ya turo mini text na cewa duk abinda nake naje na kwanta dare yayi.
Hakan yasa ina yin fitsari na samu wuri na kwanta domin ko wankan na ji ba zan iya yi ba. Kwance nake ina waya da Bahrain sai naji ana nocking door ɗina, ta shi na yi na je na buɗe sai ga Noura na gani wai tana so ta kwana a gidana. Baro ɗakinda nake ciki na yi wanda shi ne ɗakinmu ni da Dayaa na je na buɗe wani muka shiga muka kwanta a gado ɗaya da ita.
Massage ta fara mini ganin yanda ƙafafuna suka ɗan kumbura kaɗan, tana yi muna fira wanda ni duk kunya ma ta gama kamani domin babu yanda ban roƙeta ba akan ta daina ta ƙi. Mun yi rabin dare da ita muna fira sannan daga ƙarshe muka yi baccin gajiya.
Gefen su Ammie ma, kusan tun ranar da suka zo baccin su kaɗan ne, domin fira suke kwanayi da juna cike da kewa. To yau ma tare da mahaifiyarsu suka kwana su uku suna ta firarraki da ƙara samun haske akan rayuwar iyayen nasu.
Washegari, ni kam da wuri na je gyaran kaina na dawo, wanda a can aka mini jan lalle wanda ya yi kyau sosai na ji da gani domin Mijina wanda nasan lokaci kaɗan ne ya rage su iso tare da Amarya Hairi, su Aunty Labiba da sauran en uwansu da kuma Ango Emraan.
✍️ *OUM-AMEER* ✍️
*GANIN IDO* 🥀🥀
*ADABI WRITER'S ASSOCIATION*
*AMEENA IBRAHIM*
*OUM-AMEER*
*Wattpad:@Ummu-Ameer* *Arewapen:@Oumameer2671*
*FREE-BOOK*
*PAGE 56*
Muna cikin jera abinci ni da wasu masu aiki guda biyu Suhaib ya shigo tare da Zayn. Wasu kuɗin da ya bani ajiya tun kwana da suka wuce yace na ɗauko masa.
Har na miƙa masa sun juya sai kuma na ce.
"Ko za ku ci abincin ne Zayn?"
Girgiza kai Suhaib ya yi yana dariya ya ce.
"Ke yanzu Uwargida dan Allah idan na ce miki zan iya cin abinci za ki yarda?"
Tsaki na ja ina masa wata harara ta can ƙasan ido. Duniya Suhaib ya gama raina ni, shi kaɗai ke ce mini wai Uwargida. Hakan yasa na ce.
"Mts! Suhaib wannan kalmar ta uwargida da kake kirana da ita bana so fa..."
Dariya ya yi ya ce.
"Miyasa?"
"Da gaske nake faɗa maka Suhaib. Saboda ya kan sa na riƙa ji kamar zai auro wata wacce za ka riƙa kira amarya..."
Daga shi har Zayn ɗin dariya suka yi sannan daga ƙarshe ya kalle ni ya ce.
"Na rantse miki da Allah Yallaɓai ba zai iya ƙara aure ba. A yanxu dai nake faɗamiki, domin ban san abin da gaba za ta yi ba. Wai kin san artabun da ya yi akan auren Noura..."
Dariya na yi na ce.
"Wannan kuma ya wuce. Za ku ci abincin ko a'a?"
"Ni dai a'a. Kin ga tafiyata. Kuma kai idan ka tsaya, to zan yi tafiyata na barka."
Dariya muka yi sannan Zayn ɗin ya ce.
"Na gode Aunty Beenafah. Sai an jima."
Yana gab fita na ɗaga murya ina dariya na ce.
"Ka gama duk wani zumuɗinka. Abinci ne sai ka nemeshi."
Bayan na kambala na je na yi wanka na shirya cikin wata rantsatstsar Abaya baƙa sannan na fito. Suna can suna ta budurinsu ni kuma ina nan na gyara komai na shigowar mijina kawai nake jira.
