Share this page
kusan 2hours sannan ya fito muka kama hanya sai Gusau. Wani gida muka sauka wanda zan iya kiransa da gidan gilashi domin bayan ginin simintin da naga an yi amfani an kewaye gidan da shi gabaɗaya, gidan gilashi ne ɗan daidai domin bai yi girman wanda su Hajiya suke ciki ba. Ya haɗu ta ko'ina maƙurar Haɗuwa. Ni ko na ce mai abu da abinsa, gidan babban Engineer da kansa. Kallonsa na yi bayan mun shiga gidan na ce. "Ba gidanmu inda Hajiya take zamu sauka ba?" Girgiza kansa ya yi kai tsaye ya ce. "Bibi ba zan iya zama wancan gidan ba. Kin san wani abu? Har cikin zuciyata na yafe mata kuma komai ya wuce, amma ba zan iya sake zama a inuwa ɗaya da Ita ba. Na auna yafi a ƙirga amma har yanzu ko kiranta na kasa yi..." Hannunsa na kama a hankali tare da saka idanuwana a cikin nasa na ce. " Dayaa! Har yanzu shaiɗan ne yake wasa da zuciyar ka, tun da ka haƙura ya kamata ka manta komai ku dawo yanda kuke.." Wani murmushin gefen baki ya yi yana mai girgiza kansa ya ce. " Idan aka sake ƙwarya ta baro bigirenta ta faɗo ƙasa ta tarwatse...yana da matuƙar wahala ta iya dawo daidai kamar yanda take...Tashi mu shiga ciki." Miƙewa na yi tare da bin bayan sa, duk da cewa Ina da sauran maganganu da yawa a cikin bakina, dolena na haƙura na haɗiye su domin bai bani damar hakan ba. Wanka muka yi muka yi sallah sannan muka ci abincin da ban san daga ina aka kawo ba. Bayan mun kambala muka ɗan zauna domin hutawa wanda sai misalin ƙarfe shida muka shirya muka fito sai asibitin FMC. Mamaki ne da al'ajabi suka lulluɓeni ganin har da Ammie da Bahrain da kuma Dr. Basheer a ɗakin, bayan su Aunty Aysha da su Mummy Zaliha. Tsaye na yi ina bin su da ido kamar yanda suma suka kafe suna kallona tamkar sun ga wata sabuwar halitta, musamman Mummy Zaliha da Daddy wanda yake kwance kamar ruwa sai aikin bin mutane da ido. "Beenafah." Ammie ta ambaci sunana ganin na yi tsaye ina ta kallon su idanuna cike da ruwan hawaye. A hankali na taka na je gabanta na rungumeta ina faɗin. "Ammie...Ashe kuma kun zo?" "Eh,yanzu muma bamu jima da isowa ba." Waigawa na yi na kalli Dr. Basheer cike da girmamawa na ce. "Abbu ina wuni! Barka da zuwa.." "Yauwa Beenafah! Da fatan kunzo lafiya?" Hannu Ya Mohaa ya miƙa masa suka gaisa sannan shi ma Ya Hafiz ya miƙo masa nasa hannun sannan Uncle Isma'ila. Gabaɗayansu su Uncle Isma'il ɗin babu wanda bai yi mamakin ganin mutumin da yake tsaye a gaban su ba,domin sun san shi farin sani, sai dai har yanzu basu gama fahimtar alaƙar zuwanmu tare asibitin ba kuma gashi mun shigo ɗaki ɗaya a lokaci ɗaya. Yatsa Hafiz ya ɗaga yana nuna sa still da mamaki a fuskarsa ya ce. "Engineer Muhammad Araam mai kamfanin Golden pathways...Kai ne aka haɗa da Daddy Bello a lokacin da za'a gina masa kamfaninsa na magunguna, a lokacin ganinka ya yi matuƙar yi masa wahala har ta kai sai da ya janye ya fara process ɗin neman wasu sai gaka ka neme shi daga baya." Jinjina kai ya yi yana murmushi ya ce. " Allah sarki! To ya mai jiki?" " Jiki Alhamdulillah