da halin da yake ciki h'aka ya boye besanarwa iyayensa ba' yabarwa zcyrsa shikadae' gani baya zuwa yasa Aisha tai amfani da wann damar tabawa Nasir damar zuwa' daedae lokacin da zahradee yake zuwa ta medawa Nasir lokacin.
"H'akan yasa iyayenta basu luraba' mafi yawanci lokuta umma ce take tambayar zahradee'sae Aisha tace aikine yai masa yawa shiyasa becika zuwa ba.
"Umma tace dama hakane Ai idan aski yazo baki goshi yafi zafi' mudae fatanmu Allah ya tabbabar mana da alkairi yasa ayi a sa'a. Nidae a matsayina na mahaifiyarki Aisha bazan gaji da yimaki nasiha ba' Dan Allah Aisha kiwa mijinki biyayya kibar gani yana mutuwa maki babu yadda Allah baya juya al'amarinsa' biyayya da kwantar dakae nasa mijinki ya kara sonki fiye da yadda kike tsammani.
"K'uma ki rike iyayen mijinki tamkar sune suka haifeki.
"Hakan zaisa mijinki yaji ya kara sonki SBD kina wa iyayensa biyayya.
"Aisha kizamo mace ta gari mai koyi da shugsban matan aljanna' Aisha inaso a lokacin da aka kaiki dakin ki' inaso ki natsu da'kyau ki lura da abinda mijinki yakeso kuma ki lura da abinda mijinki bayaso' kirinka kwantar masa da hankali a lkcn da yake cikin damuwa' hakan yakesa kiji ance mace ta mallake mijinta' wlh aisha babu boka babu Malam ladabi da biyayya ma kawai sun isheki Aisha' kinjiko.
"Naji umma k'uma ngd.
"Umma tace Allah yai maki albarka yabaku zaman lfy.
"Shiru Aisha tai bata tanka ba.
"Yau sauran seven week biki duk g'ida biyu shirye shirye sukeyi' da safe kafin su Alhj da zahradee sufita kasuwa Hjy mmn zahradee tabi Alhj har d'akinsa lkcn yafito wanka yana yana Shafa mai' b'akin g'ado ta zauna' cikin raha Alhj yace gimbiyata yaya akaine?
"Murmushi hjy tai alamar nuna jin dadin mgnr da yai mata' snn tace dama mgnr kai kaya g'idan su iyayen yarinyar gane' shine nace bari nazo na tambayeka SBD naga mako daya ne yarage.
"Murmushi Alhj yai h'ade da cewa h'aka ne' amma kiramin son tuku.
"Babu musu tamike zuwa part d'in zahradee taje ta sanar dashi abbansa na kiransa.
"Batare da bata lkc ba ya biyota sukaje tare' da sallama suka shiga d'akin' bakin gado ta zauna kusa da maigidanta'shikuma zahradee dukawa yayi a gefe yace Abba gani.
"Alhj yace dama mgnr kai kayane g'idan su Aisha' kamar yau she kake gani yafi dacewa akai kaya?.
"Nan Hjy ta h'au f'ada inda take shiga banan take fita ba' h'aba Alhj ni da kae be'isa muyi shawara ba sae da zahradee?
"Murmushi Alhj yai snn yace son ina sauraranka.
"Zahradee yace Abba abar mgnr kai kayan nan tuku' a gigice Hjy tace mekace zahradee?
"Shiru zahradee yai.
"Alhj yace son kasan abinda kake f'adi kuwa? Murmushi karfin hali yai amma duk wanda yasan me ake kira damuwa fuskan zahradee ya baiyana.
"Karewa zahradee kallo Alhj yai snn yasa hannu ya dagosa ya zuba masa ido cikin ido ya kare masa kallo snn yace son any prbms?.
"Kai kawai yakada sbd a yadda yakeji a zcyrsa bazai iya masu bayani ba' gani ransa yafara baci da sauri yafita yabar d'akin.
"Jikin haifiyarsa yai sanyi sosae'dukkansu su biyu sun kasa mgn.
"Da sauri Alhj yasa jallabiyarsa yafita zuwa part d'in su zahradee.
"Koda yashiga gani zahradee yai zaune a bakin gado ya zabga uban tagumi hannu bibbiyu' dukaww Alhj yai a g'aban zahradee h'ade da dafe kafadar sa yace son wani abune yake faruwa wanda ka kasa sanar dani?