Ina nan sai kiran wayarsa nake ashe sun fi hour da shigowa yana can cikin gidan tare da su Ammie bayan an shige da Hairiyyah.
Fitowa na yi na je masaukin su Ammien inda a can ne suke zaune tare da su Annie da su Mummy Na'imatu. Rungume ni Hairiyyah ta yi idanun ta cike da hawaye sannan ta janye ta ce.
"I miss you..."
Dariya na yi, ina mai shafa kumatunta na ce.
"Amarya bakya laifi, ko kin kashe irin su Shuraih su Zayn su Taimiyyah."
Dariya suka kwashe da ita, sannan na kalle ta na ce.
"Kin kyau sosai Hairiyyah. Allah ya sanya alheri da albarka ya bada lafiya..."
Hugging ɗina Bahrain ya yi yana mai fashewa da kuka. Bubbuga bayan sa na fara a hankali tare da kalaman rarrashi har sai da na ji ya sarara sannan na kalli fuskarsa na ce.
"Wai duk wannan kukan na farin ciki ne?"
Hannayena ya jimƙe a nasa yana kallon idanuwana yana murmushi. Cike da alfahari ya ce.
"Aunty Beena! Tabbas kina da wata baiwa da ban san yadda zan kwatanta miki ita ba. You are not just a sister...you are a blessing to our family. Ke ɗin Yaya ta gari ce wacce tasan abun da take yi, wacce ta iya kula da rayuwar ƙannenta tamkar ita ce uwar....Thank you for all the effort, for the stress, for the sleepless nights..Allah ya saka miki da alheri. Duk wani alƙawarin da kika mini tabbas ya cika Aunty Beena...tun bani da cikakken wayau kike mini alƙawari, ni kuma a lokacin kece madogara ta kuma duk abinda kike faɗamin ban taɓa ji a raina cewa kina faɗamin ne kawai wai don ki kwantar mini da hankali na ba. Da wannan sai Allah ya dubemu ya cika mana. Ban taɓa tunanin cewa zamu kawo wannan matakin ba a rayuwa, but you pushed it to be real. You are my pride, thank you for being strong for both of us. Thank you for loving and caring for me...Thank you for being the sister that every brother dreams to have."
Jinjina kaina a hankali na share hawayena na ce.
" Na gode da yarda da kayi dani Bahrain. Ubangiji da zuciya yake aiki. Matuƙar niyyarka, mafarkinka ka gina su da yaƙini da kuma kyakkyawar zuciya wacce bata nufin kowa da sharri...to In Sha Allahu watarana wannan burin naka sai ya cika. Mafarkinmu na haɗu wa da en uwa ya cika ba?"
Murmushi yana jinjina kansa yace.
" Eh."
"To yanzu ni ce na biyo ka bashi. Ka tsaya ka yi karatu domin ka cika mini mafarkina na hawa kujerar Abbie.."
Cike da ƙwarin gwiwa ya yi twisting hannunsa a nawa yana jinjina kansa ya ce.
"In Sha Allahu, na yi miki alƙawarin wannan."
Gabaɗaya hankalin mutanen ɗakin ya dawo kanmu. Jansa na yi ba tare da na raba hannayen namu ba. Na shiga nuna masa mutane ɗaya bayan ɗaya yana gaisa wa da su sannan daga ƙarshe na dawo wurin su Aunty Labiba, inda na ganta zaune wuri ɗaya tare da su Ammie, sannu da zuwa na yi mata sannan muka gaisa na gaishe da sauran mutanen na zauna muna ɗan taɓa fira wacce duk akan dai maganar bayyanar familyn namu ne.
Kallonsa nake yanda yake ta dariya da su Ammah a gefe gwanin sha'awa da shi da su Emraan.
Fitsarin da ya dame ni ne yasa na miƙe na ce musu zan tafi gida. Yanzu ban san mi yasa ba, yawan fitsari nake kamar me, kuma idan naje ɗan tsitau nake yin sa, wanda idan ban yi ba neman nutsuwa ta nake na rasa.
