ci amanar sa kenan. Abun da ban yi a GANIN IDON sa ba, har abada ba zan aikata shi bayan shi ba. Ina son mijina sosai, nayi masa so da ƙaunar da ban yi wa wani ɗa namiji ba, kuma har abada ba zan yi ba. Mu ɗin a yanzu ba yara ba ne Jafaru...mun san abin da ya dace da wanda bai da ce ba..."
Wani irin abu ne ya ji mai matuƙar ciwo da raɗaɗin sai da yasa ya miƙe tsaye a zafafe, cikin tsananin kishi ya ce.
" Wai har yanzu ma da ya ji ma da mutuwa ba za ki daina wannan ba Beenafah? Ni fa ban aikata miki wani kuskure ba, kawai ni masoyin ki ne na Haƙiƙa. Ni ban taɓa cutar da ke ko mahaifiyar ki ba, amma shi wanda kike yiwa iƙirarin so idan ba ki sani ba, to shi ne nan wanda ya kaɗe miki mahaifiyarki da Mota har kika kusa rasa ta. Shi ne ya buge ta ya tafi ya barta..."
Wani irin tsalle zuciyata ta yi tsabar baƙin ciki wanda har ban san lokacin da na wanke masa fuska da mari ba ina mai jin yanda wata irin sabuwar tsanarsa ta shiga bijiro min ta kowane sassa na zuciyata.
Baki na na rawa na ce.
" Wai kai dan Allah wane irin mutum ne? To sai me? Sai me na ce don shi ne ya kaɗeta? Wannan mummunar maganar da ka faɗa mini a yanzu kana tunanin shi zai sa na ji tsanar sa ko me? To koma haka ɗin ne na yafe masa duniya da lahira, kuma Ammie ma ai ɗanta ne, kuma na san tabbas za ta yafe masa ita ma, na gode maka sosai da ka sanar da ni wannan, ko banza Kaga wannan nauyin idan har da gaske kake, to ya sauka daga kansa daga yau...Mamaki nake! Har da cewa ya mutu amma ba ka daina jin haushin sa ba. Kada ka bari 'ƴa' ƴansa su ji ka, domin ba za ku ƙarƙare da daɗi ba. Wallahy na tsane ka, tsana ta har abadan abada. Ko maza sun ƙare a duniya...ni ɗin ba zan taɓa auren mutum irin ka ba. Duk da cewa kayi shekaru...amma har yanzu har abada ƙwaƙwalwarka ba ta aiki yanda ya kamata. Ka tafi , kada ka sake dawowa inda nake na roƙe ka..."
Fitowa na yi na barosa a ɗakin, domin wallahy idan na ci gaba da ganinsa tabbas zuciyata bugawa za ta yi na mutu. Na tsane sa ta yanda ban san ma ya zan misalta shi ba.
Sosai na yi ƙoƙarin ɓoye damuwata, domin bana so na wargaza farin cikin mutanen da suka taru domin mu.
Hakan yasa na yi tamkar wani abu bai faru ba. Na koma muka ci gaba da hidimarmu.
Da dare bayan an fito da Kausar an sanya ta a motar Alhaji Hashi ne Na ji Bahrain ya riƙo hannuna yana faɗin.
"Aunty Beena please zo ki ji minti biyu dan Allah.."
Kallonsa na yi sai kuma na ce.
"Bahrain koma miye ka bari na kai Kausar na dawo..."
"Noo...Aunty Beena please, it's urgent. Just two minute as I said."
Tun da muka tako bamu tsaya ko'ina ba sai bakin ƙofar Parlourn waje yana mai kallona cike da magiya ya ce.
"Kin ƙi ki saurari kowa Aunty Beena ta...dan Allah ki daure ki saurari wannan ɗin...nobody will force you, but Idan hakan ta faru, zamu yi farin ciki."