"Shiru yai sae dae ido kawai.
"Son pls talk.
"Nothing'k kawai yace.
"Lock son inaso kasan da cewa ni fa mahaifinka ne' wanda a duniya bakada kamarsa' idan har kasan nine na haifeka inaso jin abinda yake faruwa.
"Zahradee naji h'aka fashewa da kuka yai' hade da kifewa a gado yana f'adin Allah Abba kafita kawai Abba....
"Kukan da yakeyi ya sashi kasa mgn.
"Gani irin kukan da yakeyi har jikinsa na rawa yasa Abba dagashi ya rungume yana f'adin is okay son.
" mgn Abba yai ta bashi har sae da ya numfasa yaga ya dae na kuka snn Abba yafita a dakin.
"Yana fita sukai karo da Hjy har zata shiga dakin Abba yace kada ta shiga ta rabu dashi.
"Hakan yasata komawa da baya.
"Batare da bata lkc ba Abba ya shirya ya fita zuwa g'idan su Ruslayni a kofar g'ida ya tsaya yasa yaro dake wucewa yai masa sallama da Ruslayni.
"Dayake shima yashirya zuwa kasuwa inda yake harkokin kasiwancinsa yasashi fitowa tare da d'an aiken.
"Gani motar Abba ne yasashi karisawa da sauri yaje inda Abba yai parking har kasa ya duka ya gaidashi' bayan sun gama gaisawa ne Abba yace nasan zakayi mmkin ganina a kofar g'idan ku' k'uma da safiya h'aka ko.
"Murmushi Ruslayni yai h'ade da cewa wlh kuwa Abba' amma Allah yasa dae lfy.
"Abba yace babu komai dama akan mgn abokin kane...
"Da sauri Ruslayni yace wani abune yafaru dashi?.
"A'a".
"Akan mgn aurensa ne ko kasan abinda ke faruwa a tsakanisa da yarinyar da yake so?
"Gaskiya abba banida lbr komai.
"Batare kuke zuwa g'idan su yarinyar dashi bane?.
"A'a" abba ni tun farkon zuwwnsa g'idan su Aisha yadda suke masa yasa naga kamar abin da rainin hankli shiya na dae na binsa.
"Amma wani abune ya hadasu da aisha?.
"Daga nan abba ya kwashe iya abinda yasani ya f'adiwa Ruslayni.
"Himm wlh nidae dama tun farko wlh Allah Abba Aisha kwata-kwata bata min ba'SBD daga gani idonta batada da mutunci' amma yanzu ina yake?.
"Abba yace to fa' Allah ya'kyau ta.
"Yana g'ida".
"Okay daga nan can kawai zanwuce.
"Nan sukai sallama.
"Tun daga lkcn Aisha tahana Alhj Nasir zuwa kofar g'idan su' Alhj Nasir babu yadda beyiba akan Aisha ta sanar dashi dalilin h'aka amma taki' cewa tai yai hkr tanaso koda zaizo yazama mgnr aure ne yakawosa amma yanzu idan yazo zai'iya bata mata shiri.
"Shima dayake akwai abinda yake shiryawa zcyrsa yasa hakan be damesa ba.
"Washe gani da yadda abba yatara duk yan'g'idan snn yasa aka kira zahradee dake kwace a daki yazo parlour' abba yace son gani da yan'uwanka' idan ni bazaka iya f'adimi ba to ga yayyinka sae kasanar dasu abinda ke faruwa.
"Shiru zahradee yai kansa a kasa.
"Shamsudee yace ba dakae akeyi bane.
"Zahradee yace Abba nafasa auren...
"Zahradee ya karisa mgnr ne h'ade da mikewa yabar gun.
"Gun yayyin hada ido suka duk sunkasa mgn SBD mmki.
"Salati kawai Hjy tai ta sanarwa ubangiji.
"Shamsudee da Nurudee mikewa sukai suka bishi daki' koda suka shiga babu irin tambayar da basu masa ba amma zahradee yace shidae fasawa ne kawai yai.
"Gani sauran kwana hudu biki babu wani abuda yashigo daga g'idan su zahradee' yasa umma tasami Alhj Muhammad da mgnr' shima yace abinda yana damusa amma idan yakira beyi laifiba?