Yana ganin ficewata shima ya yi musu sallama ya fito. Ina shigowa na duba agogon wayata na ga ƙarfe shida na yamma ne saura.
Toilet na shige, bayan na kambala na fito.
"Kina fushi ne?"
Kallon sa na yi, sai kuma na yi murmushi domin yanayin yanda ya yi tambayar ne ya bani dariya ba kaɗan ba.
Matsowa na yi tare da shigewa jikin shi na ce.
"Laifin me ka min da zan yi fushi mijina? Welcome...and I miss you."
Tattausan lips ɗinsa na ji yay min light peck a goshina sannan ya saka hannayensa ya kewayena da su tare da ɗora fuskarsa a gefen wuyana na ɗan lokaci sannan ya janye yana kallon cikin idanuna ya ce.
" Congratulations Bibina...na yi matuƙar farin ciki da jin kyakkyawan labarin cewa mu ɗin en uwana. Na sha mamaki sosai da na ji yanda abubuwa suka kasance, duk da cewa babu mamaki a cikin al'amarin ubangiji. Duk abinda ya tsara zai faru, to tabbas zai faru babu makawa. Jininmu ɗaya ta gefen iyayenmu mata, Grandma ɗinki da Grandma ɗi na uwa ɗaya uba ɗaya suke wai su ɗin twins ne. And mahaifiyarki da mahaifiyarki Noura, suma ɗin twins ne Bibi..."
Hawayena na share ina jinjina masa kaina da murmushi na ce.
" And...kai ɗin Yayana ne, kuma mijina, ɗan uwana. Miye yafi wannan farin ciki? Ga dangina na samu...kana ji ko Dayaa? Ban san waye kakana ko kakata na gefen uba ba, amma a jiya...samun Abiyh da na yi da Ammah..na ji farin ciki sosai wanda sai da na zubar da hawaye...wai dama haka ake ji? Daman idan ka rasa wani a lokaci ɗaya ya bayyana a gareka farin ciki da daɗin rai ne ke hana zuciyar ka sukuni.? Alhamdulillah! Babu abin da za mu cewa ubangiji sai godiya."
"Ina son ki Bibi! Kamar yanda na saba faɗa...ke ɗin ta daban ce a cikin dubban mata. Har yanzu ta dalilinki ne ta kuma sanadin ki ne duk waɗannan alkairan suke ta faruwa...Ina alfahari dake. Not me alone...gabaɗaya dangi kowa yana alfahari da ke. Kin cike mini kowane gurbi, kin zamto mafaka ta, mafaka ta har abada."
Murmushin jindaɗin yanda yake ta koɗa ni na yi sannan na ce.
" Mu je kaci abinci..."
Gaba na shiga har muka isa muka zauna na shiga serving na shi.
"Bibi..."
"Uhmm"
Na amsa ba tare da na kallesa ba.
"Waye ya yi wannan girke-girke!"
Sai yanxu na ɗago na kalleshi ina murmushi nace.
"Masu aiki mana."
"Kina shan routine drugs ɗin ki kuwa?"
"Sosai. Ko ɗazu sai da na sha."
A tare muka ci abinci wanda a yanzu cin abincina ya ragu sosai ba kamar can baya ba. Bana ci da yawa, sai dai kuma ba'a jimawa sosai nake sake neman wani.
Bayan mun kambala ya shige ya yi wanka sannan ya fita masallaci. Nima ina kambala isha na fice na shige can inda su Aunty Labiba aka zauna ana ta abu ɗaya wato fira. Nan aka yanke cewa idan gari ya waye. Za'a gyara ɗakin Hairiyyah da gidanta ke nan cikin estate ɗin su, wato sabon gidan da akayi. Sannan itama Suwara, ana gama ɗaura aure gobe, talata za'a juya da ita zuwa gida Nigeria.