za'a ce, sai dai bamu san abin da ya kawo ka ba?" Dr. Basheer ne ya ce. " Shi ne fa Mijin Beenafah.." Daga Hafiz ɗin, har su uncle Isma'ila, su Hassana babu wanda bai sha jinin jikin sa ba akan zallar madarar mamakin da wannan magana ta Dr. Basheer ta shayar da su. Muryar Daddy muka ji wacce ba ta ma wani fita sosai yana miƙo wani singilallen hannunsa da ya gama ƙarmashewa yana faɗin. "Beenafah...Beenafah zo kusa dani ki kawo min mijin ki na gani...kunyar duniya, wulaƙanci da tozarci sun tabbata a kai na Beenafah....Hajiya Mulaifa! Dan Allah ki yafe min.." Mummy Zaliha na wani irin kuka ta girgiza kanta ta ce. "Alhaji su yafe maka kodai su yafe mana? Komai mu kayi tare muka yi shi? Amma kai ne wanda ya fara nuna mana ƙofa, domin tun Dr. Bello yana raye kasha faɗamin cewa matar da Bello ya aura baka sonta, duk abun da kake mata kawai kana yi ne don GANIN IDON sa saboda baka da yanda zaka yi da ita tun da ya riga ya zaɓeta. Komai ta yi mana a duniyar nan zaginta kake. Da mijinta ya rasu ma farin ciki ka yi wanda kai ne ka zo min da plan ɗin yanda zamu mamaye komai ni kuma na hau na zauna har na zo na fika nuna musu tsana da ƙiyayya tare da Hassana da Hafiz..." Hannu Ammie ta ɗaga mata yayin da wasu irin zafafan hawaye suka shiga zarya akan kumatunta, a raunane ta ce. " Hajiya Zaliha ki daina dawo da hannun agogo baya! Abin da ya faru ya riga da ya faru yanzu kuma duk mun wuce wannan babin, idan mutum ya yi na gari don kan shi, idan ma ya aikata sharri to fa ɗan aike ya aika wanda dole watan watarana sai ya dawo gare sa...abu ɗaya nike so in ƙara Jan hankalin ki akai shi ne;A duk lokacin da muke jin wani yanayin ƙiyayya a tsakaninmu, to mu daina involving yaranmu a ciki, hakan yana taɓa su domin abubuwa ƙara lalacewa suke daga baya wanda ko da an so ayi sulhu, hakan yana matuƙar gagara. Kamar yanda kuka nemi alfarmar mu zo ga shi mun zo, mun yafe muku duk wani abin da yake tsakaninmu. Sai dai ka sani Alhaji Mudassir! Haƙƙin kashe Jaririn da bai san komai ba yana kan wuyan ka, wannan sai idan kun tsayu a gaban ubangiji domin shi ne wanda yasan abin da yafi da cewa da kai..." Lumshe idanunsa ya yi ya buɗe a hankali cike da wani irin raɗaɗi, hawaye wasu na bin wasu a gefen kuncensa ya ce. " Kai Co! Kai co na ni Mudassiru! Astagfirullah Allah! Ya Allah ka shiryeni, ya Allah ka ƙara shiryar dani da iyalina akan hanya madaidaiciya.." Shiru ɗakin ya ɗauka wanda baka jin ƙarar sautin komai sai na koke-kokenmu musamman Mummy Zaliha mai yin kamar za ta shiɗe tsabar yanda take ji. Haka suka bi mu ɗaya bayan ɗaya suna roƙon gafara wanda ni ce ma mai amsawa domin Bahrain ya maƙale jikin Abbu ko kaɗan ya kasa motsawa sai uban kuka da yake rusawa. "Aysha..." Muka ji Daddy ya kira Sunan Aunty Aysha a hankali wacce ke takure a gefe ɗaya ita da su Hassana suna ta kuka. Ɗagowa ta yi ta kalli gefen gadon da yake kwance a sanyaye ta ce. "Na'am Daddy!" Wani wahalallen yawu ne ya wuce masa a maƙoshinsa da ƙyar sannan ya ce. "Ki ɗauko wannan