"Umma tace laifi me? Kaidae kira muji abinda yake ciki.
"Wayarsa ya daga ya kira Alhj Kailani bayan su gaisa ne Alhj yace dama bugowa nai na tambaya sbd saura kwana hudu baku zoba baku turo wani daga bangarenku yazoba banle muji ina muka tsaya.
"Alhj yace eh hakan da kai yayi ko dama baka kiraba ni da kaina zanzo nasar dakai cewa mgnr aure dae babu idan yarodae yace yafasa.
"Yana fadin mgnr ya kashe wayarsa.
"Salati Alhj Muhammad yasa' cikin gigita umma tace lfy? Alhj yace mgnr aurene babu sunce su fasa.
"Fashewa da kuka umma tai hade da salati tana fadin yanzu SBD Allah irin cin mutunci da zasu mana kenan.
"Jin kukan umma ne yasa Aisha fitowa a guje daga dakinsu tana fadin umma lfy.
"Cikin kuka umma tace idan su zahradee ne wai sun fasa auren.
"Wani irin doguwar tsaki Aisha tai hade da cewa dan suce su fasa sae me sae kace shikadae ne autan maza'ni wlh na dauka ma mutuwa ai.
"Dan Allah umma ki daena kuka haka.
"Haba Aisha kinsan abinda kike fadi kuwa? Yaya kike mgn kamar wanda batasan ciwon kantaba.
"A lokacin ne Aisha tai dan guntun kwalla tana fadi to umma ya kikeso nace umma.
"Abbansu dake zaune kasa mgn yai.
"Umma taci gaba da cewa yanzu yaya zamuyi?
"Abba yace nima kaina tunani da yakeyi kenan' wlh hafsatu inda inada wani da zanbashi Aisha kodan na tura masu bakin cikin da suka cusami da jibi zan daurawa Aisha aure.
"Aisha najin haka wani irin dadi ne yakamata.
"Umma tace gaskiya kam' gashi babu wani dake zuwa gun ta banle ace yafito' to koda ma yafito ba lalla bane ya'amince a kwanaki hudu ga da suka rage.
"Aisha naji haka tace idan haka ne Abba ka kwatar da hnklinka insha Allahu bazakaji kunyaba duniya da lahira' idan har ka'amince akwai wani dake zuwa guna zan gwada nagani kodan naga na share maku hawaye.
"Shiru umma tai.
"Abba yace a'a aisha bazanso na takura makiba dan wata biyan bukatarmu' tunda abu yazama haka nabarwa Allah komai Allah yabaki wanda yafishi.
"Umma tace amin alhj.
"Aisha dake duke tace abba kada kadamu zan gwada nagani.
"Abba yace a'a aisha bazanso kiyi auren kiyayyaba nafiso ki auri wanda kikeso.
"Aisha tace karka damu abba.
"Mikewa tai tabar dakin' tana komawa dakinsu ta kira alhj nasir ta sanar dashi gobe yashigo gida.
"Nasir yai murna sosae dajin haka.
"Washe gari yazo gidan su Aisha' bayan sun gaisa da Bbn aisha ya gabatar da kansa kuma yace shi ko yaune idan sun shirya shima a shirye yake.
"Jin hakan abba yai murna sosae hakan yasa sukabar shi a ranar da akasa ita da zahradee.
"Zahradee wasa wasa ko fita baya iya yi' anyi anyi akaisa asibiti amma yaki.
"Ranar asabar aka daura auren aisha da nasir' zahradee najin labari fashewa da kuka yai' hade da yanke jiki yafadi sumanme.
"A gigice abba ya daukesa zuwa asibiti.
"Ana daura aure da safe da yake yan'uwan nasir sunzo' anayi azahar aka basu amarya sbd gari ba daya ba' kuma akwai tazara a tsakaninsu.
"Gani zatabar gida da yan'uwa da iyaye yasa Aisha kuka har ana riketa.
"Kwata kwata mutu 3 kawai Abba yabari suka bita SBD nisan guri.
📖🖊
☘☘
☘
AURE IBADA NE
FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘.
MMN USWAN
1⃣9⃣
"Rushing d'insa zuwa hospital' Abba dake rungume dashi a mota in ba addu'a babu abinda yakeyi' idan yai wann baya karisaea yake sakewa ya kamo wani' Shamsudee shike driving gudu yake kamar zaitashi sama.