A Rooftop ɗin gidana muka haye ni da Aunty Labiba, sis Noura, Aunty Nadeeyah, Hairiyyah da kuma Suwara. Wani shafin fira muka buɗe sabo, fira ce mai matuƙar muhimmanci da ta ƙara mana ilmi akan zamantakewa na yau da kullum. Duk firar nan da muke sai wani tausayina suke suna faɗin wai naje na kwanta waye-waye. Ni kuma dariya kawai nake musu domin wallahy bana jin komai, kawai nauyin cikin ne da kuma sauyin da jikina ya samu nake jin wani iri, amma sam bana jin alamar wata rashin lafiya ko wani abu makamancin haka.
Muna muna fira muna shan daddaɗan shayin ya kasance musu al'ada da ɗan taɓa snacks, abin da dai ranka yake so. Sai kusan ƙarfe ɗaya da wani abu na dare sannan muka sauko kowa ya nufi mahutarsa kafin gobe a ɗora kuma.
Ina shiga na tarar ba kowa, daman na sa a raina cewa, tun da naga bai kirani ba nasan cewa shima ɗin yana can tare da su Jaddi.
Zaunawa na yi kamar da gaske da sunan na jira sa. Sai gashi ban ƙara sanin ina kaina yake ba sai da na farka da asuba na jini a cikin jikin sa.
Na yi mamakin duk yawan fitsarin da nake tashi yi akai-akai yau sai gashi tunda na kwana ɗin ban farka ba, wata ƙila kuma tsabar gajiya ce shiyasa hakan.
Muna gama breakfast aka fara shirye-shiryen ɗaurin auren Emraan da Suwara yayinda muka ɗunguma gidan Hairiyyah wurin gyara mata ɗaki.
Hmm! Wai akace masu abu da abunsu. Wato an zuba mata kaya na ji da gani tamkar ba za'a mutu ba. Daman kuma yankewa suka yi da cewa, a ɓangaren su Jaddan su za su zuba mata kayan buƙata, su kuma gefen su Aunty Labiba can za su zuba na Suwara. Wannan tsarin da suka yarda da shi babu algus, domin wata duniya ce a ka ƙirƙira a wannan yankin na Suhaib da Hairiyyah.
Muna nan gidan aka kira akace an ɗaura auren, sannan bayan an kambala kuma an mayar da auren Abiyh da Ammah.
Ji na yi idanuna sun cika da hawaye, wanda a lokacin babu abinda nake son gani sai fuskokin su Ammie da kuma Amarya da ango, wato Abiyh da Ammah. Ko ya za su a ransu yau ɗin nan, bayan tsawon shekaru da rabuwa har tsufa ya kama su ga shi a yau za su ƙara kasancewa da juna. Datse tunanin na yi daga ƙarshe ina fatan koma miye, yasa su kasance da juna a wannan karon har mutuwa.
Da yamma misalin ƙarfe shida aka shiryo Hairiyyah aka kawota ɗakin ta tare da tarin addu'o'i da fatan zaman lafiya da farin ciki mai ɗorewa.
Bakin Suhaib ya kasa rufuwa a wannan daren, duk inda ya gifta bakin nan nasa har kunne.
Nan muka gama tsokanarsa bayan ta fito daga ɓangarensu Jadda mukai masa fatan alheri ya wuce. Wai don Suhaib ya raina ni, har da cewa na dafo masa ruwan zafi da breakfast da safe.
Washe gari ma, da wuri aka fito da Suwara, tare da su Aunty Labiba su Mummy Na'imatu da su Baba Ustaz domin komawa gida.
Wani irin Kuka Suwara ta fara wanda kowa da ke wurin sai da ta saka shi kuka. Da ƙyar aka samu da rarrashi da komai aka yi nasarar saka ta a mota.
Bayan an kammala komai cikin farin ciki da fatan alheri. Bayan kwana biyu kuma, su Ammie suka shirya tare da su Annie, Abiyh da Ammah suka wuce Qatar.
Hmm! Sai abun yake yiwa kowa kamar a mafarki, musamman Ammah, wacce Hawayenta suka kasa tsayawa. Cike da kewa muka rabu da juna tamkar kar mu rabu. Musamman Noura da ta bani muhimmanci sosai nima kuma nake jin ta har cikin zuciyata tare da sauran en uwa.