Wani irin dokawa ƙirjina ya yi wanda ban san lokacin da na waro ido ina Kallonsa ba na ce.
"Bahrain miye yake faruwa?"
Cikin sigar magiya ya ce.
"Idan kika shiga za ki ga ko miye, Aunty Beena dan Allah ki shiga."
Tura ƙofar na yi a hankali ina mai jera addu'ar neman tsari daga Allah domin ban san waye Bahrain ke ta yi wa wannan magiyar haka ba.
Tsaye yake yana facing window ta waje wanda ko da bai juyo ba nasan kowane ne. Jikina ne ya ɗauki ɓari yayin da na ji zuciyata ta yi wani irin nauyi. Shekaru Ashirin da Shida kenan, rana ta ƙarshe a tsakaninmu ita ce ranar da kunnuwana suka yanke daga jin muryarsa bayan Emraan ya yi nasarar fasa min wayata. A wannan satin ne na yi masa ganin ƙarshe, ganin da ban ƙara sanya shi a ido na ba sai yau. Ko lokacin da Daddyn Abdallah ya rasu cewa ya yi Ammie ta isar mini da gaisuwarsa, auren Su Arhaam da ya zo ni har aka kambala ban gansa a idona ba. Taron gamayyar kamfanoninmu da muke ma, duk da cewa yana cikin manyan ma'aikatanmu bai taɓa halarta ba, matuƙar dai da ni a ciki. Sai dai ya kawo wasu Uzuroran ya shimfiɗa.
Waigowa ya yi a hankali yana mai kallon fuskata zuciyarsa cike da taraddadi wanda ya rasa ma a wanne yanayi yake ciki.
Sautin muryarsa na ji a hankali ta fara sauka a cikin kunnuwana da cewa.
"Beenafah... Dan Allah ki zauna ki saurareni, ba zan taɓa takura miki ba, ba zan ɗaga murya ba, dan Allah ki zauna, ki zauna ki bani mintuna kin ji."
Wuri na samu na zauna ina mai jin yanda hawaye suka cicciko idona wanda ban san dalilin hakan ba.
"Ahm! Da fatan kina lafiya...ya kike ya iyali ya kuma ƙarin haƙuri? Allah ya gafarta masa ya ƙara jaddada rahamarsa a gare shi."
"Amin yah Allah, na gode sosai."
"Wato wata er magana ce ke tafe dani, ina fata ban takura ki ba Beenafah?"
Jinjina kaina na yi camly na ce.
"Ba komai, you can go ahead.."
"Beenafah kin tuna lokacin da muka rabu na ƙarshe a rayuwa? Tabbas a wannan lokacin ban san miye abinda ya yanke maganar da muke yi a waya ba a wannan ranar. But bayan abubuwa sun kasance haka, sai na ɗauka cewa yana daga cikin ƙaddarata. Na so ki tun a wancan lokacin, so mai tsanani wanda yasa na gigice na ɗimauce Beenafah. Kalmomin da na tsara domin faɗa miki a wannan ranar ban yi nasara ba Beenafah. Domin na riga na makaro, sai dai kuma suna kwance a cikin ƙirjina tsawon shekarun nan, ni na yarda da cewa so ɗaya ne,kuma daga lokacin da kika so wani bayan ni sai na hak'ura na kuma ɓoye shi can ƙasan zuciyata domin babu wata macen da ta cancanci kalmomina Beenafah tun a ranar da aka shaidamin zancen auren ki. Na rayu da matata domin bin umarnin Iyayena, amma so ɗaya na ke yi...domin ki na ke yinsa kuma daga lokacin da kika yi aure, a lokacin soyayya ta mutu daga zuciyata. Bana so in yi kuskuren bayar da kalamaina ga macen da ba ita zuciyata take so ba."
Miƙewa ya yi ya dawo kusa dani kaɗan yana mai ƙara kwantar da muryarsa ƙasa sosai yace.