"Da h'aka har suka isa hospital ko parking kirki basuyi ba Abba ya b'ude mota h'ade da fitowa da zahradee emergency room aka kaisa doctors dasukan duty to sukai can a kansa' kowa na nasa bakin kokarin'abba da Shamsudee da suke waje sae faman leke sukeyi.
" Da taimakon Allah yasa zahradee ya farfado' but still sama sama yake numfashi gani yabude ido yasa doctors d'in juna masa drip gani ya koma wani bcc yasasu fita daga d'akin' suna fita Abba da Shamsudee sukasa kai zasu shiga d'akin' da sauri doctors d'in suka dakatar dasu' h'ade da cewa dan Allah yana cikin critical condition dan h'aka yana bukatar hutu.
"Ido cikin ido suke kallon juna snn Abba ya kamo hannu Shamsudee suka zauna kan kujeran dake gefe d'akin' basu dade da zama ba saega su Hjy da Nurudee sun shigo hospital d'in ganisu da tai zaune a gefen d'akin yasata tambaya lfy?.
" shiru Abba yai mgn ta gagaresa' Shasedee yai masu bayani abinda ake ciki' salati Hjy tasa da salallami.
"Zahradee be falkaba sae gam da magrib snn ya falka Abba kawai yake ambato a bakinsa' da sauri Abba ya mike shida Shamsudee suka shiga d'akin' suma su Hjy suka bisu ciki gani hawayen dake gangaro masa ta gefen ido yasa Abba matsawa gun gadon tissue ya diba yana goge masa haeayen.
" zahradee yace Abba Aisha' Abba Aisha ta cuceni Abba.
"Abba yace son kabar mgnr Aisha d'in nan kaji da kanka son.
" wani muguwar tsaki Hjy tai h'ade da cewa Aisha me? Aishan banza.
"Shamsudee dake gefe yace to kai zahradee idan banda abinka wayasan abinda ya h'ada ku? Banle har a tayaka.
" zahradee yaci gaba da cewa Abba bansan abinda naiwa Aisha ba Abba Aisha ta gujeni Aisha ta daena sona Abba' dan Allah Abba kaje ka dawomin da Aisha wlh Abba inason Aisha Dan Allah Abba.
"Abba dake tsaya kusa dashi tsayawa yai shiru yana kallon zahradee dake kwance' gani shiru da yai yasa zahradee yunkurin mikeww zai tashi' da sari su Shamsudee suka rikeshi suna kokarin medashi ya kwanta' zahradee yace a'a ku barni kawai ni masamu sauki.
" duk zahradee yana mgnr ne amma bedae na kuka ba.
"Gani zasu gwada masa karfi yasashi rike Abba' a lokcin ne Abba ya dawo daga tunanin da yake' hannu kawai ya daga masu alama su bari.
"Abba da kansa ya jinginar da zahradee a jikin gado' snn shima ya h'au gefen gado ya zauna' cikin kuka zahradee ya kwashe duk abinda Aisha tai masa ya sanarwa iyayensa' yanayi yana kuka' har ya kare' yana karewa yasake fasawa da wani kukan h'ade da rungume Abba sa.
" Hjy dake gefe a take tace kan'buhun uba! Ni zata kawo rainin hankali to wlh bata isaba' ni da tuntuni ma ka sanar dani wlh har gida zanje naci ubanta' wai tsayama tukun waye ubanta a garin nan? Da zcy ya dibeta fisgo hannu Nurudee tai dake tsaye kusa da'ita h'ade da cewa kai zomuje har gidan naci ubansu marasa mutunci.
"Har sukai bakin kofar fita Abba yace ina zani?
" babu ko tsaoro bale shakka tace g'idan su Aisha.
"Abba yace in har kikabar nan ba gida kika jeba to bada izinina ba.
" Hjy laila macece me zafi sosae amma kuma me biyayya bata tsallake mgnr mijinta' h'akan yasa ta dawo tasamu gu ta zauna duk da h'aka inda take shiga ba nan take fita ba.
"Alhj yace kiyi hakuri h'aka nafiso naje da kaina' sbd idan har nabari kikaje nasan komai zaki iya aikata masu" kuma banaso ki aikata abinda zamu dawo muna danasani SBD bamusan abinda gaba zaiyi ba.