Bayan tafiyarsu Ammie da kwana ɗaya muma muka fito domin tafiya gida.
Har gaban Jadda na je na tsuguna da ƙyar domin zama a ƙasa yanzu yana bani wahala.
Da wasu irin hawaye ta kalleni a raunane ta ce.
"Ki yi haƙuri Beenafah. Na aikata kuskure. Sumaiha twin sister ɗina ce, ina jin ciwon da take ji a raina a duk lokacin da wani na ta ya shiga matsala. Da ita da iyalanta, wallahy ina yi musu ƙaunar da ni kaina ban yiwa kaina ita. Sai ga shi ashe sara na yi akan gaɓa dara taci gida. Ki yi haƙuri ya yafe mini."
Tafin hannuna na saka nima na share nawa hawayen, ina jinjina kaina na ce.
" Jadda kin san me? A duk lokacin da wani abu zai zo mana tsakaninmu da musulmi ɗan uwanmu, to abinda yafi cancanta shi ne mu fara duba matsalar da ido na gaskiya ido na basira. Idan muka ce son zuciya shi ne abinda zai fara zuwa farko...to tabbas zamu cutar da waɗanda ba su da wani laifi a garemu. Ni kin gano cewa jininki ce, da ace baki gano hakan ba, to tabbas da ba za ki taɓa ɗaga mini ƙafa ba."
Kaina na ɗora akan cinyar ƙafarta a hankali na ce.
" Kada ki ƙara ji a ranki cewa wai na riƙe ki a rai. Komai ya wuce a gare ni, kuma ko mijina ban faɗa masa ba. Na ɗauke shi a matsayin ƙaddara. Allah ya sadamu da alheri."
"Amin. Na gode Beenafah. Allah ubangiji ya sauke ki lafiya ya bada rayayye mai albarka. Allah ya ƙara miki albarka ya ƙara muku zaman lafiya da haƙuri a cikin rayuwar aurenku."
Tare muka fito da sauran mutanen gidan da suka rakomu har bakin mota. Hairi wacce hannun ta ke cikin na Suhaib ne ta kalleni tana ta murmushi ta ce.
" Mummy! Allah ya kai lafiya ya saukar mini dake lafiya. Please ki yi mini alƙawarin haifo mai kama dani..."
Dariya muka fashe da ita sannan na Suhaib ya buɗe mini mota yana faɗin.
"Allah ya tsare Hajiyata. Allah ya saukar mana dake lafiya."
A haka muka yi sallama da su sannan daga baya sai gashi ya shigo motar shi ma muka kama hanya.
********
Gefen Jafaru kuwa, bai samu nutsuwa ba sai da ya tattara kuɗin account ɗinsa ya cire su gabaɗaya sannan ya haɗa da babbar wayarsa ya siyar suka tafi wurin malamin.
Bayan ya gama masa bayani ya ɗauko wani ƙullin magani ya bashi sannan ya ce.
"Wannan....ka saka mata a lemu, kunu, fura ko duk wani abin sha dai. Sai ka bata tasha da hannunka da na ta...sai wannan kwallin kuma, a ranar da ka tabbatar za ta sha wannan magani, to a ranar za ka saka shi a idanun ka.....wannan kuma, ƙwan Kurciya ne,...eh..wannan shi ake kira so Tsuntsu ne. Shi kuma,ka gan shi guda uku ne. Ka soya ɗaya ka ci, ka dafa ɗaya ka kwarɗe ka ci sai kuma ka samu gindin bishiya ka binne ɗaya."
Ji ya yi wata irin matsananciyar zufa ta shiga tsatstsafo masa ta ko'ina tsabar yanda ya ji abubuwan wanda babu ɗaya mai sauƙi.
" Ka ji abin da na ce maka?"
Jiki a sanyaye ya ce.
" Malam abun ne na ji kamar babu ɗaya da zai yiyu...ko dai akwai wani aikin da za a ɗan canja wanda ba dole sai na haɗu da ita ba?"