" Beenafah! Ban zo wurin ki don neman soyayya ba a yanxu, na zo ne saboda na san ina son ki, kuma zan furta kalmomin a gare ki wanda shi ne karo na farko bayan na rasa ki a baya, INA SON KI BEENAFAH. Wannam ita ce kalmar da na so furta miki a wannan ranar. Ba lallai sai kin amsani ba, domin nasan cewa tabbas na makara. wanda ya yi nasarar auren ki, shi ne ya cancance su saboda ya kasance jajirtaccen miji na gari kuma uba na gari. Ina so don Allah ki amince ki aureni ko da ba ki jin komai a ranki na So gare ni. Ni ban damu da hakan ba, idan ka rasa masoyi... Abin yana da matuƙar wahala da zafi a zuciya. Mai yiyu wa ka ƙara jin wani son mai yi yu wa kuma ba za ka ƙara ji ba har abada. Ni ba zan taɓa yunƙurin goge tarihin mijin ki a zuciyar ki ba, domin hakan nasan ba abu ne mai yiyu wa ba. Ban zo domin maye gurbin sa ba, na zo ne don in taimaka miki wajen ɗaukar nauyin da ki ka shafe shekaru da dama kina ɗauke da shi ke kaɗai...Beenafah ki ba ni dama, ki ba ni damar da zan tsaya a gefenki domin na zamto inuwa a lokacin rana, mafaka a lokacin ruwan sama sannan kuma san yi a lokacin zafi,sannan na kasance kujera kuma mahutar ki a lokacin gajiya...na rasa damar faɗa miki waɗan nan kalaman na tsawon shekaru ashirin da shida da suka wuce...amma a yau..Allah ya ba ni wannan damar, ki amince dani kin ji. Ba lallai sai a yau ba, ba lallai sai gobe ba. Zan jira na tsawon gobe, jibi, gata har zuwa lokacin da kika ji cewa za ki iya."
Kuka na ke ina mai jin yanda kalamansa ke ratsani. Daman da gaske abun da ya yi niyyar sanar dani kenan a ranar Emraan ya karɓe wayata ya fashe ta a ƙasa? Shiyasa ya yanke wa kansa hukuncin ƙin raɓar duk inda nake?
Lumshe idanuna na yi a hankali sannan na buɗe ina mai jin wasu sabbin hawayen a zuciyata ina faɗin.
Haƙiƙa ba ka yi Ƙarya ba Yaya Ashiru da kace ka Makara. Tabbas ka makara ɗin na tsawon shekaru ashirin da shida, ka riga ka mara domin Dayaa ne kaɗai wanda yake zuciyata. Ya bani farin ciki da duk wani gatan da mace take buƙata a wurin mijinta. to amma nauyin da ka ajiye a ƙirjinka tare da haƙuri da ka nuna. A yanda ka girmama ni ka girmama Mijina, ka kuma jure tsawon shekarun nan ko bana jin son ka ba zan ƙi amincewa auren ka ba. Ko don na saka Ammie na farin ciki zan amince da kai. Ko don 'ƴa' ƴana da suka ga cancantar ya kamata ace na yi aure zan amince maka. Ko don Bahrain da ya cire nauyin da yake ji nawa ya yi mini maganar ka ba zan ƙi amincewa ba. Kalmomin Ammie ne a raina, wanda ta taɓa faɗamin cewa, ta aure Dr. Basheer ne ba don soyayya ba, sai don cike wani gurbi da ta rasa.
"Beenafah! Idan har na faɗa miki wata kalma wacce ba ta yi miki daɗi ba, dan Allah ki yi hak'uri. Ban ji daɗi ba Sam yanda ki ke ta wannan kukan haka. Da ace na san za ki zubar da hawaye haka, da tabbas ban aikata ba....Hawayenki na ƙona ni, dan Allah ki yi hak'uri."
Girgixa kaina na yi ina mai share hawayena na ce.