amanar da na baki na ce ko bayan na mutu ki damƙawa Mulaifa hannun ki da nata,ɗauko ki bata." Tashi ta yi a hankali ta saka key ta buɗe wata locker dake gefen gadon ta ɗauko wani file na fata mai kama da Jaka ta miƙa mata sannan ya ce. "Waɗannan, su ne kayayyakin mijin ki da na sace da kuma kema kayayyakin ki dana yaran ki, komai yana ciki. Kuma na gode da kuka janye ƙarar, ko a haka kika barni na san cewa ke ce da riba. Duk zakaran da Allah ya nufa da cara, to fa ko ana muzuru ana shaho sai ya y." Kallon Uncle Isma'ila Ya Mohaa ya yi ya ce. " Wane irin tsari ake kai da shi na jinya? Na ga yana jin jiki sosai..." "Ranka ya daɗe magani ana nan ana ta yi, kullum cikin siyen magani ake kuma kullum likitocin suna iya bakin ƙoƙarin su. Ga shi nan dai,sai an shafe sai kuma rai ya dawo, sai an shafe sai kuma rai ya dawo. Haka dai ake a wahalce. Da an so an fitar da shi waje inda aka yi jinyar sa na farko to abubuwan ne sai a hankali..." Jin yanda yake ta fitar da wani irin numfashi da sauri-sauri yasa hankalinmu ya koma kansa, sosai hankalina ya tashi domin in dai jinya mutum yake a gadon asibiti hakan yana matuƙar ɗaga mini hankali. Da gudu Hassana ta fita wurin kiran likita ni kuma na ƙara matsawa wurinsa ina mai kama hannunsa domin wallahy ba ƙaramin tausayi ya bani ba. Ƙoƙarin nake na buɗe bakina na bashi kalaman da wata ƙila su sanyaya masa zuciya. Sai dai kafin na yi wani yunƙuri har na kai ƙasa somammiya wanda daga nan ban ƙara sanin a ina nake ba sai da na farfaɗo na ganni a gida, saman Gado tare da Aunty Labiba a gefena. Da kyakkyawan murmushinta na fara yin tozali tana mai ƙara jimƙe hannuna a cikin na ta cike da tausasawa ta ce. "Beenafah kin farka? Sannu. Ya kike ji a yanzu? Akwai abin da yake miki ciwo? Mi kike so ki ci?" Bansan lokacinda wani irin murmushi ya suɓuce min ba saboda ba ƙaramin dariya ta bani ba na ce. "Aunty Labiba ni fa lafiyata ƙalau. Na je kawai zan yi magana da Daddy ne kawai na ga na faɗi..." Cike da farin ciki ta ce. "Allah ya ƙara miki lafiya Bibin Daddy...farar mace mai farar aniya, ga farar zuciya kamar zinari. Yanda kika saka Daddy a farin ciki...farin cikin da har sai da ya saka shi zubar da hawaye, ina miki fatan alheri, ubangiji ya albarkaceki ya kuma albarkaci abin da yake cikinki...Beenafah Giwar Daddy uwar gida kuma Amarya uwar 'ƴa' ƴansa. Allah ya ƙara miki farin ciki da kwanciyar hankali a gidan auren ki ya ƙara muku fahimtar juna. Mun gode, mun gode, Familyn ARAAM da Familyn SAMI muna godiya da wannan kyautar..." "Aunty Labiba ina Ammie.?" Tambayar da na jefa mata kenan domin ban gama fahimtar ma maganganun da take ba har yanxu. Al'amarin Daddy ya yi matuƙar ɗaga mini hankali, ya gigita ni fiye da zato. Wallahy duniyar nan ba bakin komai ba ce. Ji yanda Daddy gabaɗaya cikin lokaci ƙanƙani kamanninsa suka canja kamar ba shi ba. "Ammie yanzun nan suka wuce, su ma su Aysha ba su jima da tafiya ba." Cike da mamaki na ce. "Hala Karfe nawa ne yanzu?" Agogon wayarta ta duba tana