"Babu wani aikin da za a canza da shi Jafar, idan wannan ɗin ya yi maka to ka karɓa ka tafi. Muddin dai ka aiwatar da komai yanda na ce maka, to Beenafah za ta tsaya a tare da kai har ƙarshen Rayuwarta."
Hannu Uka ya kai yana zungurarsa,yana yi masa alama da ido akan ya karɓa.
Hannu biyu yasa ya karɓa sannan ya ajiye masa kuɗin suka yi godiya suka tashi.
Tun a hanya yake mita tamkar zai fashe da kuka yana faɗin.
"Ni duk wannan abun ina zan ganta dan Allah? Ina zan ganta ballantana ma in iya aiwatar da aikin nan? Kai koda ace na samu ganinta, ban san yanda zan yi na ba ta abu da hannuna ba in ce ta sha..."
"Mts! Ka kwantar da hankalinka mana abokina. Farin ciki ya kamata ka yi da wannan mafitar da ka samu. Kasa a ranka cewa aiki wannan har an yi shi an gama..."
Ji ya yi ma ya ƙara ɓata masa rai, hannu ya saka a aljihu ya fito da ƙwan wanda yake mini-mini sosai ya ɗaga sama yana kallo yana faɗin.
" Miye wannan ɗin ma da zai ce wai in soya ɗaya in ci sannan in dafa ɗaya? Ni gaskiya ba zan iya ci ba. Saboda haka gabaɗaya zan binne su..."
Girgiza kai Uka ya yi sannan ya ce.
"A'a fa abokina! Kada ka yi yanda ba'a ce maka ba, wallhy idan aikinka ya lallace ni ba ruwana kada ku ma ka yi blaming ɗina. Mts! Wai sai kace ba namiji ba! Ina duk zarrar ka take?, ina iƙirarin son da ka ke yiwa Beenafar yake? Common ɗan abu wannan wai ka hau complain akai. Miye wahalar a nan? Kawai ka shige jikin en gidanku ka riƙa samun update a kanta domin ka ji yaushe za ta zo ƙasar. Da zaran ta zo ai magana ta ƙare, yanxu gidansu kamar gidan ku ne, in ta kama har mota ka hau kana iya hawa ka cim mata har Sokoton da sunan ba ta haƙuri kawai ka aiwatar da aikinka, idan ma Gusau ɗin ta zo Kaga shi ke nan ta kwana gidan sauƙi. Sai aikin wannan ƙwan. Shi ke nan fa da ka kambala ka same ta kenan har abada, iyaka ka koma gefe ka jira, da kanta za ta hauka ce tace babu kowa a ranta sai kai...sannan wannan malamin ka yarda da shi Jafaru, aikinsa yi da cikawa ne. Ina tabbatar maka sai ka dawo da kanka kana masa godiya."
Ajiyar zuciya ya sauke yana mai jin nutsuwa sosai a ransa sannan ya yi wani murmushi ya ce.
" Na gode sosai Ukasha. Ka fiye mini su Qatada sau dubu miliyan. Allah ya barmu tare. Duk ranar da burina ya cika na samu Beenafah. Na yi maka alƙawarin wani abu wanda har ka mutu ba za ka manta da ni ba."
Cikin jin daɗi Uka ya yi wata dariya sannan ya ce.
" Allah dai ya biya, na Beenafah ko dubu ta taru. Kabewar kan kabari baƙin cikin mai taushe. Ai wallahy wannan matsiyacin mutumin sai ya gane cewa ya ja da babban mutum irin ka."
Da haka ya yi ta wani kuranta shi yayin da shi kuma Jafarun ke jin duk duniya babu wani shege sai shi.
Daga dare zuwa wayewar gari,har ya gama aikata wannan aikin ƙwan wanda sai da ya gama ya dinga amai tamkar zai mutu tsabar yanda yake jin ƙyanƙyami. Abu wasa-wasa sai ga shi an sadashi da gadon asibiti. Gashi ba shi da takamammiyar dubu biyar ta kai nai. Dole sai da aka gida Baba ya turo masa da kuɗi dubu ashirin aka masa ƙarin ruwa da maganguna sannan aka sallame shi.