"Cikin goats one tace yayi dawa Allah ya saukake.
" zahradee dake manne jikin Abba cire drip d'in yai h'ade da cewa Abba muje gida ni na warke.
"Abba yace a'a son kabari kakara samu sauki.
" suna cikin h'aka doctor ya shiga koda yasake dubashi yace yasamu sauki dama damuwace tai masa yawa shiyasa amma Dan Allah arinka kulawa dashi da kuma gujewa abinda zaisa yasake shiga irin wani yanayi.
"Abba yace insha Allahu.
" daga nan aka rubuta masu magunguna h'ade da sallama' suka koma gida.
"Tunda suka dawo guidance Hjy mmnsa da yayyinsa kae har ma da Abba suke bawa zahradee kyakykyawar kulawa h'ade da kwatar masa da hankali dan gani yadawo normal kamar da' kusan kullum sae Abba yai masa addu'a a ruwa yabashi yasha sbd ko Allah zaisa a cire mgnr Aisha a ransa.
" d'an koda suka dawo g'ida kullum mgnr kenan Aisha'aisha ta tafi ta barni Abba da Hjy suyi fada har sugaji' amma zahradee bedaena ambaton su Aisha ba' idan ka gansa kamar mahaukaci sbd yadda ya koma' shiyasa har bada kudi Abba yai arinka yimasa addu'a ana bashi yana sha' shima kuma yana yimasa da kansa.
"Cikin hukucin Ubangiji komai yafara daedae ta har fita kasuwa yakeyi shida Abba' amma ko da wasa bayaso a kawo masa mgnr budurwa' h'aka yaci gaba da rike kansa' amma idan har ya dauki wayarsa yafara duba pict d'in sae kawai kaji yana nisawa' da Abba yaga h'aka canza masa wayar yai wanca k'uma ya goge komai dake cikinta snn ya kai d'akin sa ya boye.
" tunda daga lkcn zahradee ya dawo normal life kamar kowa' duk wanda yasan zahradee k'uma yasan bayason mgnr budurwa bayayi masa' shima yaci gaba da harkikin kasuwancinsa gani suna samun Improvement yasa Abba ya sakan masa komai Dan yanzu kusan duk dukiyar Abba a hannu zahradee yake sbd zahradee irin mutaninan ne wanda duk abinda zasu taba sae yayi albarka' shiyasa Abba yake matukar son zahradee akan sauran yaransa.
☘☘☘ ☘☘☘
CI GABAN LABARI
Abdul be'isa garin binni kebbi ba sae gam da magrib ana saukeshi a tasha yai amfani da address d'in da umma tabashi dashi ya'isa har g'idan su Fatima a bakin gate ya tsaya sae da yasake tambayan gateman snn yace dan Allah shi kani matar maigidan ne Aisha ko zai taimaka masa ya sanar da'ita?
"Gateman yace ba matsala ga gu ya zauna ya jirashi yaje ya sanar dasu snn yashiga daga ciki' wani d'an karami bechi dake gefe ya nuna masa ya zauna' snn shikuma ya shiga daga cikin g'idan lkcn Fatima na zaune a parlour ita da yara gateman yai sallama Fatima tai masa izini daya shigo.
"Yana shigowa bayan ya gaisheta snn yace dama wani bakon saurayine yazo yace wai shi kani madam ne daga garinsu yake sunasa Abdul shine nace ya tsaya na sanar maki snn.
" Fatima tace okay bari a kirata tuku' juyawa tai gun Khadijat dake zaune kusa da'ita tace jeki ki kira antynku.
"Khadijat tace to' mikewa tai taje da sallama tashiga d'akin lkcn Aisha na zaune bakin gado ta zabga uban tagumi' gani Khadijat ta shigone yasata dagowa da sauri tace Khadijat ya akai ne?
" Khadijat tace Anty momy ne tace kizo kinyi bako.
"Aisha tace bako k'uma? Daga ina?.
" mikewa tai suka fita tare' suna tafita parlour Aisha tace Anty gani' Fatima tace gateman yashigo yake sanar dani kinyi bako' Aisha tace bako k'uma Anty toni wama nasani a garin nan da zaizo guna.