" Ba ka yi kuskure ba Yaya Ashiru...da in auri wani wanda bai cancance ni ba, gwanda na aure ka ɗin domin kai ne wanda yasan zafina bayan mijina. Ba kuɗi ko wani matsayi nake nema ba. Ina so na auri wanda zai kula dani da taimakamin wurin kulawa da yarana ba tare da jin na takura masa ba nima kuma ba tare da na takura ba. Wanda zamu girmama juna mu mututunta juna ba don wani abu da ɗaya yake da shi ba...."
"I promise you Beenafah… ba zan taɓa cutar da ke ba. Ba zan taɓa ɗora miki nauyin da ya wuce ƙarfin ki ba. Kuma ba zan taɓa neman ki goge tarihin wanda kika aura kafin ni ba. In sha Allahu zan kasance a yanda kike so na, zan kula da yaranmu da dai gwargwadon iya wa ta. Ba zan taɓa barin ki ki yi kuka ba, ba zan taɓa bari ki cutu ba."
Miƙewa na yi ina Kallonsa a hankali na ce.
" I will go now...domin ana jirana. In Sha Allahu zamu tattauna da Ammie da su Bahrain. "
Cikin farin ciki ya jinjina kansa yana murmushi ya ce.
" Take your time. Allah ya sanya alheri da albarka ya basu zaman lafiya."
"Amin. Thank you."
Ina fitowa na zuba ido ina kallon yanda kowa yayi cirko-cirko ana jirana,domin Kausar ta ce ba za'a ɗaga da ita ko'ina ba sai idan na zo. Hakan yasa na yi ƙoƙarin daidaita kaina na shige motar muka tafi muka rakata ɗakin ta wanda ya sha kaya na alfarma,sai dai mu yi addu'ar Allah ya bada zaman lafiya da zuriya ɗayyaba.
Bayan mun dawo, a daren Ammie ta same ni a ɗakina ta ce.
"Beenafah! Miye kike yanke akan Jafaru?"
Kallonta na yi, sai kuma na Girgixa kaina na ce.
"Ammie ba zan iya auren Barrister Jafaru ba. Amma na yanke zan auri Alhaji Ashiru Ammie..."
Cikin wani irin farin ciki ta zo ta zauna a kusa dani tana murmushi ta ce.
"Kai Alhamdulillah! Gaskiya na ji daɗin wannan shawarar da kika yanke. Tabbas babu wanda ya fi dacewa dake idan ba Ashiru ba..."
"To amma miyasa a farko kika ce Jafaru ne yafi dacewa Ammie?"
"Saboda ya dawo ya nuna mini da shi da iyayensa yana so ya aure ki, and Ashiru shi bai ce yana son ya aure ki ba a yanxu...kin ce kuma bakya son Emraan da duk wani wanda ya zo domin ki. Hakan yasa na ga cancancarta sa, amma idan har Ashiru ya zo da zancen auren ki, to tabbas hankalina zai fi kwanciya da shi. Sai dai shi Jafaru ina masa addu'a Allah ya bashi wata wacce zai aura ko don farin cikin iyayensa. "
" Ba zan iya auren Jafaru ba Ammie..ina fata da addu'ar iyayensa da shi kansa su yafe mini. "
" In Sha Allahu zan yi magana da su kada ki damu. Yaushe kike ganin auren ya kamata?"
" Daga zaran na tattauna da su Aryaan..In Sha Allahu sai ku yanke lokacin da kuka ga cewa ya yi muku, sai a yi. "
Cikin farin ciki ta ce.
" Masha Allah. Allah na gode maka, Allah ya amintar dake yasa albarka a cikin wannan auren da za ki yi Beenafah."
"Amin Ammie."