faɗin. "11:14pm yanzu..." Zaro ido na yi ina faɗin. "Kenan na jima a kwance, tun 6pm fa." Jinjina kai ta yi ta ce. "Haka ne." Sallama Hajiya ta yi ta shigo ɗakin tare da yi mini murmushi bayan mun haɗa ido ta ce. "Beenafah kin farka.." Yunƙurawa nayi da nufin Miƙewa zaune domin na gaishe ta, sai ga shi ta zo da sauri ta ƙara mayar dani tana faɗin. "Kwanta abinki kinji. Allah ya inganta ya saukar da ke lafiya." Mamaki nike na wannan sabbatun da suke na maganar sauka da ingantawa, ni fa har yanzu ban ɗauki haske ba. Wayar Aunty Labiba da tayi ƙara ne ta janyo hankilana ganin ta ɗauka cike da farin ciki ta kara mini a kunnena tana faɗin Nadeeyah ce. Karɓa na yi muka gaisa sannan ta yi min ya jiki. Bayan mun kambala ta kira Hairi ta bani kamar yanda Hairin ta roƙeta cewa dana farfaɗo a sanar mata. Bayan mun gama ta kamo numbern Suwara inda a nan suka yi min caa! Kowa na faɗin albarkacin bakinsa harda su Jadda suna ta min sannu. Kallon Ziza Aunty Labiba ta yi wadda ke sanƙame a inda take tsaye tunda suka shigo da Hajiya ta ce. "Ziza kin tsaya ba ki zauna ba kuma ba ki ce komai ba." To me za ta ce? Mamaki ne da al'ajabi suka sanƙameta wanda har ta kasa motsawa tsabar yanda ganina ya dokar mata zuciya. Tambayar kanta take ta yi tun ɗaxu cewa wai daman BEENAFAH ce NANA? Duk labarin da Hajiya ta bata har yau bata taɓa ji ba ko da wasa cewa wai Beenafah ce matar Ya Muhammad ba. Beenafah fa? Cab! Lallai waɗan nan mutanen sai yau ta ƙara tabbatarwa cewa su ɗin ƙwallayen shegun munafukai ne. To miye a ciki da suke ta wani ɓoye-ɓoyen faɗa mata? "Ziza! Ki samu ki zauna mana, kada ƙafafuwanki su gaji.." Murmushi ta yi sannan ta ce. "Uhm! Ai dare ma ya yi tafiya zamu yi...." Sai kuma ta dawo da kallonta gare ni still da murmushin ta ce. "Ya jikin?" Rufe idanuna na yi ba tare da na ƙara kallon inda take tsaye ba na ce. "Lafiya." "Allah ya ƙara sauƙi" "Amin." Yanayin yanda ta ji na amsa ta shi ne abin da ya ƙara bata mamaki ya sanyata ƙara shan jinin jikinta wanda ko minti biyu bata ƙara ƙwarara ba ta yi mana sai da safe ta fice ta je mota inda Oga Sule ta zauna zaman jiran fitowar Hajiya domin su koma tare, wanda sai da suka ɗan ƙara jimawa sannan suka yi mini saida safe suka tafi. Suna fita na miƙe na lallaɓa a hankali na shiga toilet na watsa ruwa sannan na yi alwala na fito na yi sallah. Ina nan a zaune da tunaninsa a raina sai ga shi ya shigo ɗauke da ledoji a hannunsa. Ajiyewa ya yi kan glass table ɗinda ke gefe ya zo ya ɗagoni muka miƙe tsaye yana tallafo haɓata cike da wani shauƙi ya yi kissing lips ɗina da goshina a hankali sannan ya rungumeni a ƙirjinsa, cikin wata irin Murya mai cikakkiyar nutsuwa da haiba ya ce. "Hankalina ya tashi sosai, na shiga matuƙar gigita,na yi matuƙar ruɗewa, na kaɗu, domin na za ta wani abin ne ya same ki. Idan wani abu ya same ki ban san yanda zan yi ba. Na gode Bibina! Allah ya saka miki da alheri. Haƙiƙa na yi farin ciki wanda ban san ma ya yanda zan misalta miki irin yanda nake ji ba a raina. Wai