"Murmushi kawai Fatima tai sbd yadda Aisha take mgn' snn tacewa Aisha jeki kiga ko waye.
" komawa tai ta dauko hijab tasa snn tafito h'ade da kiran Khadijat ta rakata' Aisha na fita gani bataga kowa kusa a gun ba tajuya zasu koma ciki da sauri gateman yace Hjy ga bakon nan snn Aisha ta tsaya fita yai yakira Abdul suka shigo tare' Aisha na ganisa a guje taje ta rungumesa h'ade da fasawa da kuka tana kiran Abdul dama Ashe zansake ganika?.
"Abdul yai matukar mmkin gani Aisha sbd gaba daya ta lalace ta fita a haiyacinta kamar ba Aisha daya sani ba' dan ma jinisane inda badan jini ba da ba lalla bane ya shedata.
"Shirun da Fatima taji yasata lekawa gani Aisha na rungume da Abdul yasata fita taje gunsa kallo daya taiwa Abdul taga kamanni Aisha a fuskansa' tace a'a Abdul yau bakone h'aka mukai to kukariso ciki mana.
" snn suka karisa ciki' tana gaba suna baya suka shiga a parlour suka zauna Fatima ta kira Khadija sukaje kitchen ruwa da juice tabawa Khadijat tace takaiwa su Abdul parlour' Khadijat na gaba Fatima na baya suka koma parlour a gaban Abdul ta'eje try d'in' bayan ya sha ruwan ne suka gaisa h'ade da tambayarsa su ummansu.
"Abdul yace duk suna lfy' sun cema a gaida ku.
" Fatima tace muna amsawa.
"Mikewa tai da Khadijat snn ta dauki Jabeer dake bcc suka basu gun' bayan tashiga dakine yasake aikan Khadijat ta kira Aisha' tare suka tafi da Aisha kitchen Fatima taje ta d'au abincnsu na dare wanda zasuci da yara ta raba biyu tace Aisha ta dauka h'ade da bata hakuri sbd abinci babu yawa k'uma abincin gida kadan yarage banle ace za'a sake dafa wani.
'" Aisha tace ba komai ngd sosae Anty.
"Itama Fatima tace babu damuwa.
" kai tsaye d'akinta takai masa abincin snn ta d'ibi nata da zataci na dare ta kara masa a nasa snn takoma parlour ta kirashi daki yazo yaci abinci.
"Zama yai dirshan akan carpet yanaci suna hira yana bata lbrin su Abba da umma' suna cikin hira ta dauko nata zataci gani abincn kadin ne yasa Abdul cewa Anty kije ki kara mana amma wann abinci kamar zakibawa yaro.
"Yage Aisha tai h'ade da cewa a'a h'aka ma ya'isheni.
" ragowar abincin da Fatima da eje tabawa yara sukaci ita k'uma tasha ruwan Lipton' lkcn kwanciya da yayi extra d'akin da babu kowa Fatima tace Aisha ta bude wa Abdul ya meant a a ciki.
📖🖊
☘☘
☘
AURE IBADA NE
FASAHA ONLINE WRITERS F.O.W.☘.
MMN USWAN
2⃣0⃣
"Da safe cikin abinda Fatima ta h'ada wa yara na breakfast ta d'ibawa Abdul tea ne da arish ko madaran kirki babu a ciki' da Aisha tashigo gaidata ne tace taje kitchen ta dauki abin breakfast takaiwa Abdul, Aisha tace to ngd Anty.
" har tajuya sai Fatima tace amma ke hkr zakiyi sbd bekai damu ba' koni bansamu wanda wajan nawa ne nabawa Abdul tunda shi bakone be kamata a barsa da yunwa ba.
"Aisha tace hakane Anty babu damuwa nagode.
" kai tsaye d'akin ta takai abincin ta'ije duk da yau ta tashi da yunwa sbd ragowar abincin tane wanda zataci da dare ta karawa Abdul yaci ita k'uma ta hkr, shiyasa ta tashi da yunwa amma yaya zatayi dole yanzu d'inma ta hakura tunda bashida inda zaije yaci inba nan ba.
"table d'in dake gefen gadonta tadora akai ta eje masa' Abdul be tashi ba sai around nine snn ya tashi bcc yana fitowa daga daki parlour yazo ya zauna snn ya kira Aisha ta waya' Aisha na fitowa tace yazo suje d'akin ta.