Washegari da muka zauna muna tattauna maganar da su Aryaan na yi mamaki da suka ce wai an sun san da zancen domin Bahrain ya sanar da su labarin yanda Ashiru ya je neman aurena da kuma yanda na auri babansu. Hakan yasa suka ga dacewarmu tunda na ƙi ƙanin Mahaifin su cewa da Emraan.
Bayan Ammie ta gama jin ra'ayoyin kowa ta tattauna da Abbu da kuma su Annie da Raihab aka saka auren wata biyu mai zuwa.
Ashiru ya yi matuƙar mamaki da farin ciki domin bai kawo komai a nan kusa ba. Sam bai ɗauka cewar abin zai faru da sauri haka ba. Ya ɓoye so da ƙaunar da yake mata tsawon shekaru, ya Karɓi Sabila domin itace xaɓin iyayensa bayan ya rasa Beenafah, ya ɗauki soyayyarta ya binne a zuciyarsa ya rufe domin ya cire rai da sake samunta har abada. So ɗaya ne kuma ya gama so akan ta. Ko a yanzu...ya yi buri da saka ran cewa zai iya samunta bayan Mijinta ya rasu. To amma a yanda yake jin cewa ta ce ba za ta ƙara aure ba a wurin Bahrain. Sai ya cire rai sai kuma gashi Bahrain ya same sa akan cewa shi ka ɗai ne wanda yafi dacewa da yayarsa, saboda haka ina ba shi shawara akan ya je gareta. Hakan yasa lokaci ɗaya So da ƙaunar da yake ji suka motso masa zuciya, take duk wani sirrin da ya binne ya shiga fitowa a hankali yana sarƙafe masa zuciya. Sai ga shi cikin ikon Allah ya yi nasara. Da ya shaidawa Su Umma Ayya har da kuka tayi na al'ajabin wannan so da yake yi wa Beenafah. Nan suka yi masa addu'a da fatan alheri na cewa ko yanxu ɗin Allah yasa ita ɗin rabon sa ce.
Bayan na koma gida tare da yara na shirya kamar yanda muka tsara muka tattaro ni da Zarah da Aliyu muka dawo, wanda su Aryaan suka yanke cewa idan lokaci yayi ana saura kwana biyu za su zo.
Ana gobe ɗaura auren ya zo yasa aka kira ni.
Yanda yake ta farin ciki ni abin har mamaki yake bani, domin ni Sam bana jin wani ɗoki ko marmarin abun a raina. Amma shi sai murna yake yana bayyanar da farin cikin sa a fili.
Kallonsa na yi sai kuma na ɗan murmusa na ce.
"Na zo sai kallona kake ka ƙi ka ce komai Yaya Ashiru..."
Jinjina kansa ya yi ya ce.
"Maman Zarah har yanxu sai nike jin komai yana mini tamkar a mafarki."
"Allah ke nan! Shi ne mai yin yanda ya so a lokacin da ya so."
Ɗan ƙara gyara zaman sa ya yi yana mai ci gaba da kallona ya ce.
"Haka ne. To, daman dalilin kiran na ki shi ne, ina so mu tattauna wata magana ce mai muhimmanci ne Maman Zarah."
Kallonsa nake a hankali ina mai bashi dukkan nutsuwata na ce.
"Allah yasa lafiya.."
"Lafiya lau In sha Allah Uwar Abdullahi...daman alfarma nake ne ma. Na san cewa kinfi ƙarfin komai da nake da shi. Kuɗi, gida, jin daɗi da more rayuwa...duk kin yi mini rata nesa ba kusa ba. Da wannan nake neman alfarmarki, dan Allah ki daure ki zauna a gidan da na sama miki a Abuja, na san dai rayuwar nan ɗin da can ba ɗaya bane... "
Girgixa kaina na yi ina mai jin tausayinsa a raina na ce masa.