ni ne yau nike da mata, tana ɗauke da cikina za ta haihu..." Ɗago fuskata na yi da sauri na kallesa ina murmushi cike da zumuɗi nace. " Da gaske? Haihuwa zamu yi? Zamu samu ɗa?" Shiru ya yi yana kallona da wani irin lallausan murmushi dake kwance akan fuskarsa. Yanda ta yi reacting ba ƙaramin ƙara hudashi ya yi ba. Wannan matar tashi Allah kaɗai yasan irin so da ƙaunar da yake mata. Ji yanda take nuna zallar farin cikinta jin cewa tana ɗauke da juna biyu... "Mijina! kasan me? Wani tafseer da na taɓa saurara malamin yana cewa;Ku yi aure, domin sunna ce ta ma'aikin Allah wanda ya ce ayi koyi da shi. Idan kuka yi aure ku roƙi Allah alheri da albarka, sannan ku yi addu'ar samun 'ƴa'ƴa na gari masu albarka, idan kun samu kuma, ku tarbiyantar da su ku kula da rayuwarsu domin su zamto yara na gari waɗanda za su yiwa addinin Allah hidima, sai rayuwarsu ta yi kyau, kuma kada ku gushe kuna yi musu addu'a da fatan alheri har zuwa numfashinku na ƙarshe...wallahy idan kuka tafiyar da su a haka, kuka sauke duk wani nauyi na su kamar yanda Allah da manzonsa suka koyar... To tabbas za ku yi alfahari da su tundaga duniya har zuwa gobe alƙiyama...Tun daga wannan ranar...babu wani lokaci da zai zo na yi sallah ba tare na roƙi wannan alherin ba..." Rungume ni ya yi yana mai jinjina kansa ya ce. " Allah na gode maka da wannan matar da ka bani..tabbas wani jinkirin alheri ne. Allah ya ƙara miki albarka. Ina son ki sosai. Allah ya raya wannan cikin ya girmar da shi cikin aminci. " " Amin." Janyewa yayi yana mai leƙa fuskata ya ce. "Mi kike so ki ci?" Dariya na yi sannan na ce. "Ni fa babu abin da yake damuna, komai ma aka bani zan ci.." Jinjina kansa ya yi yace. "To kuwa duk abin da na zo miki da shi sai kin ci...bari na yi wanka na fito" Ya shigewa na buɗe na ci duk abinda raina yake so sannan na sha ruwa wanda kafin ma ya gama abin da yake ni har na daɗe da yin bacci. Yana zaune yana cin abincin sai ga kiran Jadda ya shigo wayarsa. Fuska ba yabo ba fallasa ya ɗaga tare da yi mata sallama. Cikin farin ciki daga can ɓangarenta ta ce. "Barka Hammodi! Ina taya ka murna da wannan kyakkyawan albishir ɗinda ya riskemu. Allah ya inganta ya sauke ta lafiya. Kaga kenan alheri biyu da biyu." Cikin rashin sanin inda zancen na ta ya dosa yana wani irin murmushi ya ce. "Amin amin ya Allah Jadda. Na gode sosai, a sakamu a addu'a. A kuma tayani godiya ga Beenafah, tabbas ta gama mini komai a duniya, na gode mata. Ta zamto Mace mafi alheri a cikin rayuwa ta." "Wallahy kam Beenafah ta gama mana komai Hammodi, Allah ya ƙara muku zaman lafiya da ya ƙara muku fahimtar juna ya zaunar da ku lafiya....Bata wayar na ƙara gaishe da ita." Kallon inda nake kwance ya yi sannan ya ce. "Ai ta jima da yin bacci Jadda. Doctor ya ce ta riƙa samun bacci tana hutawa. Jiya ma kinga ga tafiya ga damuwar rashin lafiyar Babanta." "Allah sarki! To don Allah ka kula da ita yanda ya kamata ka ji ko? A kiyaye da dokar likita. Idan ma ta samu sauƙi kana iya dawowa da ita nan, domin