******
Gefen su Mummy Zaliha kuwa, sai da suka yi wata biyu cikin na uku sannan suka dawo gida, bayan an sha jinya ya samu ya farfaɗo.
Koda suka iso sun iske gidan na su an ƙara gyara shi sosai an saka musu furnitures ya dawo gida abunda ake kira gida.
A ranar da suka dawo a ranar su ma su Hussaina suka dawo daga gidan Alhaji Baba ita da Humaida.
Humaida duk tayi wani baƙi ta lalace tsabar ɗorawa kai damuwa da tunani.
Suna nan Daddy suka fashe da kuka, domin dai lafiyar nan kam sai dai ace Alhamdulillah! Murmushi ya yi musu yana mai girgiza kansa ya ce.
"Ku daina Kuka Hussaina, doguwar jinya itama wannan kaffara ce. Ni a haka ma na godewa Allah. Kun ga dai irin rayuwar da muka rayu a ciki, daula kamar ba za ta ƙare ba ko? To ina so ku ɗauki wannan a matsayin darasin rayuwa, wallahy komai na duniya yana da farko kuma yana da Ƙarshe. Musamman zalunci, gaskiya ce kaɗai ba ta ƙarewa,...har abada ba za ku taɓa jin an ce wai gaskiyar mutum ta ƙare ba sai dai ace ƙaryarsa ta ƙare."
Hussaina na kuka sosai ta ce.
" Daddy darasi na nawa kuma? Yanda muka wuce muka bar Ammie a ranar da muka koma Abuja, Beenafah tana ta kuka tamkar za ta mutu amma baka saurare ta ba, haka tarihi ya maimaita kansa da kansa. A ranar da za su wuce, Humaida na ta kuka kamar za ta ɗauke numfashi suka wuce suka barta....Daddy aure na sau biyu aka nema, kamar za'a yi, amma sai aka fasa. Wannan kaɗai ni ya ishe ni darasi. Na ji daɗi na kuma godewa Allah da har yasa kuka gane gaskiya. Allah yasa mu cika da kyau da imani, Allah ya yafe muku ya baku aljanna maɗaukakiya. Ku ɗin iyayenmu ne, komai zai faru har abada ba za mu taɓa canja ku ba, kamar yanda kuma ba za ku canja mu ba..."
Share hawaye Humaida ta yi tana kallon Mummy ta ce.
" Ni ina so na koma gidan Aunty Aysha."
Ido Mummy ta zuba mata na ɗan lokaci tana kallonta, sannan daga ƙarshe ta lumshe idanun ta hawaye masu ɗumi suka zubo mata ta girgixa kai ta ce.
" Humaida rayuwar da ƙunci ko? Kin ji komai ya sauya miki ko? Hmmm! To ke da ba ki ma wani ji ma a cikin daɗin ba kika kasa daurewa. Ina ga Beenafah wacce ta taso cikin gata gaba da baya amma muka nakasar mata da rayuwarta? Yah Allah ka yafe mana haƙƙin waɗan nan mutanen da muka ɗaukarwa kanmu."
Husaina ta ce.
" In Sha Allahu komai ya wuce Mummy. Yanzu haka ma sun haɗu da dangin mahaifiyarsu, Ammie ta gano iyayenta na gaskiya, har Sheikh ɗinma. Sannan da Mijin Beenafah da ita Ammie dangi ɗaya suke jinin su ɗaya. Abun duk da bamu gani ba. An ce ya ƙayatar sosai."
Jikin Daddy ne ya yi sanyi jin ta ambaci sunan Sheikh. Da magiya da komai aka kira daga Canada aka ce ga mahaifin Mulaifa yazo. Amma bai ji kunyar Allah ba ya yi masa bayani da cewa wai duk sun mutu a car accident. Gudu kada ya ci gaba da neman su watarana ya same su, sai ga shi yanxu
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 58 Chapter of 67