" Ai rayuwa ba za ta taɓa tabbata ba har abada, a duk lokacin da muka samu canjin ƙaddara, to dole abubuwan rayuwarmu su sauya Yaya Ashiru. Kai ne wanda zai aure ni a yanzu, kai ne kake da haƙƙin nema mini wurin zama, abinci da kuma sutura, nauyin ka ne kuma ba zan hana ka wannan ba. Zamu bika a duk inda kake da ni da 'ƴa'ƴana kuma zamu zauna da kai lafiya tare da iyalanka In Sha Allahu..."
Cikin wani jin wani irin sabon farin cikin ya ce.
" Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! Na gode Beenafah, Allah ya saka miki da alheri. Allah ya bani ikon sauke nauyin da Allah ya ɗora mini...magana ta gaba kuma, a gaskiya ba gida ɗaya na tsara za ku zauna da Sabila, gidanta daban naki daban In Sha Allahu."
Jinjina kaina na yi ina mai jin wani sanyi a raina na ce.
" Na gode sosai Allah ya saka da alheri. Ni zan shiga ciki,sai goben idan Allah ya nuna mana."
"Allah ya bamu alheri Hajiya Beenafah, na gode sosai, ki gaishe da yaran."
Washegari kamar wasan 'ƴan yara aka shigo ana shaidamin cewa an ɗaura aurena a karo na biyu da Yaya Ashiru.
Su Aunty Labiba, duk da cewa ban zaɓi ɗan uwansu ba. Sun yi matuƙar farin ciki da yi mini fatan alheri. Wanda har Emraan ɗin sai da ya kirani a waya domin bai zo ba. Amma dai su Hairi duk sun zo tare da Aunty Ziza.
Haka kowa ya shiga fatan alheri a gareni wai har da su da Arhaam a faɗin Congratulations Maami. Allah yasa albarka ya bada zaman lafiya. Su kaɗai ne suke farin ciki amma Aliyu sam baya murna, da bakin sa ya faɗa min cewa shi baya son na auri wani, kawai na zauna abina a haka, Zarah kuwa sai murna take tana faɗin ai ko Daddy ba zai so zaman Maami a haka ba.
Sai da aka cika kwana biyu da ɗaura auren sannan muka hau jirgi zuwa Abuja. Kuka nake har muka shiga cikin gidan wanda ni kaɗai na san irin abun da yake damuna. Wai ni Beenafah ni ce yau na aka rako gidan wani wanda ba Dayaa ɗina ba. Rayuwa matuƙar kana numfashi to har abada baka rabuwa da jarrabawa, domin a hakan ni sai in godewa Allah. Saboda wata sai tayi aure uku huɗu a rayuwarta wata ma fiye da haka.
Ashiru kam duk ya ruɗe sai rawar ƙafa yake kamar shi ne auren sa na farko, bayan yana da matarsa har da yara huɗu wanda har ya aurar da ɗaya daga cikin su ta farkon mai 23yrs.
Gida ne babban gida wanda ni sam ban tsammata ba, akan ganin girman shi da tsaruwarshi ne sai dai shi flat Mansion ne amma yana da yawan ɗakuna masu tsari mai kyau. Kayan da ma aka saka sun yi daidai da gidan wanda Bahrain ne da Ammie suka siya komai da komai daga waje.
******
Finale....
A hankali na fara sabawa yayin da rayuwa ta sauya mini a gidan Alhaji Ashiru,wanda ya ƙauna ce ni ya kuma nuna mini irin son da yake mini wanda ya yi ta dakonsa a zuciyar sa na tsawon shekaru.
Hakan yasa na samu nutsuwa daga ni har yara na wanda suke zaune a Dubai ɗin gidan Daddysu Emraan, idan kuma sun samu hutu sai su dawo gida inda nake. Suma su Aryaan suna yawan zuwa dubani tare da matansu waɗanda ke da yara ɗaɗɗaya a yanxu.
Abdallahna bawan Allah shi ma yana Madina wanda sai idan ya samu hutu ko wani sarari yake zuwa ya ganni
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 66 Chapter of 67