idan tana ganin ta a gida to fa ba za ta daina yawo ba." Jinjina kansa ya yi ya ce. "In Sha Allahu Jadda! Na gode sosai Allah ya saka da alheri ya ƙara girma." "Amin. Allah ya tashemu lafiya." Washe gari da wuri muka shirya muka je AA master wurin Doctor Osita Wanda ya ƙware sosai wurin yin scanning na ciki da ma duk wani abu wanda ya shafi ciki da haihuwa. Bayan an kambala ya faɗa mana cewa cikin sati shida ne da kwana biyar. Godiya ya yi masa sosai sannan muka baro wurin zuwa gida. Halin da yake ciki na tsantsar farin ciki ni abin har mamaki yake bani. Tun jiya ya kasa tsaye ya kasa zaune kamar wanda aka ce masa haihuwar ta zo. Kwana fa ya yi bai runtsa ba yana ta ibada sai da lokacin sallar asuba ya yi sannan ya fita masallaci. Koda muka isa gidan na tarar da su Maman Fakiha sun zo tare da Ammie suna zaune suna jirana. Cikin wani irin farin ciki na yi tsalle na ɗale wuyan Ya Jafaru akan tsananin farin cikin ganinsa da na yi. ✍️ *OUM-AMEER* ✍️ *GANIN IDO* 🥀🥀 *ADABI WRITER'S ASSOCIATION* *AMEENA IBRAHIM* *OUM-AMEER* *Wattpad:@Ummu-Ameer* *Arewapen:@Oumameer2671* *FREE-BOOK* *PAGE 49* "Ke!..Ke!..Subhanallah!" Ya Jafarun ya faɗa da ƙarfi yana mai tureni daga jikinsa hankalinsa a tashe. Kallon kallo suka fara sannan suka maido kallon su a kaina tsabar mamakina da ya hana su magana wanda ni sam a gare ni ban ɗauke shi komai ba tsabar yanda na tsinci kaina a farin cikin ganinsa. Sai dai kuma, yanda suka yo min caa! A kaina ne musamman Maman Fakiha shi ya dawo dani cikin hankalina wanda a take na tuna cewa ban yi daidai ba. Da sauri na waiga bayana amma kuma ban ga Ya Mohaa ba, hakan ya tabbatar mini da cewa komawa ya yi bayan mun shigo. Haƙuri na basu sannan na gaishe su suka yi min ya jikina na amsa da lafiya lau ina mai zuwa na rungume Fakiha fuskata cike da annuri. Itama Fakihar cike da farin cikin ganina ta janye tana mai ƙure fuskata da kallo ta ce. " Ashe rai kan ga rai Beenafah? Idon ki kenan? Kin shige Ƙasar Larabawa kin zauna kin yi shiru hankalinki kwance...Masha Allah! Kalli kumatunki luwai-luwai! Kin ƙara fari kin yi kyau sosai.." "Uhm! Haka dai kika ce Fakiha. Ya karatu ya kwana biyu!" "Alhamdulillah! Komai lafiya ƙalau. Kina can Ammie na ta cika mu da abubuwan alheri. Mun gode Allah ubangiji ya saka mata da mafificin alheri....kinga ya Hamza an zama Cele..?" Dariya na fashe da ita kamar yanda ta yi ina mai kallon Ammie na ce. "Ammie Ina Ya Hamza?" "Hamza yana Sokoto, exams yake yi shiyasa bai zo ba..." Bahrain na dariya ya dawo gefena ya zauna yana faɗin. "Aunty Beena ba kiga idon Ya Hamza ba jiya, tamkar wani ɗan ƙaramin yaro haka ya ɓata fuska sosai sai da Abbu ya dinga masa faɗa musamman akan muhimmancin karatunsa." Girgiza kaina na yi ina dariyar na ce. "Ai Ya Hamza har abada ba zai girma ba...." kallon gefen da Ya Jafaru ke zaune na yi ganin yanda ya keta wani kakkaucewa kallona da mamaki na ce. "Ya Jafaru ina kwana? Sai wani yi kake kamar baka gane ni ba." Sai yanzu ya ɗago fuskar sa ya kalleni fuskar