" mikewa yai suka shige bayan su gaisa ne Aisha ta d'au abin breakfast ta mika masa' Abdul yaci suna hira' duk hiran da sukeyi ba shigar Aisha yake yiba kawai amsashi takeyi amma bekai ciki ba' idonta su cika da kwallo k'adan yarage su xubo da sauri tasa hannu ta goge.
"Da Abdul ya lura da h'aka yace Aisha lfy? murmushin yake tai masa wanda bekai zuci ba' h'ade da cewa babu komai tun dare ne wani abu ya f'ada min a ido shiyasa kaga duk idanu suyi ja.
" Abdul yace sorry' idan kinga zai dameki ki sanarwa maigidanki ya kaiki hospital sbd ba'a wasa da ido fa.
"To kawai tace.
" Snn Abdul wayya ni tunda nazo banga maigidan nakuba kodai baya gari ne? Aisha tace yana nan wasu aiyukane sukasha kansa shiyasa baya samu isaishen lokcin da har zaka gansa.
"okay kina nufin baya kwanan g'ida kenan?.
"shiru Aisha tai bata sake tankasa ba.
"Abdul yace yauwa Aisha.
"na'am.
"nidae tun jiya da nazo wani iri na ganki kamar mara lfy kodae tun cuwon da umma tace kinji shine har yanzu baki dawoba.
" Eh"kawai tace.
"Amma ai kinkai wata uku da rashin lfy ko?.
" Eh"
"To kina amfani da magugunar da aka baki kuwa?.
'" ina amfani dasu mana.
"amma gaskiya yakamata ace kin canza' dubi yadda kika koma kashi kashi fa' kamar wanda batacin abinda' Aisha kodae kina zama da yunwane? ko k'uma bakijin dadin zaman g'idan ne?.
" shiru Aisha tai kanta na kasa.
"Abdul yace Aisha kiyi mgn mana.
" hawayene kawai suka zubo mata.
"lalla Aisha Akwai matsala dama shine dalilin zuwana kenan sbd su umma koda su kira number baya shiga h'aka ma na maigidanki k'uma ga munanar mafarkai da umma keyi a kanki.
" Aisha naji h'aka fashewa da kuka tai.
"gani kukan da takeyi yasashi kasa cin abincin dake gaban sa' jikinsa yai sanyi sosae.
" mikewa yai ya fita waje can gefe ya samu ya kira umma bayan sun gaisa h'ade da tambayar ya yasami aishan' Abdul yace gskya umma akwai matsala sbd ni kaina banji dadin ganita da nai ba.
"nan yazare komai ya sanarwa umma'umma harda kukanta take cewa idan mijin aishan yadawo yace tanaso mgn dashi.
" Abdul yace to umma.
"bayan fitar Abdul ne Aisha ta d'au abincin daya barshi yafita taci' dama kukanta da biyu sbd yunwar daya addabeta.
" itako Fatima ruwan Lipton tasha' gani eleven yayi yasata shiga kitchen taduba taga abinda yarage masu' shinkafa ya kare h'aka semovitar sae kuskus da taliya wanda basufi three three bag ba' tsayawa tai tai shiru tana tunanin ta'ina zata fara? ita k'uma a yadda takeji a yanzu a zcyrta bazata iya siyo kayan abinc ta ciyar da wata ba' sbd ma inda zata duba irin abinda Nasir keyi mata wlh koda ruwan g'idan bazata bari wata tasha ba.
"amma abu daya take dubawa sbd itama ta haihu k'uma bazataso yau ace yar'ta tai aure ta f'ada irin wnn yanayin ba' shine kawai dalilin dayasa duk yaran da Nasir zai aure bayan ya gama ci moriyarsu snn k'uma ya koresu suke bata tausayi.
" Amma suna Allah ya kara masu da kwadayinsu daga gani mutum bakasan daga inda yakeba kabashi aure' Ai ga irinta nan.
"wani d'an karamin tsaki tai h'ade da kuna gas tasa sanwar taliya jallop gaba daya dafa harda na dare tana gamawa tasawa Aisha da Abdul a kula daya sauran k'uma tazuba a kula ita da yara.
" koda ta kira Aisha tazo ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 38