nan babu ƙiren annuri ya ce. "Beenafah ya jikin? Allah ya ƙara afuwa." Daga haka ya miƙe ya nufi ƙofa yana faɗin sai sun fito. Ko kaɗan bai so zuwa gidan nan ba, in banda Mama da Baba da suka matsa da sam bai yi niyyan zuwa ba. Wai har su ce an zama 'ƴan uwa! Bayan an cuce sa kenan. A yanzu tabbas yasan cewa ta fi ƙarfinsa domin ta taka tsani da matakin da ta yi masa rata to amma yasan cewa har abada ba za ta samu soyayya da kulawa ba kamar yanda ya shirya mata idan da ace shi ne ya aure ta. Domin shi ɗin saurayi ne mai jini a jiki, to amma wannan ɗin miye ta gani a jikin sa har ta ji cewa ya burgeta a ranta ta ji cewa ya fi shi? Shi ne fa wanda ya fara sonta tun bata kai haka ba. Amma shi ne za ta zaɓesa dare ɗaya ta barshi. Tsaki ya buga daga ƙarshe ma ya fita ya haye abin hawa ya wuce gida ba tare da ya tsaya jiransu ba. Ni kuwa, mamakinsa ne ma ya hanani magana. Yanda ya yi reacting sai yasa ni jin ba daɗi a raina kamar na yi masa wani abin ne. Hakan yasa na kasa daurewa na kalli Mamansu na ce. "Mama! Ko dai na yi wa Ya Jafaru wani laifin ne ban sani ba?" Cike da takaicinsa ta girgiza kanta ta ce. "Ƙyale mutumin wofi Beenafah...Babanku ya ce na gaisheki sosai, baya garin ne ya tafi Lagos ɗauko kaya, idan ya dawo kina nan, zai zo ya duba ki.." Cikin jin daɗi na ce. " Allah sarki! Allah ya tsare ya dawo da shi lafiya. Ina Farisa?" Bahrain ne ya karɓe zancen ya ce. " Ta na makaranta, ai sai da ma na rakata sannan na dawo..." " Sai da ka rakata? A ina ka ganta da sassafe har ka rakata?" Ammie ta ce. "Gidan su ya kwana fa. Kuma Humaida ta yi ta binsa ya kwana a gidansu, amma ko magana ya ƙi ya mata..." Kallona ya yi yana mai jin wani irin takaicin sa a ranta ya ce. "Aunty Beena ta ya ya zan kwana a gidansu yarinyar da ta dinga wulaƙantani? A gabana fa take cin abinci ina kallonta yayin da nake jin baƙar yunwa amma ko kallon inda nake tsaye bata yi. Haka lokacin da kuka taɓa tafiya asibiti kuka barni inda Mummynsu ta ce wa Mummy na zageta haka Mummy ta dinga dukana sai da Aunty Biba ta ƙwaceni....Mts! Bana son su Aunty Beena,sam ba su da zuciya mai kyau... " Lumshe idanuna na yi na buɗe ina kallon sa, a hankali na sauke murya na ce. " Bahrain! Ita fa rayuwar nan... " Miƙewa ya yi tare da saka hannu ya toshe kunnensa alamar baya ma son saurarena ya ce. "Ba abin da za ki faɗamin game da su...i will never listen to you." Daga haka ya fita ya koma can bakin swimming pool ya tsaya Wanda kana iya hango komai daga ciki. Fira muka yi sosai har kusan 12pm sannan su Mama suka wuce suka barni tare da Ammie. Ina ciki ina sallah na ji muryar Aunty Labiba ta shigo ita da su Adeel. Cike da farin cikin xuwansu na fito na rungume Hanan ina mai yi musu sannu da zuwa. Mamaki ne ya kamani ganin Biba zaune tana kallona. "Beenafah.." "Na'am Biba..da gaske ke ce?" kallona na mayar gun Aunty Labiba na ce. "Aunty Labiba kece kika zo da ita?" Jinjina kanta tayi tana murmushi ta ce. "Eh! Hajiya ce tace a kawo miki ita. Daman kin

Chapter 48 of 67